< Luke 1 >

1 Whereas many have undertaken to compose a narrative of the things, which have been fully certified among us;
Mutane da yawa sun ɗau niyyar rubuta labarin abubuwan da aka cika a cikinmu,
2 as they delivered them to us, who were from the beginning eye-witnesses of them, and ministers of the word;
kamar yadda muka karɓe su daga waɗanda tun farko shaidu ne da kuma masu hidimar bishara.
3 it seemed good to me also, having thoroughly traced them all from the very first, to write an account of them in order to thee,
Saboda haka, da yake ni da kaina na binciko kome a hankali daga farko, na ga ya yi kyau in rubuta maka labarin dalla-dalla, ya mafifici Tiyofilus,
4 most excellent Theophilus, that thou mayst know the certainty of the things wherein thou hast been instructed.
don ka san tabbacin abubuwan da aka koyar da kai.
5 There was in the days of Herod king of Judea, a certain priest named Zacharias, of the course of Abia; and his wife was of the family of Aaron, and her name was Elisabeth.
A lokacin da Hiridus ne yake sarautar Yahudiya, an yi wani firist mai suna Zakariya, na sashin firistoci gidan Abiya. Matarsa Elizabet ma’yar zuriyar Haruna ce.
6 And they were both righteous in the sight of God, walking in all the commandments and ordinances of the Lord blameless.
Dukansu biyu kuwa masu adalci ne a gaban Allah, suna kuma bin umarnan Ubangiji da farillansa duka da halin rashin zargi.
7 And they had no child, for Elisabeth was barren; and they were both far advanced in years.
Sai dai ba su da’ya’ya, domin Elizabet bakararriya ce; kuma dukansu biyu sun tsufa.
8 And it came to pass, while he was in the order of his course performing the priest's office before God,
Wata rana da lokacin aikin firistoci na sashen Zakariya na yin hidima ya kewayo, yana kuma cikin hidimarsa ta firist a gaban Allah,
9 according to the custom of dividing the office of the priests, that it fell to his lot to burn incense, entring into the temple of the Lord:
sai aka zaɓe shi ta wurin ƙuri’a, bisa ga al’adar aikin firist, yă shiga haikalin Ubangiji yă ƙone turare.
10 and all the people were praying without at the time of offering incense.
Da lokacin ƙone turare ya yi, duk taron masu sujada suna a waje suna addu’a.
11 And there appeared to him an angel of the Lord standing on the right hand of the altar of incense.
Sai mala’ikan Ubangiji ya bayyana gare shi, tsaye a dama da bagaden turare.
12 And when Zacharias saw him, he was startled and struck with fear:
Da Zakariya ya gan shi sai ya firgita, tsoro kuma ya kama shi.
13 but the angel said unto him, Fear not, Zacharias; for thy prayer is heard, and thy wife Elisabeth shall bear thee a son, and thou shalt call his name John:
Amma mala’ikan ya ce masa, “Kada ka ji tsoro, Zakariya; an ji addu’arka. Matarka Elizabet za tă haifa maka ɗa, za ka kuma ba shi suna Yohanna.
14 and he shall be a joy and transport to thee, yea, many shall rejoice on account of his birth; for he shall be great in the sight of the Lord,
Zai zama abin murna da farin ciki a gare ka, mutane da yawa kuwa za su yi murna don haihuwarsa,
15 and he shall drink neither wine nor any other strong liquor; and he shall be filled with the holy Spirit even from his birth;
gama zai zama mai girma a gaban Ubangiji. Ba kuwa zai taɓa shan ruwan inabi ko wani abu mai sa maye ba. Zai cika da Ruhu Mai Tsarki tun haihuwa.
16 and many of the children of Israel shall he convert unto the Lord their God.
Shi ne zai juye mutanen Isra’ila da yawa zuwa wurin Ubangiji Allahnsu.
17 And he shall go before Him in the spirit and power of Elias, to turn the hearts of the fathers unto the children, and the disobedient to the wisdom of the just, to prepare for the Lord a people well-disposed.
Zai sha gaban Ubangiji, a ruhu da kuma iko irin na Iliya, domin yă juye zukatan iyaye ga’ya’yansu, marasa biyayya kuma ga zama masu biyayya don yă kintsa mutane su zama shiryayyu domin Ubangiji.”
18 And Zacharias said unto the angel, Whereby shall I know this? for I am an old man, and my wife far advanced in years.
Sai Zakariya ya tambayi mala’ikan ya ce, “Yaya zan tabbatar da wannan? Ga ni tsoho, matana kuma ta kwana biyu.”
