< Luuka 1 >

1 Nagu sa tead, on paljud teised üritanud kirja panna seda, mis on täide läinud ja puudutab ka meid.
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 Nende jutustused põhinesid esimeste pealtnägijate ja Sõna kuulutajate tõenditel
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 ja ka mina otsustasin, et kuna olen kõike seda algusest peale väga hoolikalt jälginud, oleks hea mõte kõigest toimunust kirja panna täpne jutustus.
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 Tegin seda, kallis Teofilos, et sa võiksid olla kindel, et see, mida sulle õpetati, on täiesti usaldusväärne.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 Sel ajal kui Heroodes oli Juudamaa kuningas, oli üks preester nimega Sakarias, kes oli pärit Abija preesterlikust rühmast. Ta oli abielus Eliisabetiga, kes põlvnes samuti preester Aaronist.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 Nad mõlemad tegid, mis oli Jumala ees õige, ning järgisid hoolikalt kõiki Issanda käske ja määrusi.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 Neil ei olnud lapsi, sest Eliisabet ei olnud selleks suuteline, ja nad mõlemad olid juba vanad.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 Kui Sakarias teenis preestrina Jumala ees oma preesterlikus rühmas,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 valiti ta vastavalt preestrite tavale liisu heitmisega Issanda templisse sisenema ja suitsutusrohtu põletama.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 Suitsutusohvri toomise ajal palvetas väljas suur hulk rahvast.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 Issanda ingel ilmus Sakariasele ja seisis suitsutusohvrialtari kõrval paremal pool.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 Kui Sakarias nägi inglit, oli ta rabatud ja hakkas kartma.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 Aga ingel ütles talle: „Ära karda, Sakarias! Sinu palvet on kuuldud ja su naine Eliisabet sünnitab sulle poja ja sa pead talle nimeks panema Johannes.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 Ta toob sulle rõõmu ja heameelt ning tema sünd rõõmustab paljusid.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 Ta saab suureks Issanda silmis. Ta ei joo veini ega muid alkohoolseid jooke. Teda täidab Püha Vaim juba enne sündimist.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 Ta pöörab paljud iisraellased tagasi Issanda, nende Jumala juurde.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 Ta läheb Issanda eel Eelija vaimus ja väes, et panna isad taas oma laste peale mõtlema, ning tuua need, kes on mässumeelsed, tagasi õige arusaamise juurde, et valmistada rahvas ette Issanda jaoks.“
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 „Kuidas ma saan selles kindel olla?“küsis Sakarias inglilt. „Ma olen vana mees ja ka mu naine on eakas.“
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 „Mina olen Gabriel, “vastas ingel. „Ma seisan Jumala juures ning mind saadeti sinuga rääkima ja sulle seda head uudist tooma.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 Aga kuna sa ei uskunud seda, mida ma sulle rääkisin, jääd sa tummaks ega saa kõneleda kuni määratud hetkeni, mil mu sõnad täide lähevad.“
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 Väljas ootas rahvas Sakariast ja imestas, miks tal templis nii kaua aega läheb.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 Kui ta lõpuks välja tuli, ei saanud ta nendega rääkida. Nad mõistsid, et ta oli templis näinud nägemust, sest kuigi ta suutis teha žeste, ei suutnud ta üldse rääkida.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 Pärast seda, kui ta oma teenistusaja oli lõpetanud, läks ta koju tagasi.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 Mõne aja pärast jäi tema naine Eliisabet lapseootele. Ta jäi koju viieks kuuks.
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 „Issand on seda mulle teinud, “ütles ta. „Nüüd on ta võtnud ära mu häbi teiste silmis.“
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 Eliisabeti lapseootuse kuuendal kuul saatis Jumal ingel Gabrieli noore neiu juurde, kelle nimi oli Maarja ja kes elas Galileas Naatsareti linnas.
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 Ta oli kihlatud Joosepi-nimelise mehega.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 Ingel tervitas teda. „Sul on eriline eesõigus, “ütles ta neiule. „Issand on sinuga.“
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 Maarja oli neist sõnadest hämmelduses ja juurdles, mida selline tervitus tähendab.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 „Ära karda, Maarja, “jätkas ingel, „sest Jumal on osutanud sinu suhtes armulikkust.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Sa jääd lapseootele ja tood ilmale poja. Sa pead talle nimeks panema Jeesus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 Ta saab väga tähtsaks ja teda nimetatakse Kõigekõrgema Pojaks. Issand Jumal annab talle tema isa Taaveti trooni
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 ja ta valitseb igavesti Jaakobi järeltulijate üle. Tema kuningriik ei lõpe iial.“ (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 „Kuidas see võimalik on?“küsis Maarja. „Ma olen alles neitsi.“
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 Ingel vastas: „Püha Vaim tuleb sinu peale ja Kõigekõrgema vägi varjab sind. Laps, kes sünnib, on püha, ja teda hüütakse Jumala pojaks.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 Ja su sugulane Eliisabet on oma vanas eas samuti lapseootel. Naine, kelle kohta öeldi, et ta ei ole võimeline lapsi saama, on kuuendat kuud lapseootel.
