< Psalms 89 >

1 A contemplation by Ethan, the Ezrahite. I will sing of the loving kindness of the LORD forever. With my mouth, I will make known your faithfulness to all generations.
Maskil na Etan dangin Ezra. Zan rera game da ƙauna mai girma ta Ubangiji har abada; da bakina zan sanar da amincinka a dukan zamanai.
2 I indeed declare, “Love stands firm forever. You established the heavens. Your faithfulness is in them.”
Zan furta cewa ƙaunarka tana nan daram har abada, cewa ka kafa amincinka a sama kanta.
3 “I have made a covenant with my chosen one, I have sworn to David, my servant,
Ka ce, “Na yi alkawari da zaɓaɓɓena, na rantse wa Dawuda bawana,
4 ‘I will establish your offspring forever, and build up your throne to all generations.’” (Selah)
cewa ‘Zan kafa zuriyarka har abada in kuma sa kursiyinka yă tsaya daram dukan zamanai.’” (Sela)
5 The heavens will praise your wonders, LORD, your faithfulness also in the assembly of the holy ones.
Sammai na yabon abubuwan banmamakinka, ya Ubangiji, amincinka shi ma, a cikin taron tsarkakanka.
6 For who in the skies can be compared to the LORD? Who among the sons of the heavenly beings is like the LORD,
Gama wane ne a sarari za a iya kwatanta da Ubangiji? Wane ne yake kamar Ubangiji a cikin talikan samaniya?
7 a very awesome God in the council of the holy ones, to be feared above all those who are around him?
Cikin taron tsarkaka Allah ne aka fi tsoro; shi ne mafi bantsoro fiye da dukan waɗanda suka kewaye shi.
8 LORD, God of Hosts, who is a mighty one, like you? LORD, your faithfulness is around you.
Ya Ubangiji Allah Maɗaukaki, wane ne kamar ka? Kai mai iko ne, ya Ubangiji, kuma amincinka ya kewaye ka.
9 You rule the pride of the sea. When its waves rise up, you calm them.
Kana mulkin teku mai tumbatsa; sa’ad da raƙuma sun tashi, kakan kwantar da su.
10 You have broken Rahab in pieces, like one of the slain. You have scattered your enemies with your mighty arm.
Ka ragargaza Rahab kamar waɗanda aka kashe; da hannunka mai ƙarfi ka watsar da abokan gābanka.
11 The heavens are yours. The earth also is yours, the world and its fullness. You have founded them.
Sammai naka ne, haka kuma duniya; ka kafa duniya da dukan abin da yake cikinta.
12 You have created the north and the south. Tabor and Hermon rejoice in your name.
Ka halicce arewa da kudu; Tabor da Hermon suna rera don farin ciki ga sunanka.
13 You have a mighty arm. Your hand is strong, and your right hand is exalted.
Hannunka mai iko ne; hannunka yana da ƙarfi, hannunka na dama ya sami ɗaukaka.
14 Righteousness and justice are the foundation of your throne. Loving kindness and truth go before your face.
Adalci da gaskiya su ne tushen kursiyinka; ƙauna da aminci suna tafiya a gabanka.
15 Blessed are the people who learn to acclaim you. They walk in the light of your presence, LORD.
Masu albarka ne waɗanda suka koyi yin maka kirari waɗanda suke tafiya cikin hasken da yake gabanka, Ubangiji.
16 In your name they rejoice all day. In your righteousness, they are exalted.
Suna farin ciki a cikin sunanka dukan yini; suna samun ɗaukaka cikin adalcinka.
17 For you are the glory of their strength. In your favor, our horn will be exalted.
Gama kai ne ɗaukakarsu da ƙarfinsu, kuma ta wurin alherinka ka ɗaukaka ƙahonka.
18 For our shield belongs to the LORD, our king to the Holy One of Israel.
Tabbatacce, garkuwarmu ta Ubangiji ce, ta sarkinmu ce, da kuma ta Mai Tsarki na Isra’ila ce.
19 Then you spoke in vision to your holy ones, and said, “I have given strength to the warrior. I have exalted a young man from the people.
Ka taɓa yin magana cikin wahayi, ga mutanenka masu aminci ka ce, “Na ba wa jarumi ƙarfi; na ɗaukaka saurayi daga cikin mutane.
20 I have found David, my servant. I have anointed him with my holy oil,
Na sami Dawuda bawana; da mai na mai tsarki na shafe shi.
21 with whom my hand shall be established. My arm will also strengthen him.
Hannuna zai kasance tare da shi; tabbatacce hannuna zai ƙarfafa shi.
22 No enemy will tax him. No wicked man will oppress him.
Babu abokin gāban da zai sa yă biya haraji; babu mugun mutumin da zai danne shi.
23 I will beat down his adversaries before him, and strike those who hate him.
Zan murƙushe maƙiyansa a gabansa in kashe dukan abokan gābansa.
24 But my faithfulness and my loving kindness will be with him. In my name, his horn will be exalted.
Amintacciya ƙaunata za tă kasance tare da shi, kuma ta wurin sunana za a ɗaukaka ƙahonsa.
