< Psalms 94 >

1 LORD, you God to whom vengeance belongs, you God to whom vengeance belongs, shine out.
Ya Ubangiji, Allahn da yake ramuwa, Ya Allah wanda yake ramuwa, ka haskaka.
2 Rise up, you judge of the earth. Pay back the proud what they deserve.
Ka tashi, ya Alƙalin duniya; ka sāka wa masu girman kai abin da ya dace da su.
3 LORD, how long will the wicked, how long will the wicked triumph?
Har yaushe mugaye, ya Ubangiji har yaushe mugaye za su yi ta murna?
4 They pour out arrogant words. All the evildoers boast.
Suna ta yin maganganun fariya; dukan masu aikata mugunta sun cika da fariya.
5 They break your people in pieces, LORD, and afflict your heritage.
Suna murƙushe mutanenka, ya Ubangiji; suna danne gādonka.
6 They kill the widow and the alien, and murder the fatherless.
Suna kashe gwauraye da kuma baƙi; suna kisan marayu.
7 They say, “The LORD will not see, neither will Jacob’s God consider.”
Suna ce, “Ubangiji ba ya gani; Allah na Yaƙub bai kula ba.”
8 Consider, you senseless among the people; you fools, when will you be wise?
Ku mai da hankali, ku marasa azanci a cikin mutane; ku wawaye, yaushe za ku zama masu hikima?
9 He who implanted the ear, won’t he hear? He who formed the eye, won’t he see?
Shi da ya sa kunne ba don a ji ba ne? Shi da ya yi ido ba don yă gani ba ne?
10 He who disciplines the nations, won’t he punish? He who teaches man knows.
Shi da yake yi wa al’ummai horo ba ya hukunci ne? Shi da yake koya wa mutum ba shi da sani ne?
11 The LORD knows the thoughts of man, that they are futile.
Ubangiji ya san tunanin mutum; ya san cewa tunaninsu banza ne.
12 Blessed is the man whom you discipline, LORD, and teach out of your Torah,
Mai albarka ne mutumin da ka yi masa horo, ya Ubangiji, mutumin da ka koyar daga dokarka;
13 that you may give him rest from the days of adversity, until the pit is dug for the wicked.
kana ba shi sauƙi a lokacin wahala, sai har an haƙa rami wa mugaye.
14 For the LORD won’t reject his people, neither will he forsake his inheritance.
Gama Ubangiji ba zai ƙi mutanensa ba; ba zai taɓa yashe gādonsa ba.
15 For judgment will return to righteousness. All the upright in heart shall follow it.
Za a sāke kafa hukunci a kan adalci, kuma dukan masu adalci a zuciya za su bi shi.
16 Who will rise up for me against the wicked? Who will stand up for me against the evildoers?
Wane ne zai yi gāba da mugaye domina? Wane ne zai ɗauki matsayi ya yi gāba da masu aikata mugunta domina?
17 Unless the LORD had been my help, my soul would have soon lived in silence.
Da ba don Ubangiji ya yi mini taimako ba, da tuni na zauna shiru a wurin mutuwa.
18 When I said, “My foot is slipping!” Your loving kindness, LORD, held me up.
Sa’ad da na ce, “Ƙafata na santsi,” ƙaunarka, ya Ubangiji, ta riƙe ni.
19 In the multitude of my thoughts within me, your comforts delight my soul.
Sa’ad da alhini ya yi yawa a cikina, ta’aziyyarka ta kawo farin ciki wa raina.
20 Shall the throne of wickedness have fellowship with you, which brings about mischief by statute?
Zai yiwu kursiyin da ya cika da lalaci yă haɗa kai da kai, wanda yake kawo azaba ta wurin abin da ya zartar?
21 They gather themselves together against the soul of the righteous, and condemn the innocent blood.
Sun yi ƙungiya tare a kan mai adalci suka yanke wa marar laifi hukuncin mutuwa.
22 But the LORD has been my high tower, my God, the rock of my refuge.
Amma Ubangiji ya zama kagarata, Allahna kuma dutsen da nake samun mafaka.
23 He has brought on them their own iniquity, and will cut them off in their own wickedness. The LORD, our God, will cut them off.
Zai sāka musu saboda zunubansu yă kuma hallaka su saboda muguntarsu; Ubangiji Allahnmu zai hallaka su.

< Psalms 94 >