< Luke 8 >

1 And it came to pass afterwards that He went through every city and village, preaching and declaring the good tidings of the kingdom of God: and the twelve were with Him;
Bayan wannan sai Yesu ya zazzaga gari da ƙauye, yana wa’azin bisharar mulkin Allah. Sha Biyun nan kuwa suna tare da shi,
2 and some women that had been cured of evil spirits and other infirmities, as Mary Magdalene, out of whom were cast seven demons,
da kuma waɗansu mata waɗanda aka warkar da su daga cututtukansu, da kuma mugayen ruhohi. Cikinsu akwai Maryamu (wadda ake kira Magdalin) wadda aljanu bakwai suka fito daga cikinta.
3 and Joanna the wife of Chuza Herod's steward, and Susanna, and many others, who assisted Him with their substance.
Da Yowanna matar Kuza, manajan iyalin Hiridus; da Suzana; da waɗansu mata da yawa. Waɗannan mata suna taimaka musu cikin hidima, daga cikin abin da suke da shi na zaman gari.
4 And when a great multitude was gathered together, of those that came to Him out of every city, He spake a parable saying,
Yayinda taron mai girma na taruwa, mutane kuma daga garuruwa dabam-dabam suna zuwa wurin Yesu, sai ya ba da wannan misali ya ce,
5 A sower went out to sow his seed, and as he was sowing, some fell by the way-side, and was trodden down, and the birds of the air devoured it.
“Wani manomi ya fita domin ya shuka irinsa. Da yana watsa irin, sai waɗansu suka fāɗi a kan hanya, aka tattaka su, tsuntsayen sararin sama kuma suka cinye su.
6 And some fell upon stony ground, and as soon as it sprung up, it withered away, because it had no moisture.
Waɗansu suka fāɗi a kan dutse, da suka tsira sai suka yanƙwane don babu ruwa a wurin.
7 And some fell among thorns, and the thorns sprang up with it and choked it.
Waɗansu kuma suka fāɗi a cikin ƙaya. Da suka yi girma tare, sai ƙayan suka shaƙe su.
8 But some fell on good ground, and sprang up and yielded fruit an hundred-fold. And as He said these things He cried out, "He that hath ears to hear, let him hear."
Waɗansu kuma har yanzu, suka fāɗi a ƙasa mai kyau, suka yi girma, suka ba da amfani riɓi ɗari-ɗari, fiye da abin da aka shuka.” Da faɗin haka sai ya ce, “Duk mai kunnen ji, yă ji.”
9 And his disciples asked Him, what might be the meaning of this parable.
Almajiransa suka tambaye shi ma’anar wannan misali.
10 And He said, To you it is granted to know the mysteries of the kingdom of God: but I speak to others in parables, that in seeing they may not see, and hearing they may not understand.
Sai ya ce, “Ku ne aka ba sanin asirin mulkin Allah, amma ga sauran mutane kam, ina magana da misalai, saboda, “‘ko da yake suna kallo, ba za su gani ba, ko da yake suna ji, ba za su gane ba.’
11 Now this is the meaning of the parable, The seed is the word of God:
“Ga ma’anar misalin, irin, shi ne maganar Allah.
12 and those by the way-side, are such as hear indeed; but then the devil cometh and taketh away the word from their hearts, least they should believe and be saved.
Waɗanda suka fāɗi a kan hanya su ne mutanen da suka ji, amma Iblis, yakan zo ya ɗauke maganar daga zuciyarsu, don kada su gaskata, su sami ceto.
13 And those on stony-ground are such as when they hear, receive the word with joy; but have no root, and so believe only for a while, and in the time of trial fall away.
Na kan dutse kuwa, su ne da jin maganar, sukan karɓa da murna, amma ba su da saiwa. Sukan gaskata na ɗan lokaci, amma lokacin gwaji, sai su ja da baya.
14 And that which fell among thorns, are those who when they have heard the word go away and are choked with the cares and riches, and pleasures of life, and bring no fruit to perfection.
Irin da suka fāɗi a cikin ƙaya kuwa, su ne mutanen da suka ji, amma a kwana a tashi, tunanin kayan duniya, da neman arziki, da son jin daɗi, sukan hana su ba da’ya’ya.
