< Psalms 146 >

1 Praise the LORD! Praise the LORD, my soul.
Yabi Ubangiji. Yabi Ubangiji, ya raina.
2 While I live, I will praise the LORD. I will sing praises to my God as long as I exist.
Zan yabi Ubangiji dukan kwanakina; zan rera yabo ga Allahna muddin raina.
3 Don’t put your trust in princes, in a son of man in whom there is no help.
Kada ka sa zuciyarka ga sarakuna, ga mutane masu mutuwa, waɗanda ba sa iya ceto.
4 His spirit departs, and he returns to the earth. In that very day, his thoughts perish.
Sa’ad da numfashinsu ya rabu da su sai su koma ƙasa; a wannan rana shirye-shiryensu sun zama banza.
5 Happy is he who has the God of Jacob for his help, whose hope is in the LORD, his God,
Mai albarka ne wanda Allah na Yaƙub ne taimakonsa, wanda sa zuciyarsa yana a kan Ubangiji Allahnsa.
6 who made heaven and earth, the sea, and all that is in them; who keeps truth forever;
Mahaliccin sama da ƙasa, teku, da kome da yake cikinsu, Ubangiji, wanda yake mai aminci har abada.
7 who executes justice for the oppressed; who gives food to the hungry. The LORD frees the prisoners.
Yakan biya bukatun mutanen da aka danne ya kuma ba da abinci ga mayunwata. Ubangiji yakan’yantar da’yan kurkuku,
8 The LORD opens the eyes of the blind. The LORD raises up those who are bowed down. The LORD loves the righteous.
Ubangiji yakan ba wa makafi ido, Ubangiji yakan ɗaga waɗanda aka rusunar da su ƙasa, Ubangiji yana ƙaunar masu adalci.
9 The LORD preserves the foreigners. He upholds the fatherless and widow, but he turns the way of the wicked upside down.
Ubangiji yana tsaron baƙi yana kuma lura da marayu da kuma gwauruwa, amma yakan lalatar da hanyoyin mugaye.
10 The LORD will reign forever; your God, O Zion, to all generations. Praise the LORD!
Ubangiji yana mulki har abada, Allahnki, ya Sihiyona, daga zamani zuwa zamani. Yabi Ubangiji.

< Psalms 146 >