< Jeremiah 49 >

1 `Go ye to the sones of Amon. The Lord seith these thingis. Whether no sones ben of Israel, ether an eir is not to it? whi therfor weldide Melchon the eritage of Gad, and the puple therof dwellide in the citees of Gad?
Game da Ammonawa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Isra’ila ba shi da’ya’ya maza ne? Ba shi da magāda ne? To, me ya sa Molek ya mallaki Gad? Me ya sa mutanensa suka zama a garuruwansa?
2 Lo! daies comen, seith the Lord, and Y schal make the gnaisting of batel herd on Rabath of the sones of Amon; and it schal be distried in to noise, and the vilagis therof schulen be brent with fier, and Israel schal welde hise welderis, seith the Lord.
Amma kwanaki suna zuwa,” in ji Ubangiji, “sa’ad da zan yi kirarin yaƙi a kan Rabba ta Ammonawa; zai zama tarin juji, za a sa wuta a ƙauyukan da suke kewayenta. Sa’an nan Isra’ila zai kori waɗanda suka kore shi,” in ji Ubangiji.
3 Yelle ye, Esebon, for Hay is distried; crie, ye douytris of Rabath, girde you with heiris, weile ye, and cumpasse bi heggis; for whi Melchon schal be lad in to passyng ouer, the prestis therof and princes therof togidere.
“Ki yi kuka, ya Heshbon, gama an hallaka Ai! Ku tā da murya ku yi kuka, ya mazaunan Rabba! Ku sa tufafin makoki; ku ruga nan da can a cikin katanga, gama Molek zai tafi bauta, tare da firistocinsa da kuma fadawansa.
4 What hast thou glorie in valeis? Thi valeis fleet awei, thou delicat douyter, that haddist trist in thi tresours, and seidist, Who schal come to me?
Me ya sa kuke taƙama da kwarurukanku, taƙama da kwarurukanku masu amfani? Ya ke diya marar aminci, kin dogara a wadatarki kika kuma ce, ‘Wa zai iya fāɗa mini?’
5 Lo! Y schal bringe in drede on thee, seith the Lord God of oostis, God of Israel, of alle men that ben in thi cumpasse; and ye schulen be scaterid, ech bi hym silf, fro youre siyt, and noon schal be, that gadere hem that fleen.
Zan kawo razana a kanki daga waɗanda suke kewaye da ke,” in ji Ubangiji Maɗaukaki. “Za a kore kowannenku, babu wani da zai tattara masu gudun hijira.
6 And after these thingis Y schal make the fleeris and prisoneris of the sones of Amon to turne ayen, seith the Lord.
“Duk da haka, daga baya, zan maido da wadatar Ammonawa,” in ji Ubangiji.
7 To Ydumee the Lord God of oostis seith these thingis. Whether wisdom is no more in Theman? Councel perischide fro sones, the wisdom of hem is maad vnprofitable.
Game da Edom. Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Babu sauran hikima a Teman ne? Shawara ta ɓace daga masu basira ne? Hikimarsu ta ruɓe ne?
8 Fle ye, and turne ye backis; go doun in to a swolowe, ye dwelleris of Dedan, for Y haue brouyt the perdicioun of Esau on hym, the tyme of his visitacioun.
Ku juya ku gudu, ku ɓuya a cikin kogwanni masu zurfi, ku da kuke zama a Dedan, gama zan kawo masifa a kan Isuwa a lokacin da zan hukunta shi.
9 If gadereris of grapis hadden come on thee, thei schulden haue left a clustre; if theues in the niyt, thei schulden haue rauyschid that that suffiside to hem.
In masu tsinkar’ya’yan inabi suka zo maka, ba za su rage’ya’yan inabi kaɗan ba? In ɓarayi suka zo da dare, ba za su sata abin da kawai suke bukata ba?
10 Forsothe Y haue vnhilid Esau, and Y haue schewid the hid thingis of hym, and he mai not mow be hid; his seed is distried, and hise britheren, and hise neiyboris, and it schal not be.
Amma zan washe Isuwa sarai; zan bubbuɗe wuraren ɓuyarsa, don kada yă ɓoye kansa.’Ya’yansa, danginsa da maƙwabtansa za su hallaka, ba kuwa zai ƙara kasancewa ba.
11 Forsake thi fadirles children, and Y schal make hem to lyue, and thi widewis schulen hope in me.
Ka bar marayunka; zan tsare ransu. Gwaurayenka kuma za su dogara a gare ni.”
12 For the Lord seith these thingis, Lo! thei drynkynge schulen drynke, to whiche was no doom, that thei schulden drynke the cuppe. And `schalt thou be left as innocent? thou schalt not be innocent, but thou drynkynge schalt drynke.
Ga abin da Ubangiji yana cewa, “In waɗanda ba su dace su sha kwaf ɗin ba suka sha shi, me ya sa za ka kuɓuta? Ba za ka kuɓuta ba, sai ka sha shi.