15 But that on the good ground, are those who having heard the word, retain it in a good and honest heart, and bring forth fruit with patience.
Amma irin da suka fāɗi a ƙasa mai kyau kuwa, su ne mutane masu kyakkyawar zuciya, mai kyau, da suka ji, suka riƙe, suka kuma jimre har suka ba da’ya’ya.”
16 No man when he hath lighted a candle covereth it with a vessel, or putteth it under a couch; but setteth it on a candlestick, that they who come in may see the light.
“Ba mai ƙuna fitila sa’an nan ya ɓoye ta a cikin tulu, ko kuma ya sa ta a ƙarƙashin gado ba. A maimakon haka, yakan sa ta a kan wurin ajiye fitila, saboda mutane masu shigowa su ga haske.
17 (For there is nothing secret, that shall not be made manifest: nor any thing concealed, which shall not be made known and come to light.)
Ba abin da yake ɓoye da ba za a fallasa ba. Kuma ba abin da yake rufe, da ba za a sani ba, ko a fitar da shi a fili ba.
18 Take heed therefore how ye hear: for whosoever improveth what he hath, to him shall more be given; and whosoever hath not, even what he seemeth to have shall be taken from him.
Saboda haka, ku yi tunani da kyau yadda kuke saurara. Duk wanda yake da shi, za a ƙara masa, duk wanda ba shi da shi kuma, abin da yake tsammani yana da shi ma, za a karɓe daga gare shi.”
19 Now his mother and his brethren came to Him, and could not come at Him for the croud:
Sai uwar Yesu da’yan’uwansa suka zo, domin su gan shi, amma ba su iya zuwa kusa da shi ba, saboda taron.
20 and it was told Him, Thy mother and thy brethren stand without desiring to see thee.
Sai wani ya faɗa masa cewa, “Ga uwarka da’yan’uwanka suna tsaye a waje suna so su gan ka.”
21 And He answered and said unto them, My mother and my brethren are these that hear the word of God and do it.
Ya amsa ya ce, “Mahaifiyata da’yan’uwana, su ne waɗanda suke jin maganar Allah, suna kuma aikata ta.”
22 And it came to pass on one of the days that He went into a ship, Himself and his disciples, and He said to them, Let us go over to the other side of the lake.
Wata rana Yesu ya ce wa almajiransa, “Mu haye zuwa wancan gefen tafkin.” Sai suka shiga jirgin ruwa suka fara tafiya.
23 And they launched forth: but as they were failing, He fell asleep: and a storm of wind came down upon the lake, and they were filled with water, and were in great danger.
Da suna cikin tafiya, sai barci ya kwashe shi. Sai wata babban iska ta taso kan tafkin, har ruwa ya fara shiga cikin jirgin. Suka shiga babban hatsari.
24 And they came to Him and awoke Him, saying, Master, master, we are perishing. Then He arose and rebuked the wind, and the raging of the water, and they ceased, and there was a calm.
Almajiran suka je suka tashe shi daga barci, suka ce, “Ubangiji, Ubangiji, za mu nutse!” Ya tashi ya kwaɓe iskar da kuma haukar ruwan. Sai ruwan da iskar suka natsu. Kome ya yi tsit.
25 And He said unto them, Where is your faith? But they were struck with awe and amazement, and said one to another, who is this? for He commandeth even the winds and the sea, and they obey Him.
Sai ya tambayi almajiransa, “Ina bangaskiyarku?” A cikin tsoro da mamaki, suka ce wa junansu, “Wane ne wannan? Yana ba da umarni ga iska da ruwa ma, kuma suna biyayya da shi?”
26 And they sailed to the country of the Gadarenes, which is over against Galilee.
Suka shiga jirgin ruwa zuwa yankin Gerasenawa da yake a hayin tafkin, daga wajen Galili.
27 And when He was landed, there met Him a man out of the city, who had been possessed by demons a long while, and wore no clothes, and abode in no dwelling but the tombs.
Da Yesu ya sauka daga jirgin, sai ga wani mutum mai aljanu daga garin. Mutumin ya daɗe bai sa tufafi ba, kuma ba ya zama a gida. Yana zama a cikin kaburbura.
