< Numbers 31 >

1 The LORD spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “Avenge the children of Israel on the Midianites. Afterward you shall be gathered to your people.”
“Ka ɗaukar wa Isra’ilawa fansa, a kan Midiyawa. Bayan wannan za ka mutu, a kuwa tara ka ga mutanenka.”
3 Moses spoke to the people, saying, “Arm men from among you for war, that they may go against Midian, to execute the LORD’s vengeance on Midian.
Saboda haka Musa ya ce wa mutane, “Ku shirya waɗansu daga cikin mazanku, su tafi su yi yaƙi da Midiyawa don su ɗaukar wa Ubangiji fansa a kansu.”
4 You shall send one thousand out of every tribe, throughout all the tribes of Israel, to the war.”
Ku aiki maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
5 So there were delivered, out of the thousands of Israel, a thousand from every tribe, twelve thousand armed for war.
Saboda haka aka samo mayaƙa dubu goma sha biyu shiryayyu don yaƙi, maza dubu ɗaya daga kowace kabilar Isra’ila.
6 Moses sent them, one thousand of every tribe, to the war with Phinehas the son of Eleazar the priest, to the war, with the vessels of the sanctuary and the shofars for the alarm in his hand.
Musa ya aike su zuwa yaƙi, dubu ɗaya daga kowace kabila, tare da Finehas ɗan Eleyazar, firist, wanda ya ɗauki kayayyaki daga wuri mai tsarki da ƙahoni don kiran yaƙi.
7 They fought against Midian, as the LORD commanded Moses. They killed every male.
Suka yi yaƙi da Midiyawa, suka kashe kowane mutum yadda Ubangiji ya umarci Musa.
8 They killed the kings of Midian with the rest of their slain: Evi, Rekem, Zur, Hur, and Reba, the five kings of Midian. They also killed Balaam the son of Beor with the sword.
A cikin waɗanda aka kashe kuwa akwai Ewi, Rekem, Zur, Hur da Reba; sarakuna biyar na Mediyawa. Suka kuma kashe Bala’am ɗan Beyor da takobi.
9 The children of Israel took the women of Midian captive with their little ones; and all their livestock, all their flocks, and all their goods, they took as plunder.
Isra’ilawa suka kwashe mata da yaran Midiyawa, a matsayin bayi. Suka kwashe shanunsu da tumakinsu da kuma dukan dukiyarsu, a matsayin ganima.
10 All their cities in the places in which they lived, and all their encampments, they burned with fire.
Suka ƙone dukan garuruwan da Midiyawa suke zama, da dukan sansaninsu.
11 They took all the captives, and all the plunder, both of man and of animal.
Suka kwashe dukan ganima haɗe da mutane da dabbobi,
12 They brought the captives with the prey and the plunder, to Moses, and to Eleazar the priest, and to the congregation of the children of Israel, to the camp at the plains of Moab, which are by the Jordan at Jericho.
suka kawo bayi da ganiman nan, wurin Musa da Eleyazar firist, da kuma jama’ar Isra’ilawa, a sansaninsu a filayen Mowab kusa da Urdun daga ƙetaren Yeriko.
13 Moses and Eleazar the priest, with all the princes of the congregation, went out to meet them outside of the camp.
Musa, da Eleyazar firist da dukan shugabannin jama’a, suka fito suka tarye su a bayan sansani.
14 Moses was angry with the officers of the army, the captains of thousands and the captains of hundreds, who came from the service of the war.
Musa kuwa ya husata da shugabannin sojojin da suke shugabannin dubbai da shugabannin ɗari-ɗarin da suka dawo daga yaƙi.
15 Moses said to them, “Have you saved all the women alive?
Ya tambaye su ya ce, “Kun bar dukan mata da rai?
16 Behold, these caused the children of Israel, through the counsel of Balaam, to commit trespass against the LORD in the matter of Peor, and so the plague was among the congregation of the LORD.
Su ne waɗanda suka bi shawarar Bala’am suka kuma zama sanadin sa Isra’ilawa suka juya wa Ubangiji baya, har ya kawo abin da ya faru da Feyor, har annoba ya kashe dukan mutanen Ubangiji.
