< Psalms 29 >

1 A Psalm by David. Ascribe to the LORD, you sons of the mighty, ascribe to the LORD glory and strength.
Zabura ta Dawuda. Ku ba da girma ga Ubangiji, ya ku manya, ku ba da girma ga Ubangiji saboda ɗaukaka da kuma ƙarfinsa.
2 Ascribe to the LORD the glory due to his name. Worship the LORD in holy array.
Ku ba da girma ga Ubangiji, ɗaukakar da ta dace da sunansa; ku bauta wa Ubangiji cikin ɗaukakar tsarkinsa.
3 The LORD’s voice is on the waters. The God of glory thunders, even the LORD on many waters.
Muryar Ubangiji tana a bisa ruwaye; Allah Maɗaukaki ya yi tsawa, Ubangiji ya yi tsawa a bisa manyan ruwaye.
4 The LORD’s voice is powerful. The LORD’s voice is full of majesty.
Muryar Ubangiji mai iko ce; muryar Ubangiji da girma take.
5 The LORD’s voice breaks the cedars. Yes, the LORD breaks in pieces the cedars of Lebanon.
Muryar Ubangiji ta kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon. Ubangiji ya kakkarya itatuwan al’ul na Lebanon kucu-kucu.
6 He makes them also to skip like a calf; Lebanon and Sirion like a young, wild ox.
Ya sa dutsen Lebanon ya yi ta tsalle kamar ɗan maraƙi, Siriyon kuma kamar ɗan jakin jeji.
7 The LORD’s voice strikes with flashes of lightning.
Muryar Ubangiji ta buga da walƙatar walƙiya.
8 The LORD’s voice shakes the wilderness. The LORD shakes the wilderness of Kadesh.
Muryar Ubangiji ta girgiza hamada Ubangiji ya girgiza Hamadan Kadesh.
9 The LORD’s voice makes the deer calve, and strips the forests bare. In his temple everything says, “Glory!”
Muryar Ubangiji ta murɗa itatuwan oak ya kakkaɓe itatuwan kurmi. Kuma a cikin haikalinsa kowa ya ce, “Ɗaukaka!”
10 The LORD sat enthroned at the Flood. Yes, the LORD sits as King forever.
Ubangiji na zaune yana sarauta a bisa rigyawa; Ubangiji yana sarauta kamar Sarki har abada.
11 The LORD will give strength to his people. The LORD will bless his people with peace.
Ubangiji kan ba da ƙarfi ga mutanensa; Ubangiji kan albarkace mutanensa da salama.

< Psalms 29 >