< Proverbs 22 >

1 A good name is more desirable than great riches, and loving favor is better than silver and gold.
An fi son suna mai kyau fiye da wadata mai yawa; tagomashi kuma ya fi azurfa ko zinariya.
2 The rich and the poor have this in common: The LORD is the maker of them all.
Mawadaci da matalauci suna da abu guda. Ubangiji ne Mahaliccinsu duka.
3 A prudent man sees danger and hides himself; but the simple pass on, and suffer for it.
Mai basira kan ga damuwa tana zuwa yă nemi mafaka, amma marar azanci kan yi ta tafiya yă kuma sha wahala.
4 The result of humility and the fear of the LORD is wealth, honor, and life.
Sauƙinkai da tsoron Ubangiji sukan kawo wadata da girmamawa da kuma rai.
5 Thorns and snares are in the path of the wicked; whoever guards his soul stays far from them.
A hanyoyin mugu akwai kaya da tarko, amma duk wanda ya kiyaye ransa kan kauce musu.
6 Train up a child in the way he should go, and when he is old he will not depart from it.
Ka hori yaro a hanyar da ya kamata yă bi, kuma sa’ad da ya tsufa ba zai bar ta ba.
7 The rich rule over the poor. The borrower is servant to the lender.
Mawadaci yakan yi mulki a kan matalauci, mai cin bashi kuwa bawan mai ba da bashi ne.
8 He who sows wickedness reaps trouble, and the rod of his fury will be destroyed.
Duk wanda ya shuka mugunta yakan girbe wahala, za a kuma hallaka sandar fushinsa.
9 He who has a generous eye will be blessed, for he shares his food with the poor.
Mai bayarwa hannu sake shi kansa zai sami albarka, gama yakan raba abincinsa da matalauta.
10 Drive out the mocker, and strife will go out; yes, quarrels and insults will stop.
Ka hori mai ba’a, hatsaniya kuwa za tă yi waje; fitina da zargi kuma za su ƙare.
11 He who loves purity of heart and speaks gracefully is the king’s friend.
Duk mai son tsabtar zuciya wanda kuma jawabinsa mai alheri ne zai zama aminin sarki.
12 The LORD’s eyes watch over knowledge, but he frustrates the words of the unfaithful.
Idanun Ubangiji na lura da sani, amma yakan ƙi kalmomin marar aminci.
13 The sluggard says, “There is a lion outside! I will be killed in the streets!”
Rago kan ce, “Akwai zaki a waje!” Ko kuma “Za a kashe ni a tituna!”
14 The mouth of an adulteress is a deep pit. He who is under the LORD’s wrath will fall into it.
Bakin mazinaciya rami ne mai zurfi; duk wanda yake a ƙarƙashin fushin Ubangiji zai fāɗa a ciki.
15 Folly is bound up in the heart of a child; the rod of discipline drives it far from him.
Wauta tana da yawa a zuciyar yara, amma sandar horo zai kore ta nesa da su.
16 Whoever oppresses the poor for his own increase and whoever gives to the rich, both come to poverty.
Duk wanda yake danne matalauta don yă azurta kuma duk wanda yake kyauta ga mawadata, dukansu kan talauta.
17 Turn your ear, and listen to the words of the wise. Apply your heart to my teaching.
Ka kasa kunne ka kuma saurara ga maganganu masu hikima; ka yi amfani da abin da nake koyarwa,
18 For it is a pleasant thing if you keep them within you, if all of them are ready on your lips.
gama yana da daɗi sa’ad da ka kiyaye su a zuciyarka ka kuma kasance da su a shirye a leɓunanka.
19 I teach you today, even you, so that your trust may be in the LORD.
Domin dogarawarka ta kasance ga Ubangiji, ina koya maka yau, har kai ma.
20 Haven’t I written to you thirty excellent things of counsel and knowledge,
Ban rubuta maka maganganu talatin ba, maganganun shawara da sani,
21 To teach you truth, reliable words, to give sound answers to the ones who sent you?
ina koya maka gaskiya da kalmomin da za ka dogara a kai, saboda ka iya ba da amsa daidai ga duk wanda ya aike ka?
22 Don’t exploit the poor because he is poor; and don’t crush the needy in court;
Kada ka zalunci matalauta a kan suna matalauta kada kuma ka ƙwari wanda ba shi da mai taimako a gaban shari’a,
23 for the LORD will plead their case, and plunder the life of those who plunder them.
gama Ubangiji zai yi magana dominsu zai kuwa washe waɗanda suka washe su.
24 Don’t befriend a hot-tempered man. Don’t associate with one who harbors anger,
Kada ka yi abokantaka da mai zafin rai, kada ka haɗa kai da wanda ba shi da wuya ya yi fushi,
25 lest you learn his ways and ensnare your soul.
in ba haka ba za ka koyi hanyoyinsa ka kuma sa kanka a tarko.
26 Don’t you be one of those who strike hands, of those who are collateral for debts.
Kada ka zama mai ɗaukar lamuni ko ka ba da jingina saboda bashi;
27 If you don’t have means to pay, why should he take away your bed from under you?
gama in ka kāsa biya za a ƙwace gadon da kake kwanciya a kai ma.
28 Don’t move the ancient boundary stone which your fathers have set up.
Kada ka matsar da shaidar kan iyakar da kakanninka suka kafa.
29 Do you see a man skilled in his work? He will serve kings. He won’t serve obscure men.
Kana ganin mutumin da yake da gwaninta a cikin aikinsa? Zai yi wa sarakuna hidima; ba zai yi hidima wa mutanen da ba su iya ba.

< Proverbs 22 >