17 Now therefore kill every male among the little ones, and kill every woman who has known man by lying with him.
Yanzu ku kashe dukan yara maza, ku kuma kashe kowace macen da ta yi lalata da namiji,
18 But all the girls, who have not known man by lying with him, keep alive for yourselves.
amma ku bar kowace yarinyar da ba tă taɓa yin lalata da namiji ba.
19 “Encamp outside of the camp for seven days. Whoever has killed any person, and whoever has touched any slain, purify yourselves on the third day and on the seventh day, you and your captives.
“Dukanku da kuka kashe mutum, ko kuka taɓa wani da aka kashe, dole ku kasance a bayan sansani har kwana bakwai. A rana ta uku da rana ta bakwai dole ku tsabtacce kanku da kuma bayinku.
20 You shall purify every garment, and all that is made of skin, and all work of goats’ hair, and all things made of wood.”
Ku tsarkake kowace taguwa da kuma kome da aka yi da fata, da gashin akuya, ko kuwa itace.”
21 Eleazar the priest said to the men of war who went to the battle, “This is the statute of the law which the LORD has commanded Moses.
Sa’an nan Eleyazar firist, ya ce wa sojojin da suka je yaƙi, “Wannan ita ce ƙa’idar da Ubangiji ya ba wa Musa.
22 However the gold, and the silver, the bronze, the iron, the tin, and the lead,
Zinariya, azurfa, tagulla, baƙin ƙarfe, kuza, darma
23 everything that may withstand the fire, you shall make to go through the fire, and it shall be clean; nevertheless it shall be purified with the water for impurity. All that doesn’t withstand the fire you shall make to go through the water.
da dukan abin da wuta ba ta iya ci, dole yă shiga wuta sa’an nan zai zama da tsabta. Amma dole a kuma tsarkake ta da ruwan tsarkakewa. Duk abin da wuta za tă iya ci, dole a shigar da ita a ruwan tsarkakewa.
24 You shall wash your clothes on the seventh day, and you shall be clean. Afterward you shall come into the camp.”
A rana ta bakwai za ku wanke tufafinku, sa’an nan za ku tsarkaka, bayan haka ku shigo sansani.”
25 The LORD spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya yi magana da Musa ya ce,
26 “Count the plunder that was taken, both of man and of animal, you, and Eleazar the priest, and the heads of the fathers’ households of the congregation;
“Da kai da Eleyazar firist, da shugabannin jama’a, ku ƙidaya dukan mutane da dabbobin da aka ci da yaƙi.
27 and divide the plunder into two parts: between the men skilled in war, who went out to battle, and all the congregation.
Ku kasa ganimar kashi biyu, ku ba sojojin da suka tafi yaƙi kashi ɗaya, kashi ɗaya kuma ku ba wa jama’a.
28 Levy a tribute to the LORD of the men of war who went out to battle: one soul of five hundred; of the persons, of the cattle, of the donkeys, and of the flocks.
Daga sojojin da suka je yaƙin kuwa, ka ware ganima wa Ubangiji, ka ɗauki ɗaya daga cikin mutum ɗari biyar, da shanu ɗari biyar, da jakuna ɗari biyar, da tumaki ɗari biyar.
29 Take it from their half, and give it to Eleazar the priest, for the LORD’s wave offering.
Ka ɗauki wannan sashe daga rabin rabonsu ka ba wa Eleyazar firist, a matsayin sashe na Ubangiji.
30 Of the children of Israel’s half, you shall take one drawn out of every fifty, of the persons, of the cattle, of the donkeys, and of the flocks, of all the livestock, and give them to the Levites, who perform the duty of the LORD’s tabernacle.”
Daga cikin rabin rabon Isra’ilawa, ka zaɓi ɗaya daga kowane hamsin na mutane, shanu, jakuna, tumaki, awaki ko kuma sauran dabbobi. Ka ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.”
31 Moses and Eleazar the priest did as the LORD commanded Moses.
Saboda haka Musa da Eleyazar suka aikata yadda Ubangiji ya umarci Musa.
32 Now the plunder, over and above the booty which the men of war took, was six hundred seventy-five thousand sheep,
Yawan ganimar da sojoji suka kawo ita ce tumaki 675,000
33 seventy-two thousand head of cattle,
shanu 72,000
34 sixty-one thousand donkeys,
da jakuna 61,000.