19 And the angel answering said to him, I am Gabriel, that stand in the presence of God, and I am sent to speak to thee, and to tell thee this good news:
Mala’ikan ya ce, “Ni ne Jibra’ilu. Ina tsaya a gaban Allah, an kuma aiko ni in yi maka magana, in kuma faɗa maka wannan labari mai daɗi.
20 and now shalt thou be dumb, and not able to speak, until the day that these things shall come to pass; because thou believedst not my words, which shall be fulfilled at their season.
Yanzu za ka zama bebe, ba za ka ƙara iya magana ba sai ranar da wannan magana ta cika, saboda ba ka gaskata da kalmomina waɗanda za su zama gaskiya a daidai lokacinsu ba.”
21 And the people were waiting for Zacharias, and wondered at his staying so long in the temple:
Ana cikin haka, mutane suna jiran Zakariya, suna kuma mamaki me ya sa ya daɗe haka a cikin haikali.
22 but when he came out he could not speak to them, and they perceived that he had seen a vision in the temple; and he made signs to them, and continued speechless:
Da ya fito, bai iya yin musu magana ba. Sai suka gane, ya ga wahayi ne a haikali, domin ya dinga yin musu alamu, amma ya kāsa yin magana.
23 and as soon as the days of his ministration were accomplished, he departed to his own house.
Da lokacin hidimarsa ya cika, sai ya koma gida.
24 And after these days his wife Elisabeth conceived, and retired five months,
Bayan wannan, matarsa Elizabet ta yi ciki, ta kuma riƙa ɓuya har wata biyar.
25 saying, the Lord hath thus dealt with me in the days wherein he looked upon me to take away my reproach among men.
Sai ta ce, “Ubangiji ne ya yi mini wannan. A waɗannan kwanaki ya nuna tagomashinsa ya kuma kawar mini da kunya a cikin mutane.”
26 But in the sixth month the angel Gabriel was sent by God to a city of Galilee called Nazareth,
A wata na shida, sai Allah ya aiki mala’ika Jibra’ilu zuwa Nazaret, wani gari a Galili,
27 to a virgin who was betrothed to a man, whose name was Joseph, of the house of David; and the name of the virgin was Mary.
gun wata budurwar da aka yi alkawarin aurenta ga wani mutum mai suna Yusuf daga zuriyar Dawuda. Sunan budurwar Maryamu.
28 And when the angel came in to the room to her, he said, Hail, thou that art highly favoured; the Lord is with thee;
Mala’ikan ya je wurinta ya ce, “A gaishe ki, ya ke da kika sami tagomashi ƙwarai! Ubangiji yana tare da ke.”
29 blessed art thou among women! and when she saw him, she was confused at what he said, and pondered in her mind what sort of salutation this could be.
Maryamu ta damu ƙwarai da kalmominsa, tana tunani wace irin gaisuwa ce haka?
30 And the angel said unto her, Fear not, Mary; for thou hast found favor with God:
Amma mala’ikan ya ce mata, “Kada ki ji tsoro, Maryamu, kin sami tagomashi a wurin Allah.
31 and behold thou shalt conceive in thy womb, and shalt bring forth a son, and shalt call his name JESUS:
Ga shi za ki yi ciki ki kuma haifi ɗa, za ki kuma ba shi suna Yesu.
32 He shall be great, and shall be called the Son of the Most High, and the Lord God shall give Him the throne of David his father,
Zai zama mai girma, za a kuma kira shi Ɗan Maɗaukaki. Ubangiji Allah zai ba shi gadon sarautar kakansa Dawuda,
33 and He shall reign over the house of Jacob for ever, and of his kingdom there shall be no end. (aiōn g165)
zai yi mulkin gidan Yaƙub har abada, mulkinsa kuma ba zai taɓa ƙare ba.” (aiōn g165)
34 Then said Mary to the angel, How can this be, since I am a virgin?
Maryamu ta tambayi mala’ikan ta ce, “Yaya wannan zai yiwu, da yake ni budurwa ce?”
35 And the angel answered and said unto her, The holy Spirit shall come upon thee, and the power of the Most High shall overshadow thee, and therefore thine holy offspring shall be called the Son of God: and lo,
Mala’ikan ya amsa ya ce, “Ruhu Mai Tsarki zai sauko miki, ikon Maɗaukaki kuma zai rufe ke. Saboda haka, Mai Tsarkin nan da za a haifa, za a kira shi Ɗan Allah.
