< Psalms 46 >

1 For the Chief Musician. By the sons of Korah. According to Alamoth. God is our refuge and strength, a very present help in trouble.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta’Ya’yan Kora maza. Bisa ga alamot Waƙa ce. Allah ne mafakarmu da ƙarfinmu, kullum yana a shirye yă taimaka a lokacin wahala.
2 Therefore we won’t be afraid, though the earth changes, though the mountains are shaken into the heart of the seas;
Saboda haka ba za mu ji tsoro ba, ko da ƙasa ta girgiza duwatsu kuma suka fāɗi cikin zurfin teku,
3 though its waters roar and are troubled, though the mountains tremble with their swelling. (Selah)
ko da ruwansa suna ruri suna kumfa duwatsu kuma suna girgiza da tumbatsansu. (Sela)
4 There is a river, the streams of which make the city of God glad, the holy place of the tents of the Most High.
Akwai kogi mai rafuffukan da suke sa birnin Allah murna, tsattsarkan wuri inda Mafi Ɗaukaka ke zama.
5 God is within her. She shall not be moved. God will help her at dawn.
Allah yana cikinta, ba za tă fāɗi ba; Allah zai taimake ta da safe.
6 The nations raged. The kingdoms were moved. He lifted his voice and the earth melted.
Al’ummai suna hayaniya, mulkoki sun fāɗi; ya ɗaga muryarsa, duniya ta narke.
7 The LORD of Hosts is with us. The God of Jacob is our refuge. (Selah)
Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)
8 Come, see the LORD’s works, what desolations he has made in the earth.
Zo ku ga ayyukan Ubangiji, kangon da ya kawo a kan duniya.
9 He makes wars cease to the end of the earth. He breaks the bow, and shatters the spear. He burns the chariots in the fire.
Ya sa yaƙoƙi suka yi tsit ko’ina a duniya. Ya kakkarya bakkuna ya kuma ragargaza māsu, ya ƙone garkuwoyi da wuta.
10 “Be still, and know that I am God. I will be exalted among the nations. I will be exalted in the earth.”
“Ku natsu ku kuma san cewa ni ne Allah; za a ɗaukaka ni a cikin al’ummai, za a ɗaukaka ni cikin duniya.”
11 The LORD of Hosts is with us. The God of Jacob is our refuge. (Selah)
Ubangiji Maɗaukaki yana tare da mu; Allah na Yaƙub ne kagararmu. (Sela)

< Psalms 46 >