28 But when he saw Jesus, he cried out and fell down to Him, and said with a loud voice, What have I to do with thee, Jesus, thou Son of the most high God? I beseech thee, do not torment me.
Da ya ga Yesu, sai mutumin ya ɗaga murya da ƙarfi, ya fāɗi a gabansa, yana ihu cewa, “Ina ruwanka da ni, Yesu, Ɗan Allah Mafi Ɗaukaka? Ina roƙonka, kada ka ba ni wahala!”
29 (For He commanded the impure spirit to come out of the man; which had oftentimes seized him so violently, that tho' he was bound with chains and fetters, yet he broke the bands asunder, and was driven by the demon into those lonely places.)
Gama Yesu ya riga ya umarci mugun ruhun ya fita daga mutumin. Sau da yawa mugun ruhun ya sha kamunsa. Ko da yake akan daure shi hannu da ƙafa, da sarƙa, a kuma yi gadinsa, amma yakan tsinke sarƙoƙinsa, aljanun kuma su kore shi zuwa wuraren kaɗaici, inda ba kowa.
30 And Jesus asked him, saying, What is thy name? and he said, Legion: because many demons were entred into him.
Yesu ya tambaye shi, “Mene ne sunanka?” Sai ya amsa, “Tuli,” gama aljanu masu ɗumbun yawa ne suna cikinsa.
31 And they besought Him that He would not command them to go into the abyss: (Abyssos g12)
Suka yi ta roƙonsa kada yă umarce su su shiga ramin Abis. (Abyssos g12)
32 but as there was there an herd of many swine feeding on the mountain, they intreated Him that He would suffer them to enter into them, and He permitted them.
A wurin kuwa, akwai babban garken aladu da suke kiwo a gefen tudu. Aljanun suka roƙi Yesu ya bar su, su shiga cikin aladun, ya kuwa yardar musu.
33 So the demons went out of the man and entred into the swine: and the herd ran violently down the hill into the lake and were drowned.
Da aljanun suka fita daga cikin mutumin, sai suka shiga cikin aladun. Garken kuma ya gangara daga kan tudun zuwa cikin tafkin, kuma suka nutse.
34 And when those that looked after them saw what was done they fled; and went and told it in city and country:
Da masu kiwon aladun suka ga abin da ya faru, sai suka ruga da gudu zuwa garin da kewaye suka kai labari.
35 and the people went out to see what was done, and came to Jesus; and found the man, from whom the demons were gone out, sitting at the feet of Jesus, clothed and in his right mind:
Mutanen kuma suka fito don su ga abin da ya faru. Da suka iso wurin Yesu, sai suka tarar da mutumin da aljanun suka fita daga cikinsa, yana zaune kusa da Yesu sanye da tufafi, kuma cikin hankalinsa, sai tsoro ya kama su.
36 and they were afraid, for those that saw it told them how the demoniac was healed.
Waɗanda suka ga abin da faru, suka gaya wa mutanen yadda aka warkar da mai aljanun.
37 And all the people of the country round about the Gadarenes desired Him to depart from them; for they were seized with great fear: and He went into the ship and returned.
Sai dukan mutanen yankin Gerasenawa suka roƙi Yesu ya bar su, don sun tsorata sosai. Sai Yesu ya shiga jirgin ruwa ya tafi.
38 Now the man from whom the demons were gone out, prayed Him to let him be with Him: but Jesus sent him away,
Mutumin da aka fitar da aljanun daga cikinsa, ya roƙi Yesu don yă tafi tare da shi, amma Yesu ya sallame shi ya ce,
39 saying, Return home, and relate what God hath done for thee. So he went away publishing through the whole city what great things Jesus had done to him.
“Koma gida, ka shaida babban alherin da Allah ya yi maka.” Sai mutumin ya tafi yana faɗin abin da Yesu ya yi masa a duk garin.
40 And when Jesus returned, a great multitude of people received Him; for they were all waiting for Him.
Da Yesu ya koma, taron suka marabce shi, don dā ma duk suna jiransa.