36 thy cousin Elisabeth also hath conceived a son in her old age, and this is the sixth month with her that was called barren;
’Yar’uwarki Elizabet ma za tă haifi ɗa a tsufanta, ita da aka ce bakararriya, ga shi tana a watanta na shida.
37 for nothing is impossible with God.
Gama ba abin da zai gagari Allah.”
38 Then Mary said, Behold the servant of the Lord, may it be unto me according to thy word. So the angel departed from her.
Maryamu ta amsa ta ce, “To, ni baiwar Allah ce, bari yă zama mini kamar yadda ka faɗa.” Sai mala’ikan ya tafi abinsa.
39 Then Mary arose and went with speed into the hill-country, to a city of Juda,
A lokacin sai Maryamu ta shirya ta gaggauta zuwa wani gari a ƙasar tudu ta Yahudiya,
40 and came into the house of Zacharias, and saluted Elisabeth.
inda ta shiga gidan Zakariya ta kuma gai da Elizabet.
41 And as soon as Elisabeth heard the salutation of Mary, the child leaped in her womb, and Elisabeth was filled with the holy Spirit:
Da Elizabet ta ji gaisuwar Maryamu, sai jaririn da yake a cikinta ya yi motsi. Elizabet kuma ta cika da Ruhu Mai Tsarki.
42 and she cried out with a loud voice, and said, Blessed art thou among women, and blessed is the fruit of thy womb:
Sai ta ɗaga murya da ƙarfi ta ce, “Ke mai albarka ce a cikin mata. Mai albarka ne kuma ɗan da za ki haifa!
43 and whence is this honor to me, that the mother of my Lord should come to me?
Me ya sa na sami wannan tagomashi har da mahaifiyar Ubangijina za tă zo wurina?
44 for behold, as soon as the voice of thy salutation reached my ears, the child in my womb leaped for joy:
Da jin gaisuwarki, sai jaririn da yake cikina ya yi motsi don murna.
45 and blessed is she that believed; for there shall be a performance of the things that were told her from the Lord.
Mai albarka ce wadda ta gaskata cewa abin da Ubangiji ya faɗa mata zai cika!”
46 And Mary said, "My soul doth magnify the Lord, and my spirit hath rejoiced in God my Saviour;
Sai Maryamu ta ce, “Raina yana ɗaukaka Ubangiji
47 for He hath regarded the low estate of his handmaid:
ruhuna kuma yana farin ciki da Allah Mai Cetona,
48 for behold, from henceforth shall all generations call me blessed:
gama ya lura da ƙasƙancin baiwarsa. Daga yanzu nan gaba dukan zamanai za su ce da ni mai albarka,
49 for He that is mighty hath done great things for me,
gama Mai Iko Duka ya yi mini manyan abubuwa, sunansa labudda Mai Tsarki ne.
50 and his name is holy, and his mercy is on them that fear Him, unto all generations.
Jinƙansa ya kai ga masu tsoronsa, daga zamani zuwa zamani.
51 He hath wrought powerfully with his arm; He hath confounded those that were proud in the imagination of their heart.
Ya aikata manyan ayyuka da hannunsa; ya watsar da waɗanda suke masu girman kai a zurfin tunaninsu.
52 He hath cast down the mighty from their thrones, and exalted the humble.
Ya saukar da masu mulki daga gadajen sarautarsu amma ya ɗaukaka ƙasƙantattu.
53 He hath filled the hungry with good things, and the rich He hath sent away empty.
Ya ƙosar da masu yunwa da kyawawan abubuwa amma ya sallami mawadata hannu wofi.
54 He hath supported Israel his servant,
Ya taimaki bawansa Isra’ila, yana tunawa yă nuna jinƙai
55 in remembrance of his mercy (even as He promised to our fathers, to Abraham and to his seed, ) for ever." (aiōn g165)
ga Ibrahim da zuriyarsa har abada, kamar yadda ya faɗa wa kakanninmu.” (aiōn g165)
56 And Mary stayed with her about three months, and then returned to her own house.
Maryamu ta zauna da Elizabet kusan wata uku sa’an nan ta koma gida.
57 Now when Elisabeth's time for her delivery was fully come, she brought forth a son:
Sa’ad da kwanaki suka yi don Elizabet ta haihu, sai ta haifi ɗa.
58 and her neighbours and kindred heard that the Lord had magnified his mercy towards her, and they congratulated her;
Maƙwabtanta da’yan’uwanta suka ji cewa Ubangiji ya nuna mata jinƙai mai yawa, suka kuma taya ta farin ciki.
