< Luuka 5 >

1 Ühel päeval, kui Jeesus seisis Galilea mere ääres, tunglesid inimesed tema ümber, et Jumala sõna kuulda.
Wata rana, Yesu yana tsaye a bakin Tafkin Gennesaret, mutane kuma suna ta matsawa kewaye da shi, domin su ji maganar Allah,
2 Jeesus märkas kaldal kaht paati, mille olid jätnud sinna kalurid, kes oma võrke pesid.
sai ya hangi jiragen ruwa biyu a bakin tafkin, waɗanda masu kamun kifi suka bari suna wankin abin kamun kifinsu.
3 Jeesus astus paati, sellesse, mis kuulus Siimonale, ja palus tal paadi vette tõugata, kaldast veidi eemale. Siis Jeesus istus paadis maha ja õpetas sealt rahvast.
Sai ya shiga ɗaya jirgin ruwan da yake na Siman, ya kuma roƙe shi yă tura shi kaɗan daga gaci. Sai ya zauna a jirgin ruwan, ya koyar da mutane daga ciki.
4 Pärast seda kui ta kõnelemise oli lõpetanud, ütles ta Siimonale: „Mine välja sügavamasse vette ja lase oma võrgud püüdmiseks sisse.“
Da ya gama magana, sai ya ce wa Siman, “Ka tuƙa jirgin zuwa inda akwai zurfi, ka saukar da abin kamun kifinka ka kama kifi.”
5 „Õpetaja, nägime kogu öö tõsist vaeva, kuid ei püüdnud midagi. Aga kui sa nii ütled, siis lasen võrgud sisse, “vastas Siimon.
Siman ya amsa ya ce, “Ranka yă daɗe, duk dare mun yi ta fama ba mu kama kome ba, amma tun da ka ce haka, zan saki abin kamun kifin.”
6 Kui võrgud olid vees, täitis suur kalaparv võrgud nii, et need olid rebenemas.
Da suka yi haka, sai suka kama kifi da yawa, har abin kamun kifinsu suka fara tsintsinkewa.
7 Nad andsid märku kaaslastele teises paadis ja palusid neil appi tulla. Teised tulid ja mõlemad paadid said kalu täis. Paadid olid nii täis, et hakkasid vajuma.
Sai suka kira abokansu a ɗaya jirgin, su zo su taimake su, suka kuwa zo. Suka cika jiragen biyu da kifi cif, har jiragen suka fara nutsewa.
8 Kui Siimon Peetrus nägi, mis oli juhtunud, langes ta Jeesuse ette põlvili. „Issand, hoia palun minust eemale, sest ma olen patune inimene!“hüüatas ta.
Da Siman Bitrus ya ga wannan, sai ya fāɗi a gaban Yesu ya ce, “Rabu da ni, Ubangiji. Ni mai zunubi ne!”
9 Sest tema ja kõik, kes olid temaga koos, olid maale tõmmatud kalasaagist hämmastuses.
Gama mamaki ya kama shi da abokansa duka, saboda yawan kifin da suka kama.
10 Jaakobus ja Johannes, Sebedeuse pojad, Siimona kaaskalurid, tundsid sama. „Ära karda, “ütles Jeesus Siimonale. „Sest nüüdsest peale püüad sa inimesi!“
Yaƙub da Yohanna,’ya’yan Zebedi, abokan aikin Siman su ma suka yi mamaki. Sai Yesu ya ce wa Siman, “Kada ka ji tsoro, daga yanzu za ka riƙa kama mutane ne.”
11 Nõnda siis vedasid nad paadid kaldale, jätsid kõik maha ja järgnesid Jeesusele.
Sai suka jawo jiragen ruwansu zuwa gaci, suka bar kome da kome, suka bi shi.
12 Kord kui Jeesus külastas üht linna, kohtus ta mehega, kel oli väga raske pidalitõbi. Mees heitis näoli maha ja anus Jeesust: „Palun, Issand, kui sa tahad, võid sa mind puhtaks teha.“
Yayinda Yesu yake ɗaya daga cikin garuruwan nan, sai ga wani mutum wanda kuturta ta ci ƙarfinsa. Da ganin Yesu, sai ya fāɗi da fuskarsa a ƙasa, ya roƙe shi ya ce, “Ubangiji, in ka yarda, kana iya ka tsabtacce ni.”
13 Jeesus sirutas käe ja puudutas meest. „Ma tahan, “ütles ta. „Saa puhtaks!“Pidalitõbi kadus otsekohe.
Yesu ya miƙa hannunsa ya taɓa mutumin ya ce, “Na yarda, ka zama da tsabta!” Nan da nan, sai kuturtar ta rabu da shi.