13 For Y swoor bi my silf, seith the Lord, that Bosra schal be in to wildirnesse, and in to schenschipe, and in to forsakyng, and in to cursyng; and alle the citees therof schulen be in to euerlastynge wildirnessis.
Na rantse da kaina,” in ji Ubangiji, “cewa Bozra za tă zama kufai da kuma abin tsoro, abin dariya da abin la’ana; kuma dukan garuruwanta za su kasance kufai har abada.”
14 I herde an heryng of the Lord, and Y am sent a messanger to hethene men; be ye gaderid togidere, and come ye ayens it, and rise we togidere in to batel.
Na ji saƙo daga Ubangiji cewa; an aiki jakada zuwa ga al’ummai ya ce, “Ku tattara kanku don ku fāɗa mata! Ku tashi don yaƙi!”
15 For lo! Y haue youe thee a litil oon among hethene men, despisable among men.
“Yanzu zan mai da kai ƙanƙani a cikin al’ummai abin reni a cikin mutane.
16 Thi boost, and the pride of thin herte, hath disseyued thee, that dwellist in the caues of stoon, and enforsist to take the hiynesse of a litil hil; whanne thou as an egle hast reisid thi nest, fro thennus Y schal drawe thee doun, seith the Lord.
Tsoron da ka sa ake ji da kuma girman kan zuciyarka ya ruɗe ka, kai da kake zama a kogon dutse, kai da kake kan tudu. Ko da yake ka gina wa kanka sheƙa can bisa kamar na gaggafa, daga can zan sauko da kai ƙasa,” in ji Ubangiji.
17 And Ydumee schal be forsakun; ech man that schal passe bi it, schal wondre, and schal hisse on alle the woundis therof;
“Edom za tă zama abin tsoro; dukan wanda ya wuce zai giggice ya yi tsaki saboda dukan mikinta.
18 as Sodom and Gommor is distried, and the niy citees therof, seith the Lord. A man schal not dwelle there, and the sone of man schal not enhabite it.
Kamar yadda aka tumɓuke Sodom da Gomorra, tare da garuruwan da suke maƙwabtaka da su,” in ji Ubangiji, “haka ba wanda zai zauna a can; ba wani da zai zauna a cikinta.
19 Lo! as a lioun he schal stie, fro the pride of Jordan to the strong fairnesse; for Y schal make hym renne sudenli to it; and who schal be the chosun man, whom Y schal sette bifore hym? For who is lijk to me, and who schal suffre me? and who is this scheepherde, that schal ayenstonde my cheer?
“Kamar zaki mai haurawa daga kurmin Urdun zuwa wurin kiwo mai kyau, zan kori Edom daga ƙasarta nan da nan. Wane ne zaɓaɓɓen da zan naɗa don wannan? Wane ne yake kama da ni kuma wa zai kalubalance ni? Kuma wane makiyayi ne zai yi gāba da ni?”
20 Therfor here ye the councel of the Lord, which he took of Edom, and his thouytis, whiche he thouyte of the dwelleris of Theman. If the litle of the floc caste not hem doun, if thei distrien not with hem the dwellyng of hem, ellis no man yyue credence to me.
Saboda haka, ku ji abin da Ubangiji ya shirya a kan Edom, abin da ya nufa wa waɗanda suke zama a Teman. Za a ja ƙanana na garken tumaki a tafi; zai hallaka wurin kiwonsu sarai saboda su.
21 The erthe was mouyd of the vois of fallyng of hem; the cry of vois therof was herd in the reed see.
Amon fāɗuwarsu zai sa ƙasa ta girgiza; za a kuma ji muryar kukansu a Jan Teku.
22 Lo! as an egle he schal stie, and fle out, and he schal sprede abrood hise wynges on Bosra; and the herte of the strong men of Idumee schal be in that dai, as the herte of a womman trauelynge of child.
Duba! Gaggafa tana firiya tana kuma saukowa, tana buɗe fikafikanta a bisa Bozra. A wannan rana zukatan jarumawan Edom za su zama kamar macen da take naƙuda.
23 To Damask. Emath is schent, and Arphath, for thei herden a ful wickid heryng; thei weren disturblid in the see, for angwisch thei miyten not haue reste.
Game da Damaskus. “Hamat da Arfad sun giggice, gama sun ji mummunar labari. Suna damuwa, sun damu kamar tekun da baya hutu.
24 Damask was discoumfortid, it was turned in to fliyt; tremblyng took it, angwischis and sorewis helden it, as a womman trauelynge of child.
Damaskus ta karai ta juya don ta gudu tsoro kuma ya kama ta; wahala da zafi sun kama ta, zafi kamar na mace mai naƙuda.
25 How forsoken thei a preisable citee, the citee of gladnesse?
Me ya sa ba a tafi aka bar sanannen birnin nan ba, birnin da nake jin daɗi?
26 Therfor the yonge men therof schulen falle in the stretis therof, and alle men of batel schulen be stille in that dai, seith the Lord of oostis.
