< Psalms 50 >

1 A Psalm by Asaph. The Mighty One, God, the LORD, speaks, and calls the earth from sunrise to sunset.
Zabura ta Asaf. Maɗaukaki, Allah, Ubangiji, ya yi magana ya kuma kira duniya daga fitowar rana zuwa inda take fāɗuwa.
2 Out of Zion, the perfection of beauty, God shines out.
Daga Sihiyona, cikakkiya a kyau, Allah na haskakawa.
3 Our God comes, and does not keep silent. A fire devours before him. It is very stormy around him.
Allahnmu yana zuwa ba kuwa zai yi shiru ba; wuta mai cinyewa a gabansa, babban hadari kuma ya kewaye shi.
4 He calls to the heavens above, to the earth, that he may judge his people:
Ya kira sammai da suke bisa, da duniya, don yă shari’anta mutanensa.
5 “Gather my holy ones together to me, those who have made a covenant with me by sacrifice.”
“Ku tattara mini shafaffuna, waɗanda suka yi alkawari da ni ta wurin hadaya.”
6 The heavens shall declare his righteousness, for God himself is judge. (Selah)
Sammai kuwa sun yi shelar adalcinsa gama Allah kansa alƙali ne. (Sela)
7 “Hear, my people, and I will speak. Israel, I will testify against you. I am God, your God.
“Ku ji, ya mutanena, zan kuwa yi magana, Ya Isra’ila, zan kuwa ba da shaida a kanku. Ni ne Allah, Allahnku.
8 I don’t rebuke you for your sacrifices. Your burnt offerings are continually before me.
Ba na tsawata muku saboda hadayunku ko kuwa hadayunku na ƙonawa, waɗanda kuka taɓa kawo a gabana.
9 I have no need for a bull from your stall, nor male goats from your pens.
Ba na bukatan bijimi daga turkenku ko awaki daga garkunanku,
10 For every animal of the forest is mine, and the livestock on a thousand hills.
gama kowace dabbar kurmi nawa ne, da kuma shanu a kan dubban tuddai.
11 I know all the birds of the mountains. The wild animals of the field are mine.
Na san kowane tsuntsun da yake a duwatsu kuma halittun filaye nawa ne.
12 If I were hungry, I would not tell you, for the world is mine, and all that is in it.
Da a ce ina jin yunwa ai, ba sai na faɗa muku ba, gama duniyar nawa ne, da kome da yake cikinta.
13 Will I eat the meat of bulls, or drink the blood of goats?
Ina cin naman bijimai ne ko ina shan jinin awaki ne?
14 Offer to God the sacrifice of thanksgiving. Pay your vows to the Most High.
“Ku miƙa hadayar godiya ga Allah, ku cika alkawuranku ga Mafi Ɗaukaka,
15 Call on me in the day of trouble. I will deliver you, and you will honor me.”
ku kira gare ni a ranar wahala; zan cece ku, za ku kuwa girmama ni.”
16 But to the wicked God says, “What right do you have to declare my statutes, that you have taken my covenant on your lips,
Amma ga mugaye, Allah ya ce, “Wace dama ce kuke da ita na haddace dokokina ko na yin maganar alkawarina a leɓunanku?
17 since you hate instruction, and throw my words behind you?
Kun ƙi umarnina kuka kuma zubar da kalmomina a bayanku
18 When you saw a thief, you consented with him, and have participated with adulterers.
Sa’ad da kuka ga ɓarawo, kukan haɗa kai da shi; kukan haɗa kai da mazinata.
19 “You give your mouth to evil. Your tongue frames deceit.
Kuna amfani da bakunanku don mugunta kuna kuma gyara harshenku don ruɗu.
20 You sit and speak against your brother. You slander your own mother’s son.
Kuna ci gaba da magana a kan ɗan’uwanku ku kuma yi maganar ƙarya a kan ɗan mahaifinku.
21 You have done these things, and I kept silent. You thought that I was just like you. I will rebuke you, and accuse you in front of your eyes.
Kun yi waɗannan abubuwa na kuwa yi shiru; kun ɗauka gaba ɗaya ni kamar ku ne. Amma zan tsawata muku in kuma zarge ku a fuskarku.
22 “Now consider this, you who forget God, lest I tear you into pieces, and there be no one to deliver.
“Ku lura da wannan, ku da kuka manta da Allah, ko kuwa in yayyage ku kucu-kucu, ba kuma wanda zai cece ku.
23 Whoever offers the sacrifice of thanksgiving glorifies me, and prepares his way so that I will show God’s salvation to him.”
Shi wanda ya miƙa hadayun godiya yakan girmama ni, ya kuma shirya hanya saboda in nuna masa ceton Allah.”

< Psalms 50 >