41 And behold there came a man whose name was Jairus, a ruler of the synagogue, and he fell at the feet of Jesus, and intreated Him to come into his house:
Sai wani mutum mai suna Yayirus, wani mai mulkin majami’a, ya zo ya fāɗi a gaban Yesu, yana roƙonsa ya zo gidansa,
42 for he had an only daughter, about twelve years old, and she was dying. (But as He was going, the people crouded Him:
domin diyarsa ɗaya tak, wadda ta kai shekara goma sha biyu, tana bakin mutuwa. Da Yesu yake kan hanyarsa, taron mutane masu yawa suka yi ta matsa shi a kowane gefe.
43 and a woman who had been in a flux twelve years, and had spent her whole livelyhood upon physicians,
A wurin kuwa, akwai wata mace wadda tana da ciwon zubar da jini, har na shekara goma sha biyu, amma babu wanda ya iya warkar da ita.
44 but could not be healed by any, came close behind Him and touched the hem of his garment, and immediately her flux was stopt.
Sai ta zo ta bayansa, ta taɓa bakin rigarsa. Nan da nan, zubar da jininta ya tsaya.
45 And Jesus said, Who touched me? When all denied it, Peter, and those that were with him, said, Sir, the multitudes throng and press thee, and dost thou ask, Who was it that touched me?
Yesu ya yi tambaya, “Wa ya taɓa ni?” Bayan kowa ya yi musu, sai Bitrus ya ce, “Ubangiji, ai, mutane da yawa suna matsinka ta kowane gefe.”
46 And Jesus said, Somebody hath touched me: for I perceive a peculiar virtue is gone out of me.
Amma Yesu ya ce, “Wani ya taɓa ni, na san cewa iko ya fita daga wurina.”
47 And when the woman saw that she was not concealed, she came trembling, and fell down to Him, and declared before all the people, for what reason she had touched Him, and how she was healed immediately.
Sai macen, da ta ga ba halin ɓoyewa, sai ta fita, jikinta na rawa, ta fāɗi a gabansa. A gaban dukan mutanen, ta faɗi dalilin da ya sa ta taɓa shi, da yadda ta warke nan take.
48 And He said unto her, Daughter, be comforted, thy faith has healed thee, go in peace.)
Sai Yesu ya ce mata, “Diyata, bangaskiyarki ta warkar da ke. Ki sauka lafiya.”
49 While He was yet speaking, there cometh one from the ruler of the synagogue's, and said to Him, Thy daughter is dead, trouble not the Master.
Yayinda Yesu na cikin magana har yanzu, sai ga wani daga gidan Yayirus, mai mulkin majami’ar ya ce, “Kada ka ƙara damun malam, diyarka ta rasu.”
50 But Jesus hearing it, answered saying, Fear not, only believe, and she shall be recovered.
Da Yesu ya ji wannan, sai ya ce wa Yayirus, “Kada ka ji tsoro, ka gaskata, za a kuma warkar da ita.”
51 And when He came to the house, He suffered none to go in but Peter, and James, and John, and the father and mother of the child.
Da ya iso gidan Yayirus, sai ya hana kowa yă bi shi cikin ɗakin, sai dai Bitrus, da Yohanna, da Yaƙub, da kuma mahaifin da mahaifiyar.
52 And they were all weeping and bewailing her: but He said, Weep not; she is not dead, but sleepeth.
Ana cikin haka, dukan mutanen kuma sai kuka da makoki suke ta yi, domin yarinyar. Sai Yesu ya ce, “Ka daina yin kuka, ba tă mutu ba, tana barci ne.”
53 And they laughed at Him, knowing that she was dead.
Sai suka yi masa dariya, da yake sun san cewa, ta mutu.
54 But He turned them all out, and taking hold of her hand, called to her, saying, Child, arise.
Amma Yesu ya kama ta a hannu ya ce, “Diyata, tashi.”
55 And her spirit returned, and immediately she stood up: and He ordered something to be given her to eat.
Ruhunta ya dawo, kuma ta tashi, nan take. Yesu ya ce musu, su ba ta wani abu tă ci.
56 And her parents were exceedingly astonished: but He charged them to tell no one what was done.
Iyayenta suka yi mamaki, amma ya ba su umarni kada su faɗa wa kowa abin da ya faru.

< Luke 8 >