35 and thirty-two thousand persons in all, of the women who had not known man by lying with him.
Akwai kuma mata 32,000 da ba su yi lalata ba da namiji ba.
36 The half, which was the portion of those who went out to war, was in number three hundred thirty-seven thousand five hundred sheep;
Kashin da aka ba sojoji waɗanda suka tafi yaƙi shi ne, tumaki 337,500,
37 and the LORD’s tribute of the sheep was six hundred seventy-five.
tumakin da aka ware wa Ubangiji kuwa 657 ne;
38 The cattle were thirty-six thousand, of which the LORD’s tribute was seventy-two.
shanu 36,000, shanun da aka ware wa Ubangiji kuwa 72 ne;
39 The donkeys were thirty thousand five hundred, of which the LORD’s tribute was sixty-one.
jakuna 30,500, jakunan da aka ware wa Ubangiji kuwa 61 ne;
40 The persons were sixteen thousand, of whom the LORD’s tribute was thirty-two persons.
mutane 16,000, mutanen da aka ware wa Ubangiji kuwa 32 ne.
41 Moses gave the tribute, which was the LORD’s wave offering, to Eleazar the priest, as the LORD commanded Moses.
Musa ya ba wa Eleyazar abin da aka ware wa Ubangiji, kamar yadda Ubangiji ya umarci Musa.
42 Of the children of Israel’s half, which Moses divided off from the men who fought
Kashin da aka ba wa Isra’ilawa, wanda Musa ya ware daga cikin na waɗanda suka tafi yaƙi,
43 (now the congregation’s half was three hundred thirty-seven thousand five hundred sheep,
kashin da aka ba wa jama’a kuwa tumaki 337,500 ne,
44 thirty-six thousand head of cattle,
shanu 36,000,
45 thirty thousand five hundred donkeys,
jakuna 30,500
46 and sixteen thousand persons),
da mutane 16,000.
47 even of the children of Israel’s half, Moses took one drawn out of every fifty, both of man and of animal, and gave them to the Levites, who performed the duty of the LORD’s tabernacle, as the LORD commanded Moses.
Daga rabin kashi na Isra’ilawa, Musa ya ɗauki ɗaya daga cikin hamsin na mutane da na dabbobi, yadda Ubangiji ya umarce shi, ya ba wa Lawiyawan da suke lura da tabanakul na Ubangiji.
48 The officers who were over the thousands of the army, the captains of thousands, and the captains of hundreds, came near to Moses.
Sai shugabannin da suka shugabancin rundunar yaƙin, shugabanni na dubu-dubu da shugabanni na ɗari-ɗari, suka zo wurin Musa
49 They said to Moses, “Your servants have taken the sum of the men of war who are under our command, and there lacks not one man of us.
suka ce masa, “Barorinka sun ƙidaya mayaƙan da suke ƙarƙashinmu, babu ko ɗayan ya ɓace.
50 We have brought the LORD’s offering, what every man found: gold ornaments, armlets, bracelets, signet rings, earrings, and necklaces, to make atonement for our souls before the LORD.”
Saboda haka mun kawo wa Ubangiji hadaya na kayan zinariya da kowannenmu ya samu, mundaye, ƙawane,’yan kunne da duwatsun wuya, don yin wa kanmu kafara a gaban Ubangiji.”
51 Moses and Eleazar the priest took their gold, even all worked jewels.
Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya da kayan adon duka daga gare su.
52 All the gold of the wave offering that they offered up to the LORD, of the captains of thousands, and of the captains of hundreds, was sixteen thousand seven hundred fifty shekels.
Dukan zinariya da shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, waɗanda Musa da Eleyazar suka karɓa, suka kuma miƙa hadaya ga Ubangiji, nauyinta ta kai shekel 16,750.
53 The men of war had taken booty, every man for himself.
Kowane soja, ya kwashi ganima wa kansa.
54 Moses and Eleazar the priest took the gold of the captains of thousands and of hundreds, and brought it into the Tent of Meeting for a memorial for the children of Israel before the LORD.
Musa da Eleyazar firist, suka karɓi zinariya daga shugabannin dubu-dubu da shugabannin ɗari-ɗari, suka kawo cikin Tentin Sujada, don su zama abin tuni ga Isra’ilawa a gaban Ubangiji.

< Numbers 31 >