< Luke 1 >

1 Seeing that many did take in hand to set in order a narration of the matters that have been fully assured among us,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 as they did deliver to us, who from the beginning became eye-witnesses, and officers of the Word, —
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 it seemed good also to me, having followed from the first after all things exactly, to write to thee in order, most noble Theophilus,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 that thou mayest know the certainty of the things wherein thou wast instructed.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 There was in the days of Herod, the king of Judea, a certain priest, by name Zacharias, of the course of Abijah, and his wife of the daughters of Aaron, and her name Elisabeth;
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 and they were both righteous before God, going on in all the commands and righteousnesses of the Lord blameless,
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 and they had no child, because that Elisabeth was barren, and both were advanced in their days.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 And it came to pass, in his acting as priest, in the order of his course before God,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 according to the custom of the priesthood, his lot was to make perfume, having gone into the sanctuary of the Lord,
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 and all the multitude of the people were praying without, at the hour of the perfume.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 And there appeared to him a messenger of the Lord standing on the right side of the altar of the perfume,
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 and Zacharias, having seen, was troubled, and fear fell on him;
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 and the messenger said unto him, 'Fear not, Zacharias, for thy supplication was heard, and thy wife Elisabeth shall bear a son to thee, and thou shalt call his name John,
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 and there shall be joy to thee, and gladness, and many at his birth shall joy,
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 for he shall be great before the Lord, and wine and strong drink he may not drink, and of the Holy Spirit he shall be full, even from his mother's womb;
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 and many of the sons of Israel he shall turn to the Lord their God,
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 and he shall go before Him, in the spirit and power of Elijah, to turn hearts of fathers unto children, and disobedient ones to the wisdom of righteous ones, to make ready for the Lord, a people prepared.'
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 And Zacharias said unto the messenger, 'Whereby shall I know this? for I am aged, and my wife is advanced in her days?'
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 And the messenger answering said to him, 'I am Gabriel, who have been standing near before God, and I was sent to speak unto thee, and to proclaim these good news to thee,
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 and lo, thou shalt be silent, and not able to speak, till the day that these things shall come to pass, because thou didst not believe my words, that shall be fulfilled in their season.'
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 And the people were waiting for Zacharias, and wondering at his tarrying in the sanctuary,
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 and having come out, he was not able to speak to them, and they perceived that a vision he had seen in the sanctuary, and he was beckoning to them, and did remain dumb.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 And it came to pass, when the days of his service were fulfilled, he went away to his house,
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 and after those days, his wife Elisabeth conceived, and hid herself five months, saying —
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 'Thus hath the Lord done to me, in days in which He looked upon [me], to take away my reproach among men.'
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 And in the sixth month was the messenger Gabriel sent by God, to a city of Galilee, the name of which [is] Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 to a virgin, betrothed to a man, whose name [is] Joseph, of the house of David, and the name of the virgin [is] Mary.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 And the messenger having come in unto her, said, 'Hail, favoured one, the Lord [is] with thee; blessed [art] thou among women;'
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 and she, having seen, was troubled at his word, and was reasoning of what kind this salutation may be.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 And the messenger said to her, 'Fear not, Mary, for thou hast found favour with God;
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 and lo, thou shalt conceive in the womb, and shalt bring forth a son, and call his name Jesus;
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 he shall be great, and Son of the Highest he shall be called, and the Lord God shall give him the throne of David his father,
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 and he shall reign over the house of Jacob to the ages; and of his reign there shall be no end.' (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 And Mary said unto the messenger, 'How shall this be, seeing a husband I do not know?'
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 And the messenger answering said to her, 'The Holy Spirit shall come upon thee, and the power of the Highest shall overshadow thee, therefore also the holy-begotten thing shall be called Son of God;
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 and lo, Elisabeth, thy kinswoman, she also hath conceived a son in her old age, and this is the sixth month to her who was called barren;
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 because nothing shall be impossible with God.'
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 And Mary said, 'Lo, the maid-servant of the Lord; let it be to me according to thy saying,' and the messenger went away from her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 And Mary having arisen in those days, went to the hill-country, with haste, to a city of Judea,
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 and entered into the house of Zacharias, and saluted Elisabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 And it came to pass, when Elisabeth heard the salutation of Mary, the babe did leap in her womb; and Elisabeth was filled with the Holy Spirit,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 and spake out with a loud voice, and said, 'Blessed [art] thou among women, and blessed [is] the fruit of thy womb;
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 and whence [is] this to me, that the mother of my Lord might come unto me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 for, lo, when the voice of thy salutation came to my ears, leap in gladness did the babe in my womb;
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 and happy [is] she who did believe, for there shall be a completion to the things spoken to her from the Lord.'
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 And Mary said, 'My soul doth magnify the Lord,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 And my spirit was glad on God my Saviour,
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 Because He looked on the lowliness of His maid-servant, For, lo, henceforth call me happy shall all the generations,
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 For He who is mighty did to me great things, And holy [is] His name,
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 And His kindness [is] to generations of generations, To those fearing Him,
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 He did powerfully with His arm, He scattered abroad the proud in the thought of their heart,
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He brought down the mighty from thrones, And He exalted the lowly,
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 The hungry He did fill with good, And the rich He sent away empty,
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 He received again Israel His servant, To remember kindness,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 As He spake unto our fathers, To Abraham and to his seed — to the age.' (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 And Mary remained with her about three months, and turned back to her house.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 And to Elisabeth was the time fulfilled for her bringing forth, and she bare a son,
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 and the neighbours and her kindred heard that the Lord was making His kindness great with her, and they were rejoicing with her.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 And it came to pass, on the eighth day, they came to circumcise the child, and they were calling him by the name of his father, Zacharias,
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 and his mother answering said, 'No, but he shall be called John.'
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 And they said unto her — 'There is none among thy kindred who is called by this name,'
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 and they were making signs to his father, what he would wish him to be called,
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 and having asked for a tablet, he wrote, saying, 'John is his name;' and they did all wonder;
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 and his mouth was opened presently, and his tongue, and he was speaking, praising God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 And fear came upon all those dwelling around them, and in all the hill-country of Judea were all these sayings spoken of,
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 and all who heard did lay them up in their hearts, saying, 'What then shall this child be?' and the hand of the Lord was with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 And Zacharias his father was filled with the Holy Spirit, and did prophesy, saying,
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 'Blessed [is] the Lord, the God of Israel, Because He did look upon, And wrought redemption for His people,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 And did raise an horn of salvation to us, In the house of David His servant,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 As He spake by the mouth of His holy prophets, Which have been from the age; (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 Salvation from our enemies, And out of the hand of all hating us,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 To do kindness with our fathers, And to be mindful of His holy covenant,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 An oath that He sware to Abraham our father,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 To give to us, without fear, Out of the hand of our enemies having been delivered,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 To serve Him, in holiness and righteousness Before Him, all the days of our life.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And thou, child, Prophet of the Highest Shalt thou be called; For thou shalt go before the face of the Lord, To prepare His ways.
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 To give knowledge of salvation to His people In remission of their sins,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 Through the tender mercies of our God, In which the rising from on high did look upon us,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 To give light to those sitting in darkness and death-shade, To guide our feet to a way of peace.'
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 And the child grew, and was strengthened in spirit, and he was in the deserts till the day of his shewing unto Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >