< Psalms 114 >

1 When Israel went out of Egypt, the house of Jacob from a people of foreign language,
Sa’ad da Isra’ila ya fito daga Masar, gidan Yaƙub daga mutane masu baƙon harshe,
2 Judah became his sanctuary, Israel his dominion.
Yahuda ya zama wuri mai tsarki na Allah, Isra’ila mallakarsa.
3 The sea saw it, and fled. The Jordan was driven back.
Teku ya kalla ya kuma gudu, Urdun ya juye da baya;
4 The mountains skipped like rams, the little hills like lambs.
duwatsu suka yi tsalle kamar raguna, tuddai kamar tumaki.
5 What was it, you sea, that you fled? You Jordan, that you turned back?
Me ya sa, ya teku, kika gudu, Ya Urdun, ka juya baya,
6 You mountains, that you skipped like rams? You little hills, like lambs?
ku duwatsu, kuka yi tsalle kamar raguna, ku tuddai, kamar tumaki?
7 Tremble, you earth, at the presence of the Lord, at the presence of the God of Jacob,
Ki yi rawar jiki, ya duniya, a gaban Ubangiji, a gaban Allah na Yaƙub,
8 who turned the rock into a pool of water, the flint into a spring of waters.
wanda ya juye dutse ya zama tafki, dutse mai ƙarfi zuwa maɓulɓulan ruwa.

< Psalms 114 >