< Numbers 13 >

1 The LORD spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “Send men, that they may spy out the land of Canaan, which I give to the children of Israel. Of every tribe of their fathers, you shall send a man, every one a prince among them.”
“Ka aiki waɗansu mutane zuwa ƙasar Kan’ana, wadda nake ba Isra’ilawa. Daga kowace kabila, ka aiki ɗaya daga cikin shugabanninta.”
3 Moses sent them from the wilderness of Paran according to the commandment of the LORD. All of them were men who were heads of the children of Israel.
Saboda haka bisa ga umarnin Ubangiji, Musa ya aike su daga Hamadan Faran. Dukansu kuwa shugabanni ne na Isra’ilawa.
4 These were their names: Of the tribe of Reuben, Shammua the son of Zaccur.
Shugabannin kuwa su ne, Shammuwa ɗan Zakkur, daga kabilar Ruben;
5 Of the tribe of Simeon, Shaphat the son of Hori.
Shafat ɗan Hori, daga kabilar Simeyon;
6 Of the tribe of Judah, Caleb the son of Jephunneh.
Kaleb ɗan Yefunne, daga kabilar Yahuda;
7 Of the tribe of Issachar, Igal the son of Joseph.
Igal ɗan Yusuf, daga kabilar Issakar;
8 Of the tribe of Ephraim, Hoshea the son of Nun.
Hosheya ɗan Nun, daga kabilar Efraim;
9 Of the tribe of Benjamin, Palti the son of Raphu.
daga kabilar Benyamin, Falti ɗan Rafu;
10 Of the tribe of Zebulun, Gaddiel the son of Sodi.
Gaddiyel ɗan Sodi, daga kabilar Zebulun;
11 Of the tribe of Joseph, of the tribe of Manasseh, Gaddi the son of Susi.
Gaddi ɗan Susi, daga kabilar Manasse (wata kabilar Yusuf);
12 Of the tribe of Dan, Ammiel the son of Gemalli.
Ammiyel ɗan Gemalli, daga kabilar Dan;
13 Of the tribe of Asher, Sethur the son of Michael.
Setur ɗan Mika’ilu, daga kabilar Asher;
14 Of the tribe of Naphtali, Nahbi the son of Vophsi.
Nabi ɗan Bofsi, daga kabilar Naftali;
15 Of the tribe of Gad, Geuel the son of Machi.
Geyuwel ɗan Maki, daga kabilar Gad.
16 These are the names of the men who Moses sent to spy out the land. Moses called Hoshea the son of Nun Joshua.
Waɗannan su ne sunayen mutanen da Musa ya aika su binciki ƙasar. (Sai Musa ya ba Hosheya ɗan Nun, suna Yoshuwa.)
17 Moses sent them to spy out the land of Canaan, and said to them, “Go up this way by the South, and go up into the hill country.
Sa’ad da Musa ya aike su domin su binciki Kan’ana ya ce, “Ku haura, ku ratsa ta Negeb har zuwa ƙasar tudu.
18 See the land, what it is; and the people who dwell therein, whether they are strong or weak, whether they are few or many;
Ku ga yadda ƙasar take, ku ga ko mutanen da suke zama a can ƙarfafa ne, ko raunannu, ko su kima ne, ko kuma suna da yawa.
19 and what the land is that they dwell in, whether it is good or bad; and what cities they are that they dwell in, whether in camps, or in strongholds;
Wace irin ƙasa ce suke zama a ciki, Mai kyau ce, ko mummuna? Waɗanne irin birane ne suke zama a ciki? Suna da katanga, ko babu?
20 and what the land is, whether it is fertile or poor, whether there is wood therein, or not. Be courageous, and bring some of the fruit of the land.” Now the time was the time of the first-ripe grapes.
Yaya ƙasar take? Tana da wadata, ko babu? Akwai itatuwa, ko babu? Ku yi iya ƙoƙarinku ku ɗebo daga cikin albarkar ƙasar ku kawo.” (Lokacin farkon nunan inabi ne.)
21 So they went up, and spied out the land from the wilderness of Zin to Rehob, to the entrance of Hamath.
Saboda haka suka haura, suka binciki ƙasar daga Hamadan Zin har zuwa Rehob, wajen Lebo Hamat.