Tabbatacce, samarinta za su fāɗi a tituna; dukan sojojinta za su yi shiru a wannan rana,” in ji Ubangiji Maɗaukaki.
27 And Y schal kyndle fier in the wal of Damask, and it schal deuoure the bildyngis of Benadab.
“Zan cinna wa katangar Damaskus wuta; za tă ci kagaran Ben-Hadad.”
28 To Cedar, and to the rewme of Azor, which Nabugodonosor, kyng of Babiloyne, smoot, the Lord seith these thingis. Rise ye, and stie to Cedar, and distrie ye the sones of the eest.
Game da Kedar da mulkokin Hazor, waɗanda Nebukadnezzar sarkin Babilon ya fāɗa wa. Ga abin da Ubangiji yana cewa, “Tashi, ku fāɗa wa Kedar ku kuma hallaka mutanen Gabas.
29 Thei schulen take the tabernaclis of hem, and the flockis of hem; thei schulen take to hem the skynnes of hem, and alle the vessels of hem, and the camels of hem; and thei schulen clepe on hem inward drede in cumpas.
Za a ƙwace tentunansu da garkunansu; za a tafi da mafakanta tare da dukan kayayyakinsu da raƙumansu. Mutane za su yi musu ihu, ‘Razana ko’ina!’
30 Fle ye, go ye awei greetli, ye that dwellen in Asor, sitte in swolewis, seith the Lord. For whi Nabugodonosor, kyng of Babiloyne, hath take councel ayens you, and he thouyte thouytis ayens you.
“Ku yi maza ku gudu! Ku zauna a kogo masu zurfi, ku da kuke zama a Hazor,” in ji Ubangiji. “Nebukadnezzar sarkin Babilon ya shirya muku maƙarƙashiya; ya ƙulla maƙarƙashiya a kanku.
31 Rise ye togidere, and stie ye to a pesible folk, and dwellinge tristili, seith the Lord; not doris nether barris ben to it, thei dwellen aloone.
“Ku tashi ku kuma fāɗa wa al’umma da sauƙi wadda take zama da ƙarfin hali,” in ji Ubangiji, “al’ummar da ba ta da ƙofofi ko ƙyamare; mutanenta suna zama su kaɗai.
32 And the camels of hem schulen be in to rauyschyng, and the multitude of her beestis in to prey; and Y schal schatere hem in to ech wynd, that ben biclippid on the long heer, and bi ech coost of hem Y schal brynge perischyng on hem, seith the Lord.
Za a washe raƙumansu, garkunansu mai girma za su zama ganima. Zan watsar da waɗanda suke a wurare masu nesa a ko’ina zan kuma kawo musu masifa a kowane gefe,” in ji Ubangiji.
33 And Asor schal be in to a dwellyng place of dragouns; it schal be forsakun `til in to withouten ende; a man schal not dwelle there, nether the sone of man schal enhabite it.
“Hazor za tă zama mazaunin diloli, kufai har abada. Ba wanda zai zauna a can; ba wanda zai zauna a cikinta.”
34 The word of the Lord that was maad to Jeremye, the profete, ayens Elam, in the bigynnyng of the rewme of Sedechie,
Ga maganar Ubangiji da ta zo wa Irmiya annabi game da Elam, a farkon mulkin Zedekiya sarkin Yahuda.
35 kyng of Juda, and seide, The Lord of oostis, God of Israel, seith these thingis, Lo! Y schal breke the bowe of Elam, and Y schal take the strengthe of hem.
Ga abin da Ubangiji Maɗaukaki yana cewa, “Ga shi, zan karye ƙarfin Elam, zaunannen ƙarfinsu.
36 And I schal bringe on Elam foure wyndis; fro foure coostis of heuene, and Y schal wyndewe hem in to alle these wyndis, and no folc schal be, to which the fleeris of Elam schulen not come.
Zan kawo a kan Elam a kusurwoyi huɗu daga kusurwoyi huɗu na duniya; zan watsar da su zuwa kusurwoyi huɗu, kuma ba al’ummar da masu gudun hijirar Elam ba za su kai ba.
37 And Y schal make Elam for to drede bifore her enemyes, and in the siyt of men sekynge the lijf of hem; and Y schal brynge on hem yuel, the wraththe of my strong veniaunce, seith the Lord; and Y schal sende after hem a swerd, til Y waste hem.
Zan ragargaza Elam a gaban maƙiyansu, a gaban waɗanda suke neman ransu; zan kawo masifa a kansu, da zafin fushina,” in ji Ubangiji. “Zan runtume su da takobi sai na kawo ƙarshensu.
38 And Y schal sette my kyngis seete in Elam, and Y schal leese therof kyngis, and princes, seith the Lord.
Zan sa kursiyina a Elam in kuma hallaka sarkinta da fadawanta,” in ji Ubangiji.
39 But in the laste daies Y schal make the prisoneris of Elam to turne ayen, seith the Lord.
“Duk da haka zan maido da wadatar Elam a kwanaki masu zuwa,” in ji Ubangiji.

< Jeremiah 49 >