25 I will set his hand also on the sea, and his right hand on the rivers.
Zan sa hannunsa a bisa teku, hannunsa na dama a bisa koguna.
26 He will call to me, ‘You are my Father, my God, and the rock of my salvation!’
Zai yi kira gare ni yă ce, ‘Kai ne Mahaifina, Allahna, Dutse mai cetona.’
27 I will also appoint him my firstborn, the highest of the kings of the earth.
Zan kuma naɗa shi ɗan farina, mafi ɗaukaka cikin sarakunan duniya.
28 I will keep my loving kindness for him forever more. My covenant will stand firm with him.
Zan ci gaba da ƙaunarsa har abada, alkawarina da shi ba zai taɓa fasa ba.
29 I will also make his offspring endure forever, and his throne as the days of heaven.
Zan kafa zuriyarsa har abada, kursiyinsa muddin sammai suna nan.
30 If his children forsake my Torah, and don’t walk in my ordinances;
“In’ya’yansa maza suka yashe dokata ba su kuwa bi ƙa’idodina ba,
31 if they break my statutes, and don’t keep my commandments;
in suka take ƙa’idodina suka kuma kāsa kiyaye umarnaina,
32 then I will punish their sin with the rod, and their iniquity with stripes.
zan hukunta zunubinsu da sanda, laifinsu da bulala;
33 But I will not completely take my loving kindness from him, nor allow my faithfulness to fail.
amma ba zan ɗauke ƙaunata daga gare shi ba, ba kuwa zan taɓa rasa cika amincina ba.
34 I will not break my covenant, nor alter what my lips have uttered.
Ba zan take alkawarina ba ko in canja abin da leɓunana suka ambata.
35 Once I have sworn by my holiness, I will not lie to David.
Sau ɗaya ba ƙari, na rantse da tsarkina, ba kuwa zan yi ƙarya wa Dawuda ba,
36 His offspring will endure forever, his throne like the sun before me.
cewa zuriyarsa za tă ci gaba har abada kuma kursiyinsa zai dawwama a gabana kamar rana;
37 It will be established forever like the moon, the faithful witness in the sky.” (Selah)
zai kahu har abada kamar wata, amintacciyar shaida a cikin sarari.” (Sela)
38 But you have rejected and spurned. You have been angry with your anointed.
Amma ka ƙi, ka yi ƙyama ka kuma yi fushi sosai da shafaffenka.
39 You have renounced the covenant of your servant. You have defiled his crown in the dust.
Ka soke alkawarin da ka yi da bawanka ka kuma ƙazantar da rawaninsa a ƙura.
40 You have broken down all his hedges. You have brought his strongholds to ruin.
Ka rurrushe dukan katangansa ka sa kagaransa suka zama kufai.
41 All who pass by the way rob him. He has become a reproach to his neighbors.
Dukan waɗanda suka wuce sun washe shi; ya zama abin dariya wajen maƙwabtansa.
42 You have exalted the right hand of his adversaries. You have made all of his enemies rejoice.
Ka ɗaukaka hannun dama na maƙiyansa; ka sa dukan abokan gābansa suna farin ciki.
43 Yes, you turn back the edge of his sword, and haven’t supported him in battle.
Ka juye bakin takobinsa ba ka kuma taimake shi a cikin yaƙi ba.
44 You have ended his splendor, and thrown his throne down to the ground.
Ka kawo ƙarshen darajarsa ka kuma jefar da kursiyinsa ƙasa.
45 You have shortened the days of his youth. You have covered him with shame. (Selah)
Ka rage kwanakin ƙuruciyarsa; ka rufe shi da mayafin kunya. (Sela)
46 How long, LORD? Will you hide yourself forever? Will your wrath burn like fire?
Har yaushe, ya Ubangiji za ka ɓoye? Za ka ɓoye har abada ne? Har yaushe fushinka zai yi ta ci kamar wuta?
47 Remember how short my time is, for what vanity you have created all the children of men!
Ka tuna yadda raina mai wucewa ne. Gama ka halicce dukan mutane ba amfani!
48 What man is he who shall live and not see death, who shall deliver his soul from the power of Sheol? (Selah) (Sheol h7585)
Wanda mutum ne zai rayu da ba zai ga mutuwa ba, ko yă cece kansa daga ikon kabari? (Sela) (Sheol h7585)
49 Lord, where are your former loving kindnesses, which you swore to David in your faithfulness?
Ya Ubangiji, ina ƙaunar mai girma ta dā, wadda cikin amincinka ka rantse wa Dawuda?
50 Remember, Lord, the reproach of your servants, how I bear in my heart the taunts of all the mighty peoples,
Ka tuna, Ubangiji, yadda aka yi wa bawanka ba’a, yadda na jimre a zuciyata da zage-zagen dukan al’ummai,
51 With which your enemies have mocked, LORD, with which they have mocked the footsteps of your anointed one.
zage-zagen da abokan gābanka suka yi mini, ya Ubangiji, da suka yi wa kowane matakin da shafaffenka ya ɗauka.
52 Blessed be the LORD forever more. Amen, and Amen.
Yabo ya tabbata ga Ubangiji har abada!

< Psalms 89 >