59 and on the eighth day they came to circumcise the child: and they would have called him Zacharias, after the name of his father:
A rana ta takwas, sai suka zo don a yi wa yaron kaciya, dā za su sa masa sunan mahaifinsa Zakariya ne,
60 but his mother said, No, but he shall be called John:
amma mahaifiyar yaron ta ce, “A’a! Za a ce da shi Yohanna.”
61 and they said to her, There is none of thy relations of this name.
Sai suka ce mata, “Ba wani a cikin danginku mai wannan suna.”
62 And they made signs to his father, what name he would have him called by.
Sai suka yi alamu wa mahaifinsa, don su san sunan da zai su a kira yaron.
63 And he called for a writing-tablet, and wrote upon it, His name is John: and they all wondered.
Ya yi alama a kawo masa allo, a gaban kowa sai ya rubuta, “Sunansa Yohanna.” Dukan mutane kuwa suka yi mamaki.
64 And his mouth was opened immediately, and his tongue loosed, and he spake and praised God.
Nan da nan bakinsa ya buɗe harshensa kuma ya saku, sai ya fara magana yana yabon Allah.
65 And an awe fell upon all that dwelt round about them; and all these things were divulged through the whole hill-country of Judea.
Maƙwabta duk suka cika da tsoro, mutane kuwa suka yi ta yin magana game da dukan waɗannan abubuwa a ko’ina a cikin ƙasar tudu ta Yahudiya.
66 And all that heard them, laid them up in their hearts, saying, What a child will this be? And the hand of the Lord was with him.
Duk waɗanda suka ji wannan kuwa sun yi mamaki suna cewa, “To, me yaron nan zai zama?” Gama hannun Ubangiji yana tare da shi.
67 And his father Zacharias was filled with the holy Spirit,
Mahaifinsa Zakariya ya cika da Ruhu Mai Tsarki sai ya yi annabci ya ce,
68 and prophesied, saying, "Blessed be the Lord God of Israel, for He hath visited and wrought redemption for his people,
“Yabo ya tabbata ga Ubangiji, Allah na Isra’ila, domin ya zo ya kuma fanshe mutanensa.
69 and hath raised up an horn of salvation for us,
Ya tā mana ƙahon ceto a gidan bawansa Dawuda
70 in the house of his servant David, as He spake by the mouth of his holy prophets from the beginning, (aiōn g165)
(yadda ya yi magana tun tuni ta wurin annabawansa masu tsarki), (aiōn g165)
71 even salvation from our enemies, and from the hand of all that hate us,
cewa zai cece mu daga abokan gābanmu daga kuma hannun dukan waɗanda suke ƙinmu
72 to display his mercy towards our fathers, and to remember his holy covenant,
don yă nuna jinƙai ga kakanninmu, yă kuma tuna da alkawarinsa mai tsarki,
73 according to the oath which He sware to Abraham our father,
rantsuwar da ya yi wa mahaifinmu Ibrahim,
74 to grant unto us, that we being delivered out of the hand of our enemies, might serve Him without fear, in holiness and righteousness before Him,
don yă kuɓutar da mu daga hannun abokan gābanmu, yă kuma sa mu iya yin masa hidima babu tsoro,
75 all the days of our life.
cikin tsarki da adalci a gabansa dukan kwanakinmu.
76 And thou, my child, shalt be called the prophet of the most High; for thou shalt go before the face of the Lord,
“Kai kuma, ɗana, za a ce da kai annabin Maɗaukaki; gama za ka sha gaban Ubangiji don ka shirya masa hanya,
77 to make known salvation to his people,
don ka sanar da mutanensa ceto, ta wurin gafarar zunubansu,
78 in the remission of their sins, through the tender mercy of our God, whereby the day-spring hath visited us from on high,
saboda jinƙai na Allahnmu mai ƙauna, hasken nan na ceto zai ɓullo mana daga sama,
79 to enlighten them that sit in darkness and in the shadow of death, to direct our feet into the way of peace."
don yă haskaka a kan waɗanda suke zama cikin duhu, da kuma cikin inuwar mutuwa, don yă bi da ƙafafunmu a hanyar salama.”
80 And the child grew, and became strong in spirit: and he was in the deserts till the time of his being manifested to Israel.
Yaron kuwa ya yi girma ya kuma ƙarfafa a ruhu; ya zauna a hamada sai lokacin da ya fito a fili ga mutanen Isra’ila.

< Luke 1 >