< Psalms 38 >

1 A Psalm by David, for a memorial. LORD, don’t rebuke me in your wrath, neither chasten me in your hot displeasure.
Zabura ta Dawuda. Roƙo ne. Ya Ubangiji, kada ka tsawata mini cikin fushinka ko ka hore ni cikin hasalarka.
2 For your arrows have pierced me, your hand presses hard on me.
Gama kibiyoyinka sun soke ni, hannunka kuma ya fāɗo a kaina.
3 There is no soundness in my flesh because of your indignation, neither is there any health in my bones because of my sin.
Saboda hasalarka babu lafiya a jikina; ƙasusuwana ba lafiya saboda zunubina.
4 For my iniquities have gone over my head. As a heavy burden, they are too heavy for me.
Laifofina sun mamaye ni kamar nauyin da ya sha ƙarfin ɗauka.
5 My wounds are loathsome and corrupt because of my foolishness.
Miyakuna sun ruɓe suna kuma wari saboda wawancina na zunubi.
6 I am in pain and bowed down greatly. I go mourning all day long.
An tanƙware ni aka kuma ƙasƙantar da ni; dukan yini ina ta kuka.
7 For my waist is filled with burning. There is no soundness in my flesh.
Bayana yana fama da zazzaɓi; babu lafiya a jikina.
8 I am faint and severely bruised. I have groaned by reason of the anguish of my heart.
Na gaji sharkaf an kuma ragargaza ni; ina nishi da wahala a cikin zuciyata.
9 Lord, all my desire is before you. My groaning is not hidden from you.
Dukan bukatata tana a shimfiɗe a gabanka, ya Ubangiji; ajiyar zuciyata ba ta ɓoyuwa daga gare ka.
10 My heart throbs. My strength fails me. As for the light of my eyes, it has also left me.
Zuciyata na bugu, ƙarfina kuma ya ƙare, har ma haske ya rabu da idanuna.
11 My lovers and my friends stand aloof from my plague. My kinsmen stand far away.
Abokaina da maƙwabtana sun guje ni saboda miyakuna; maƙwabtana ba sa zuwa kusa.
12 They also who seek after my life lay snares. Those who seek my hurt speak mischievous things, and meditate deceits all day long.
Waɗanda suke neman raina sun sa tarkonsu, waɗanda suke so su cuce ni suna zance lalatar da ni; yini sukutum suna ƙulla mini maƙarƙashiya.
13 But I, as a deaf man, don’t hear. I am as a mute man who doesn’t open his mouth.
Ni kamar kurma ne, wanda ba ya ji, kamar bebe, wanda ba ya iya buɗe bakinsa.
14 Yes, I am as a man who doesn’t hear, in whose mouth are no reproofs.
Na zama kamar mutumin da ba ya ji, wanda bakinsa ba ya iya ba da amsa.
15 For I hope in you, LORD. You will answer, Lord my God.
Na dogara gare ka, ya Ubangiji; za ka amsa, ya Ubangiji Allahna.
16 For I said, “Don’t let them gloat over me, or exalt themselves over me when my foot slips.”
Gama na ce, “Kada ka bar su su yi farin ciki a kaina ko su yi kirari a kaina sa’ad da ƙafata ta yi santsi.”
17 For I am ready to fall. My pain is continually before me.
Gama ina gab da fāɗuwa, kuma cikin azaba nake kullum.
18 For I will declare my iniquity. I will be sorry for my sin.
Na furta laifina; na damu da zunubina.
19 But my enemies are vigorous and many. Those who hate me without reason are numerous.
Da yawa ne masu gāba da ni da ƙarfi; waɗanda suke kina ba dalili sun yi yawa.
20 They who render evil for good are also adversaries to me, because I follow what is good.
Waɗanda suke sāka alherina da mugunta, suna cin zarafina sa’ad da nake bin abin da yake daidai.
21 Don’t forsake me, LORD. My God, don’t be far from me.
Ya Ubangiji, kada ka yashe ni; kada ka yi nesa da ni, ya Allahna.
22 Hurry to help me, Lord, my salvation.
Zo da sauri ka taimake ni, Ya Ubangiji Mai Cetona.

< Psalms 38 >