< Luke 1 >

1 Forsothe for manye men enforceden to ordeyne the tellyng of thingis, whiche ben fillid in vs,
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 as thei that seyn atte the bigynnyng, and weren ministris of the word,
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 bitaken, it is seen also to me, hauynge alle thingis diligentli bi ordre, to write to thee,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 thou best Theofile, that thou knowe the treuthe of tho wordis, of whiche thou art lerned.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 In the daies of Eroude, kyng of Judee, ther was a prest, Sakarie bi name, of the sorte of Abia, and his wijf was of the douytris of Aaron, and hir name was Elizabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 And bothe weren iust bifor God, goynge in alle the maundementis and iustifiyngis of the Lord, withouten pleynt.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 And thei hadden no child, for Elizabeth was bareyn, and bothe weren of grete age in her daies.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 And it bifel, that whanne Zacarie schulde do the office of preesthod, in the ordre of his cours tofor God,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 aftir the custome of the preesthod, he wente forth bi lot, and entride in to the temple, to encense.
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 And al the multitude of the puple was with outforth, and preiede in the our of encensyng.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 And an aungel of the Lord apperide to hym, and stood on the riythalf of the auter of encense.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 And Zacarie seynge was afraied, and drede fel vpon hym.
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 And the aungel seide to hym, Zacarie, drede thou not; for thi preyer is herd, and Elizabeth, thi wijf, schal bere to thee a sone, and his name schal be clepid Joon.
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 And ioye and gladyng schal be to thee; and many schulen `haue ioye in his natyuyte.
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 For he schal be greet bifor the Lord, and he schal not drynke wyn and sidir, and he schal be fulfillid with the Hooli Goost yit of his modir wombe.
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 And he schal conuerte many of the children of Israel to her Lord God;
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 and he schal go bifor hym in the spirit and the vertu of Helie; and he schal turne the hertis of the fadris in to the sones, and men out of bileue to the prudence of iust men, to make redi a perfit puple to the Lord.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 And Zacarie seide to the aungel, Wherof schal Y wite this? for Y am eld, and my wijf hath gon fer in to hir daies.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 And the aungel answeride, and seide to hym, For Y am Gabriel, that stonde niy bifor God; and Y am sent to thee to speke, and to euangelize to thee these thingis.
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 And lo! thou schalt be doumbe, and thou schalt not mow speke til in to the dai, in which these thingis schulen be don; for thou hast not bileued to my wordis, whiche schulen be fulfillid in her tyme.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 And the puple was abidynge Zacarie, and thei wondriden, that he tariede in the temple.
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 And he yede out, and myyte not speke to hem, and thei knewen that he hadde seyn a visioun in the temple. And he bikenyde to hem, and he dwellide stille doumbe.
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 And it was don, whanne the daies of his office weren fulfillid, he wente in to his hous.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 And aftir these daies Elizabeth, his wijf, conseyuede, and hidde hir fyue monethis, and seide,
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 For so the Lord dide to me in the daies, in whiche he bihelde, to take awei my repreef among men.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 But in the sixte moneth the aungel Gabriel was sent fro God in to a citee of Galilee, whos name was Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 to a maidyn, weddid to a man, whos name was Joseph, of the hous of Dauid; and the name of the maidun was Marie.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 And the aungel entride to hir, and seide, Heil, ful of grace; the Lord be with thee; blessid be thou among wymmen.
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 And whanne sche hadde herd, sche was troublid in his word, and thouyte what maner salutacioun this was.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 And the aungel seide to hir, Ne drede thou not, Marie, for thou hast foundun grace anentis God.
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 Lo! thou schalt conceyue in wombe, and schalt bere a sone, and thou schalt clepe his name Jhesus.
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 This schal be greet, and he schal be clepid the sone of the Hiyeste; and the Lord God schal yeue to hym the seete of Dauid, his fadir,
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 and he schal regne in the hous of Jacob with outen ende, and of his rewme schal be noon ende. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 And Marie seide to the aungel, On what maner schal this thing be doon, for Y knowe not man?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 And the aungel answeride, and seide to hir, The Hooly Goost schal come fro aboue in to thee, and the vertu of the Hiyeste schal ouerschadewe thee; and therfor that hooli thing that schal be borun of thee, schal be clepid the sone of God.