14 „Ära kellelgi midagi ütle, “õpetas Jeesus teda. „Mine ja näita end preestrile ja too oma tervenemise tõestuseks Moosese seaduses nõutud tseremoniaalohvrid.“
Sai Yesu ya umarce shi ya ce, “Kada ka gaya wa kowa, amma ka tafi ka nuna kanka ga firist, ka kuma miƙa hadayu da Musa ya umarta, saboda tsarkakewarka ta zama shaida a gare su.”
15 Ikkagi levisid kuuldused Jeesusest üha enam ja enam. Suured rahvahulgad tulid Jeesust kuulama ja oma haigustest terveks saama.
Duk da haka, labarinsa ya ƙara bazuwa sosai, har taron mutane suka dinga zuwa don jinsa, da kuma neman warkarwa daga cututtukansu.
16 Aga sageli tõmbus Jeesus vaiksesse paika ja palvetas.
Amma Yesu sau da yawa, yakan keɓe kansa zuwa wuraren da ba kowa, yă yi addu’a.
17 Ühel päeval, kui Jeesus õpetas, istusid seal ka variserid ja vaimulikud õpetajad, kes olid tulnud kogu Galileast, Juudamaalt ja Jeruusalemmast. Issanda vägi tervendada oli temaga, nii et ta suutis inimesi terveks teha.
Wata rana, da yake cikin koyarwa, waɗansu Farisiyawa da malaman dokoki waɗanda suka zo daga kowane ƙauye a Galili, Yahudiya da Urushalima kuwa suna zaune. Ikon Ubangiji yana nan don yă warkar da masu ciwo.
18 Mõned mehed tulid ja kandsid mati peal halvatud meest. Nad üritasid teda sisse viia, et teda Jeesuse ette asetada.
Sai ga waɗansu mutane suka kawo wani shanyayye a kan tabarma. Suka yi ƙoƙari su shigar da shi cikin gidan, domin su kwantar da shi a gaban Yesu.
19 Kuid nad ei suutnud läbi rahva teed leida, seega läksid nad üles katusele ja tegid katusekivide vahele augu. Seejärel lasksid nad mehe koos matiga alla, otse rahva sekka, Jeesuse ette.
Da suka ga babu hanyar da za su bi saboda taron, sai suka haura rufin, suka saukar da shi a kan tabarmarsa, ta bakin ramin da suka huda a rufin, suka ajiye shi a tsakiyar taron, a gaban Yesu.
20 Kui Jeesus nägi, missugune usk oli neil temasse, ütles ta mehele: „Sinu patud on andeks antud.“
Da Yesu ya ga bangaskiyarsu, sai ya ce, “Saurayi, an gafarta maka zunubanka.”
21 Vaimulikud õpetajad ja variserid hakkasid selle üle arutlema. „Kes ta on, et niimoodi Jumalat teotab?“küsisid nad. „Kes võib patte andeks anda? Ainult Jumal võib seda teha!“
Farisiyawa da malaman dokoki suka fara yin tunani a zukatansu, “Wane ne wannan mutum da yake saɓo haka? Wa zai iya gafarta zunubai, in ba Allah kaɗai ba?”
22 Jeesus teadis, mida nad arutlevad, seepärast küsis ta neilt: „Miks te seda kahtluse alla seate?
Yesu ya san abin da suke tunani, sai ya yi tambaya ya ce, “Don me kuke tunanin waɗannan abubuwa a zukatanku?
23 Mis on lihtsam? Kas öelda, et sinu patud on andeks antud või „Tõuse püsti ja kõnni!“?
Wanne ya fi sauƙi, a ce, ‘An gafarta maka zunubanka,’ ko kuma a ce, ‘Tashi, ka yi tafiya’?
24 Kuid ma tõestan teile, et inimese Pojal on õigus siin maa peal patte andeks anda.“Seejärel ütles ta halvatud mehele: „Ma ütlen sulle: tõuse üles, võta oma matt ja mine koju.“
Amma domin ku san cewa Ɗan Mutum yana da iko a duniya ya gafarta zunubai.” Sai ya ce wa shanyayyen, “Na ce maka, tashi, ɗauki tabarmarka ka tafi gida.”
25 Jalamaid tõusis mees nende ees püsti. Ta võttis mati, mille peal ta oli lamanud, ning läks Jumalat ülistades koju.
Nan da nan, ya tashi tsaye a gabansu, ya ɗauki tabarmar da yake kwance a kai, ya tafi gida, yana yabon Allah.
