< Psalms 51 >

1 For the Chief Musician. A Psalm by David, when Nathan the prophet came to him, after he had gone in to Bathsheba. Have mercy on me, God, according to your loving kindness. According to the multitude of your tender mercies, blot out my transgressions.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Zabura ta Dawuda. Sa’ad da annabi Natan ya zo wurinsa bayan Dawuda ya yi zina da Batsheba. Ka yi mini jinƙai, ya Allah, bisa ga ƙaunarka marar ƙarewa; bisa ga tausayinka mai girma ka shafe laifofina.
2 Wash me thoroughly from my iniquity. Cleanse me from my sin.
Ka wanke dukan kurakuraina ka tsarkake ni daga zunubina.
3 For I know my transgressions. My sin is constantly before me.
Gama ina sane da laifofina zunubaina kuma kullum suna a gabana.
4 Against you, and you only, I have sinned, and done that which is evil in your sight, so you may be proved right when you speak, and justified when you judge.
Kai kaɗai na yi wa zunubi na yi abin da yake mugu a idonka, ta haka an tabbatar kai mai gaskiya sa’ad da ka yi magana aka kuma nuna kai mai adalci ne sa’ad da ka hukunta.
5 Behold, I was born in iniquity. My mother conceived me in sin.
Tabbatacce ni mai zunubi ne tun haihuwa mai zunubi daga lokacin da mahaifiyata ta yi cikina.
6 Behold, you desire truth in the inward parts. You teach me wisdom in the inmost place.
Tabbatacce kana son gaskiya a sassan ciki; ka koya mini hikima a wuri can ciki.
7 Purify me with hyssop, and I will be clean. Wash me, and I will be whiter than snow.
Ka tsarkake ni da hizzob, zan kuwa zama tsab; ka wanke ni, zan kuma fi dusan ƙanƙara fari.
8 Let me hear joy and gladness, that the bones which you have broken may rejoice.
Bari in ji farin ciki da murna; bari ƙasusuwan da ka ragargaza su yi farin ciki.
9 Hide your face from my sins, and blot out all of my iniquities.
Ka ɓoye fuskarka daga zunubaina ka kuma shafe dukan kurakuraina.
10 Create in me a clean heart, O God. Renew a right spirit within me.
Ka halitta zuciya mai tsabta a cikina, ya Allah, ka kuma sabunta tsayayyen ruhu a cikina.
11 Don’t throw me from your presence, and don’t take your Holy Spirit from me.
Kada ka fid da ni daga gabanka ko ka ɗauke Ruhunka Mai Tsarki daga gare ni.
12 Restore to me the joy of your salvation. Uphold me with a willing spirit.
Ka mayar mini farin cikin cetonka ka kuma ba ni ruhun biyayya, yă riƙe ni.
13 Then I will teach transgressors your ways. Sinners will be converted to you.
Ta haka zan koyar wa masu laifi hanyoyinka, masu zunubi kuma za su komo gare ka.
14 Deliver me from the guilt of bloodshed, O God, the God of my salvation. My tongue will sing aloud of your righteousness.
Ka cece ni daga laifin jini, ya Allah, Allahn da ya cece ni, harshena kuwa zai rera adalcinka.
15 Lord, open my lips. My mouth will declare your praise.
Ya Ubangiji, ka buɗe leɓunana, bakina kuwa zai furta yabonka.
16 For you don’t delight in sacrifice, or else I would give it. You have no pleasure in burnt offering.
Ba ka farin ciki a hadaya, ai da na kawo; ba ka jin daɗin hadayun ƙonawa.
17 The sacrifices of God are a broken spirit. O God, you will not despise a broken and contrite heart.
Hadayun Allah su ne karyayyen ruhu; karyayyiya da kuma zuciya mai tuba, Ya Allah, ba za ka ƙi ba.
18 Do well in your good pleasure to Zion. Build the walls of Jerusalem.
Cikin jin daɗinka ka sa Sihiyona ta yi nasara; ka gina katangar Urushalima.
19 Then you will delight in the sacrifices of righteousness, in burnt offerings and in whole burnt offerings. Then they will offer bulls on your altar.
Ta haka za a kasance da hadayu masu adalci, hadayun ƙonawa ɗungum don su faranta ka; sa’an nan za a miƙa bijimai a bagadenka.

< Psalms 51 >