< Psalms 96 >

1 Sing to the LORD a new song! Sing to the LORD, all the earth.
Ku rera sabuwar waƙa ga Ubangiji; ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka.
2 Sing to the LORD! Bless his name! Proclaim his salvation from day to day!
Ku rera ga Ubangiji, ku yabe sunansa; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
3 Declare his glory among the nations, his marvelous works among all the peoples.
Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, manyan ayyukansa a cikin dukan mutane.
4 For the LORD is great, and greatly to be praised! He is to be feared above all gods.
Gama da girma Ubangiji yake, ya kuma cancanci yabo; tilas a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
5 For all the gods of the peoples are idols, but the LORD made the heavens.
Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ne ya yi sammai.
6 Honor and majesty are before him. Strength and beauty are in his sanctuary.
Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da ɗaukaka suna a cikin tsarkakar wurinsa.
7 Ascribe to the LORD, you families of nations, ascribe to the LORD glory and strength.
Ku ba wa Ubangiji, ya iyalan al’ummai ku ba wa Ubangiji ɗaukaka da kuma ƙarfi.
8 Ascribe to the LORD the glory due to his name. Bring an offering, and come into his courts.
Ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku kawo sadaka ku kuma zo cikin filayen gidansa.
9 Worship the LORD in holy array. Tremble before him, all the earth.
Ku bauta wa Ubangiji da darajar tsarkinsa; ku yi rawar jiki a gabansa, dukan duniya.
10 Say among the nations, “The LORD reigns.” The world is also established. It can’t be moved. He will judge the peoples with equity.
Ku faɗa cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki.” Duniya ta kahu daram, ba za a iya matsar da ita ba; zai yi wa mutane hukunci da gaskiya.
11 Let the heavens be glad, and let the earth rejoice. Let the sea roar, and its fullness!
Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari teku tă yi ruri, da kuma dukan abin da yake cikinsa;
12 Let the field and all that is in it exult! Then all the trees of the woods shall sing for joy
bari gonaki su yi tsalle da murna, da kuma kome da yake cikinsu. Ta haka dukan itatuwan kurmi za su rera don farin ciki;
13 before the LORD; for he comes, for he comes to judge the earth. He will judge the world with righteousness, the peoples with his truth.
za su rera a gaban Ubangiji, gama yana zuwa, yana zuwa don yă hukunta duniya. Zai hukunta duniya cikin adalci mutane kuma cikin amincinsa.

< Psalms 96 >