26 Kõik olid juhtunust täielikult jahmunud ning suures aukartuses ülistasid nad Jumalat, öeldes: „See, mida me täna nägime, oli hämmastav!“
Kowa ya yi mamaki, ya kuma yabi Allah. Suka cika da tsoro, suna cewa, “Mun ga abubuwan banmamaki yau.”
27 Hiljem, kui Jeesus oli linnast lahkumas, nägi ta maksukogujat nimega Leevi oma tolliputkas istumas. „Järgne mulle, “ütles Jeesus talle.
Bayan wannan, sai Yesu ya fita, ya ga wani mai karɓar haraji, mai suna Lawi, yana zaune a wurin da ake karɓar haraji. Yesu ya ce masa, “Bi ni.”
28 Leevi tõusis püsti, jättis kõik sinnapaika ja järgnes Jeesusele.
Sai Lawi ya tashi, ya bar kome da kome, ya bi shi.
29 Leevi korraldas oma kodus Jeesuse auks suure pidusöögi. Rahva hulgas, kes koos nendega sõi, oli palju maksukogujaid ja teisi. Kuid variserid ja vaimulikud õpetajad kurtis Jeesuse jüngritele, öeldes:
Sai Lawi ya shirya wa Yesu wani babban liyafa a gidansa. Wani babban taron na masu karɓar haraji, tare da waɗansu suna cin abinci tare da su.
30 „Miks te sööte ja joote koos maksukogujate ja patustega?“
Amma Farisiyawa da malaman dokokin da suke a ƙungiyarsu, suka yi wa almajiransa gunaguni, suna cewa, “Don me kuke ci, kuke sha tare da masu karɓar haraji da masu zunubi?”
31 „Arsti ei vaja terved, vaid haiged, “vastas Jeesus.
Yesu ya amsa musu ya ce, “Ai, masu lafiya ba sa bukatar likita, sai dai marasa lafiya.
32 „Ma ei tulnud kutsuma meeleparandusele neid, kes elavad õigesti. Ma tulin kutsuma patuseid.“
Ban zo don in kira masu adalci ba, sai dai masu zunubi zuwa ga tuba.”
33 „Aga Johannese jüngrid paastuvad sageli ja palvetavad ning variseride jüngrid samuti. Kuid sinu jüngrid seda ei tee, nad käivad söömas ja joomas, “ütlesid nad talle.
Suka ce masa, “Almajiran Yohanna sukan yi azumi da addu’a, haka ma almajiran Farisiyawa, amma naka sai ci da sha.”
34 „Kas peiupoisid peaksid paastuma sel ajal, kui peigmees on nende juures?“küsis Jeesus.
Yesu ya amsa ya ce, “Za ku iya sa abokan ango yin azumi yayinda yake tare da su?
35 „Ei, aga tuleb aeg, mil peigmees võetakse nende juurest ära. Küll nad siis paastuvad.“
Amma lokaci yana zuwa, da za a ɗauke ango daga gare su. A waɗancan kwanakin ne za su yi azumi.”
36 Siis esitas ta neile näitliku selgituse: „Uute rõivaste küljest ei rebita paika, et vanu rõivaid lappida. Muidu oleks uued rõivad rikutud ja uuelt pärit paik ei sobiks vanale.
Sai ya faɗa musu wannan misali ya ce, “Ba wanda yakan yage ƙyalle daga sabuwar riga ya yi wa tsohuwar riga faci. In ya yi haka, zai yage sabuwar rigar, kuma facin daga sabuwar ba zai dace da tsohuwar rigar ba.
37 Värsket veini ei panda vanadesse nahklähkritesse, sest kui seda teha, rebeneksid vanad lähkrid värske veini tõttu. Siis läheks raisku nii vein kui ka veinilähkrid.
Kuma ba wanda yakan zuba sabon ruwan inabi a cikin tsofaffin salkuna. In ya yi haka, sabon ruwan inabi zai farfashe salkunan, ruwan inabin yă zube, salkunan kuma su lalace.
38 Värske vein pannakse uutesse lähkritesse.
A’a, sai dai a zuba sabon ruwan inabi a sababbin salkuna.
39 Ja pärast vana veini joomist ei soovi keegi värsket veini, sest öeldakse, et „vana maitseb hästi“.“
Kuma ba wanda yakan so shan sabon ruwan inabi bayan ya sha tsohon, don yakan ce, ‘Ai, tsohon ya fi kyau.’”

< Luuka 5 >