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 And lo! Elizabeth, thi cosyn, and sche also hath conceyued a sone in hir eelde, and this moneth is the sixte to hir that is clepid bareyn;
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 for euery word schal not be inpossible anentis God.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 And Marie seide, Lo! the handmaydyn of the Lord; be it don to me aftir thi word. And the aungel departide fro hir.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 And Marie roos vp in tho daies, and wente with haaste in to the mounteyns, in to a citee of Judee.
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 And sche entride in to the hous of Zacarie, and grette Elizabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 And it was don, as Elizabeth herde the salutacioun of Marie, the yong child in hir wombe gladide. And Elizabeth was fulfillid with the Hooli Goost,
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 and criede with a greet vois, and seide, Blessid be thou among wymmen, and blessid be the fruyt of thi wombe.
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 And whereof is this thing to me, that the modir of my Lord come to me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 For lo! as the voice of thi salutacioun was maad in myn eeris, the yong child gladide in ioye in my wombe.
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 And blessid be thou, that hast bileued, for thilke thingis that ben seid of the Lord to thee, schulen be parfitli don.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 And Marie seide, Mi soule magnyfieth the Lord,
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 and my spirit hath gladid in God, myn helthe.
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 For he hath biholdun the mekenesse of his handmaidun.
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 For lo! of this alle generaciouns schulen seie that Y am blessid. For he that is myyti hath don to me grete thingis, and his name is hooli.
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 And his mercy is fro kynrede in to kynredes, to men that dreden hym.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 He made myyt in his arme, he scaterede proude men with the thouyte of his herte.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He sette doun myyti men fro sete, and enhaunside meke men.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 He hath fulfillid hungri men with goodis, and he hath left riche men voide.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 He, hauynge mynde of his mercy, took Israel, his child;
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 as he hath spokun to oure fadris, to Abraham and to his seed, in to worldis. (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 And Marie dwellide with hir, as it were thre monethis, and turnede ayen in to hir hous.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 But the tyme of beryng child was fulfillid to Elizabeth, and sche bare a sone.
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 And the neiyboris and cosyns of hir herden, that the Lord hadde magnyfied his mercy with hir; and thei thankiden hym.
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 And it was don in the eiyte dai, thei camen to circumcide the child; and thei clepiden hym Zacarie, bi the name of his fadir.
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 And his moder answeride, and seide, Nay, but he schal be clepid Joon.
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 And thei seiden to hir, For no man is in thi kynrede, that is clepid this name.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 And thei bikeneden to his fadir, what he wolde that he were clepid.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 And he axynge a poyntil, wroot, seiynge, Joon is his name.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 And alle men wondriden. And anoon his mouth was openyd, and his tunge, and he spak, and blesside God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 And drede was maad on alle her neiyboris, and alle these wordis weren pupplischid on alle the mounteyns of Judee.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 And alle men that herden puttiden in her herte, and seiden, What maner child schal this be? For the hoond of the Lord was with hym.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 And Zacarie, his fadir, was fulfillid with the Hooli Goost, and prophesiede,
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 and seide, Blessid be the Lord God of Israel, for he hath visitid, and maad redempcioun of his puple.
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 And he hath rerid to vs an horn of heelthe in the hous of Dauid, his child.
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 As he spak bi the mouth of hise hooli prophetis, that weren fro the world. (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 Helthe fro oure enemyes, and fro the hoond of alle men that hatiden vs.
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 To do merci with oure fadris, and to haue mynde of his hooli testament.
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 The greet ooth that he swoor to Abraham, oure fadir, to yyue hym silf to vs.
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 That we with out drede delyuered fro the hoond of oure enemyes,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 serue to hym, in hoolynesse and riytwisnesse bifor hym in alle oure daies.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And thou, child, schalt be clepid the prophete of the Hiyest; for thou schalt go bifor the face of the Lord, to make redi hise weies.
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 To yyue scyence of helthe to his puple, in to remyssioun of her synnes;
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 bi the inwardnesse of the merci of oure God, in the whiche he spryngynge vp fro an hiy hath visitid vs.
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 To yyue liyt to hem that sitten in derknessis and in schadewe of deeth; to dresse oure feet in to the weie of pees.
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 And the child wexide, and was coumfortid in spirit, and was in desert placis `til to the dai of his schewing to Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >