< Lamentations 5 >

1 Remember, LORD, what has come on us. Look, and see our reproach.
Ka tuna, ya Ubangiji, abin da ya faru da mu; duba, ka ga kunyar da muka sha.
2 Our inheritance has been turned over to strangers, our houses to aliens.
An ba wa baƙi gādonmu, gidajenmu kuma aka ba bare.
3 We are orphans and fatherless. Our mothers are as widows.
Mun zama marayu marasa ubanni, uwayenmu kamar gwauraye.
4 We must pay for water to drink. Our wood is sold to us.
Dole mu sayi ruwan da muke sha; sai mun biya mu sami itace.
5 Our pursuers are on our necks. We are weary, and have no rest.
Masu fafararmu sun kusa kama mu; mun gaji kuma ba dama mu huta.
6 We have given our hands to the Egyptians, and to the Assyrians, to be satisfied with bread.
Mun miƙa kanmu ga Masar da Assuriya don mu sami isashen abinci.
7 Our fathers sinned, and are no more. We have borne their iniquities.
Kakanninmu sun yi zunubi kuma ba sa nan yanzu, mu ne aka bari muna shan hukuncinsu.
8 Servants rule over us. There is no one to deliver us out of their hand.
Bayi suna mulki a kanmu, kuma ba wanda zai’yantar da mu daga hannuwansu.
9 We get our bread at the peril of our lives, because of the sword in the wilderness.
Muna samun burodi a bakin rayukanmu domin takobin da yake a jeji.
10 Our skin is black like an oven, because of the burning heat of famine.
Fatar jikinmu ta yi zafi kamar murhu, muna jin zazzaɓi domin yunwa.
11 They ravished the women in Zion, the virgins in the cities of Judah.
An yi wa mata fyaɗe a cikin Sihiyona, da kuma budurwai a cikin garuruwan Yahuda.
12 Princes were hanged up by their hands. The faces of elders were not honored.
An rataye’ya’yan sarakuna da hannuwansu; ba a ba wa dattawa girma.
13 The young men carry millstones. The children stumbled under loads of wood.
Samari suna faman yin niƙa; yara kuma suna fama da ƙyar da nauyin kayan itace.
14 The elders have ceased from the gate, and the young men from their music.
Dattawan sun bar ƙofar birnin, samari sun daina rera waƙa.
15 The joy of our heart has ceased. Our dance is turned into mourning.
Farin ciki ya rabu da zuciyarmu; rayuwarmu ta zama makoki.
16 The crown has fallen from our head. Woe to us, for we have sinned!
Rawani ya fāɗi daga kanmu. Kaiton mu gama mun yi zunubi!
17 For this our heart is faint. For these things our eyes are dim:
Domin wannan zuciyarmu ta yi sanyi; domin waɗannan abubuwa idanunmu sun dushe
18 for the mountain of Zion, which is desolate. The foxes walk on it.
gama Tudun Sihiyona ya zama kufai, sai diloli ke yawo a wurin.
19 You, LORD, remain forever. Your throne is from generation to generation.
Ya Ubangiji, kai ne mai iko har abada; kursiyinka ya dawwama cikin dukan zamani.
20 Why do you forget us forever, and forsake us for so long a time?
Don mene ne kake mantawa da mu koyaushe? Me ya sa ka yashe mu da jimawa?
21 Turn us to yourself, LORD, and we will be turned. Renew our days as of old.
Ka sāke jawo mu gare ka, ya Ubangiji, don mu komo; ka sabunta kwanakinmu su zama kamar yadda suke a dā
22 But you have utterly rejected us. You are very angry against us.
sai dai in ka ƙi mu gaba ɗaya kana fushi da mu fiye da yadda za a iya aunawa.

< Lamentations 5 >