22 They went up by the South, and came to Hebron; and Ahiman, Sheshai, and Talmai, the children of Anak, were there. (Now Hebron was built seven years before Zoan in Egypt.)
Suka kuma haura ta Negeb, suka iso Hebron, inda Ahiman, da Sheshai, da Talmai, zuriyar Anak, suke zama. (An gina Hebron da shekara bakwai kafin a gina Zowan a Masar.)
23 They came to the valley of Eshcol, and cut down from there a branch with one cluster of grapes, and they bore it on a staff between two. They also brought some of the pomegranates and figs.
Da suka iso Kwarin Eshkol, sai suka yanko reshe guda na nonon inabi tare da’ya’yansa cunkus. Mutum biyu suka ɗauka shi rataye a sanda a kafaɗarsu, suka haɗa tare da rumman da kuma ɓaure.
24 That place was called the valley of Eshcol, because of the cluster which the children of Israel cut down from there.
Sai aka kira wurin Kwarin Eshkol saboda nonon inabin da suka yi cunkus, wanda Isra’ilawa suka yanko a wurin.
25 They returned from spying out the land at the end of forty days.
A ƙarshen kwana arba’in sai suka komo daga bincikensu.
26 They went and came to Moses, to Aaron, and to all the congregation of the children of Israel, to the wilderness of Paran, to Kadesh; and brought back word to them and to all the congregation. They showed them the fruit of the land.
Suka dawo wurin Musa, da Haruna, da dukan jama’ar Isra’ilawa, a Kadesh, a Hamadan Faran. A can suka ba da rahoton ga dukan taron da yake wurin, suka kuma nuna musu amfanin ƙasar.
27 They told him, and said, “We came to the land where you sent us. Surely it flows with milk and honey, and this is its fruit.
Suka ce wa Musa, “Mun je ƙasar da ka aike mu, ƙasar tana zub da madara da zuma! Ga kuma amfaninta.
28 However, the people who dwell in the land are strong, and the cities are fortified and very large. Moreover, we saw the children of Anak there.
Amma fa mazaunan can ɗin ƙarfafa ne, an kuma kewaye biranen da manya-manyan katanga. Mun kuma ga zuriyar Anak a can.
29 Amalek dwells in the land of the South. The Hittite, the Jebusite, and the Amorite dwell in the hill country. The Canaanite dwells by the sea, and along the side of the Jordan.”
Amalekawa suna zama a Negeb; Hittiyawa, Yebusiyawa da kuma Amoriyawa, suna zama ne a ƙasar tudu. Kan’aniyawa kuma suna zama kusa da teku da kuma a bakin Urdun.”
30 Caleb stilled the people before Moses, and said, “Let’s go up at once, and possess it; for we are well able to overcome it!”
Sai Kaleb ya sa mutane suka yi shiru a gaban Musa, sai ya ce, “Ya kamata mu tafi mu mallaki ƙasar, gama lalle za mu iya cinta.”
31 But the men who went up with him said, “We aren’t able to go up against the people; for they are stronger than we.”
Amma sauran mutanen da suka je tare da shi, suka ce, “Ba za mu iya kara da mutanen nan ba; sun fi mu ƙarfi.”
32 They brought up an evil report of the land which they had spied out to the children of Israel, saying, “The land, through which we have gone to spy it out, is a land that eats up its inhabitants; and all the people who we saw in it are men of great stature.
Sai suka yaɗa labari marar kyau ga Isra’ilawa game da ƙasar da suka binciko. Suka ce, “Ƙasar da muka ratsa cikinta domin mu leƙi asirinta, tana cinye waɗanda suke zama a cikinta. Dukan mutanen da muka gani a wurin, ƙatti ne.
33 There we saw the Nephilim, the sons of Anak, who come from the Nephilim. We were in our own sight as grasshoppers, and so we were in their sight.”
Mun ga Nefilimawa a can (zuriyar Anak sun fito ne daga Nefilim). Sai muka ga kanmu kamar fāra ne kawai, haka kuwa muke a gare su.”

< Numbers 13 >