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 Jumala jaoks ei ole miski võimatu.“
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 „Siin ma olen, valmis olema Issanda teenija, “ütles Maarja. „Sündigu minuga just nii, nagu sa ütlesid.“Seejärel ingel lahkus tema juurest.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Veidi aja pärast pani Maarja end valmis ja kiirustas Juudamaa mägedesse, linna, kus oli
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 Sakariase maja. Sisse astudes hõikas ta Eliisabetti.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 Kohe kui Eliisabet kuulis Maarja häält, hüppas laps tema ihus rõõmu pärast. Püha Vaim täitis Eliisabeti
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 ja ta hüüdis valju häälega: „Kui õnnistatud oled sina naiste hulgas ja kui õnnistatud on laps, kes sinust sünnib!
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 Miks mind nõnda austatakse, et mu Issanda ema mind külastab?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 Kui ma kuulsin sind tervitust hüüdmas, hüppas laps mu ihus rõõmu pärast.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 Kui õnnelik sa oled, sest sa oled veendunud, et Issand teeb seda, mida ta sulle tõotas!“
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 Maarja vastas: „Kuidas ma ülistan Issandat!
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 Olen väga õnnelik Jumalas, mu Päästjas,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 sest ta otsustas, et mina, tema teenija, olen oma tagasihoidlikust taustast hoolimata tema silmis väärtuslik. Nüüdsest peale ütlevad kõik põlvkonnad, et ma olen õnnistatud.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 Kõigeväeline Jumal on teinud mulle suuri asju, tema nimi on püha.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 Tema halastus kestab põlvest põlve nendele, kes teda austavad.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 Oma suure jõuga on ta lõhkunud tükkideks need, kes ülbelt ennast targaks peavad.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 Ta kisub mõjukad nende troonidelt maha ja ülendab need, kes on alandlikud.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 Ta annab näljastele häid asju süüa ja saadab rikkad tühje käsi minema.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 Ta on aidanud oma sulast Iisraeli ja pidanud teda halastuses meeles,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 just nagu ta meie isadele, Aabrahamile ja tema järeltulijatele, igaveseks ajaks tõotas.“ (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 Maarja jäi Eliisabeti juurde kolmeks kuus ja naasis siis koju.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Eliisabetil jõudis sünnitamise aeg kätte ja ta tõi ilmale poja.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 Naabrid ja sugulased kuulsid, kuidas Issand oli talle oma suurt headust osutanud, ning nad tähistasid seda koos temaga.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 Kaheksa päeva pärast tulid nad poissi ümber lõikama. Nad kavatsesid talle isa järgi nimeks panna Sakarias.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 „Ei, “ütles Eliisabet. „Tema nimeks peab saama Johannes.“
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 „Aga teie sugulaste hulgas pole kedagi, kellel see nimi oleks, “ütlesid nad talle.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 Žestide abil küsisid nad Sakariaselt, poisi isalt, mis nime tahaks ta oma pojale panna.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 Sakarias andis märku, et talle antaks midagi, mille peale kirjutada. Kõigi üllatuseks kirjutas ta: „Tema nimi on Johannes.“
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 Kohe suutis ta jälle rääkida ja hakkas Jumalat ülistama.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 Kõiki läheduses elavaid inimesi täitis juhtunu tõttu aukartus ning kuuldus sellest levis kogu Juuda mägismaal.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 Igaüks, kes seda kuulis, mõtles, mida see peaks tähendama. „Kes sellest poisist saab?“küsisid nad, sest oli selge, et ta oli Jumala jaoks väga eriline.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 Tema isa Sakarias täitus Püha Vaimuga ja kuulutas prohvetlikult:
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 „Issand, Iisraeli Jumal, on imeline, sest ta on tulnud oma rahva juurde ja nad vabastanud.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 Ta on andnud meile suure Päästja oma sulase Taaveti järglaste hulgast,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 nagu ta tõotas ammu aega tagasi oma pühade prohvetite kaudu. (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 Ta tõotas päästa meid meie vaenlaste käest, nende käest, kes meid vihkavad.
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 Ta halastas meie isade peale ja pidas meeles oma püha lepingut −
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 tõotust, mille ta oli andnud meie isale Aabrahamile.
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 Ta vabastab meid hirmust ja päästab meid meie vaenlaste käest,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 et saaksime teda teenida ning teha kogu oma elu seda, mis on hea ja õige.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 Kuigi sa oled alles väike laps, hüütakse sind Kõigekõrgema prohvetiks, sest sa lähed Issanda eel valmistama talle teed ja
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 kuulutama tema rahvale teadmisi päästest pattude andestuse kaudu.
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Tänu Jumala hoolitsevale headusele laseb taevas meile koiduvalgust paista,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 et see säraks neile, kes elavad pimeduses ja surma varjus, ning juhiks meid rahu teel.“
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 Poiss Johannes kasvas ja sai vaimulikult tugevaks. Ta elas kõrbes, kuni jõudis kätte aeg avalikult Iisraeli teenida.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luuka 1 >