< Joshua 15 >

1 The lot for the tribe of the children of Judah according to their families was to the border of Edom, even to the wilderness of Zin southward, at the uttermost part of the south.
An raba wa kabilar Yahuda gādonsu ta wurin yin ƙuri’a, bisa ga iyalansu, rabon ya kai har zuwa sashen Edom, zuwa Jejin Zin can kurewar kudu.
2 Their south border was from the uttermost part of the Salt Sea, from the bay that looks southward;
Iyakarsu a kudanci ta tashi tun daga kurewar kudu na Tekun Gishiri,
3 and it went out southward of the ascent of Akrabbim, and passed along to Zin, and went up by the south of Kadesh Barnea, and passed along by Hezron, went up to Addar, and turned toward Karka;
zuwa kudancin Hanyar Kunama, ta ci gaba har zuwa Zin, zuwa kudancin Kadesh Barneya. Sa’an nan ta kurɗa zuwa Hezron har zuwa Addar, ta kuma karkata zuwa Karka.
4 and it passed along to Azmon, went out at the brook of Egypt; and the border ended at the sea. This shall be your south border.
Sai ta wuce zuwa Azmon ta haɗu da Rafin Masar, ta ƙarasa a Bahar Rum. Wannan shi ne iyakarsu ta kudu.
5 The east border was the Salt Sea, even to the end of the Jordan. The border of the north quarter was from the bay of the sea at the end of the Jordan.
Iyakarsu ta gabas kuwa ita ce Tekun Gishiri wadda ta zarce har zuwa gaɓar Urdun. Iyakarsu ta arewa ta fara ne daga Tekun Gishiri a bakin Urdun,
6 The border went up to Beth Hoglah, and passed along by the north of Beth Arabah; and the border went up to the stone of Bohan the son of Reuben.
wajen Bet-Hogla ta wuce har zuwa arewancin Bet-Araba, zuwa Dutsen Bohan ɗan Ruben.
7 The border went up to Debir from the valley of Achor, and so northward, looking toward Gilgal, that faces the ascent of Adummim, which is on the south side of the river. The border passed along to the waters of En Shemesh, and ended at En Rogel.
Sai iyakar ta haura zuwa Debir daga Kwarin Akor ta juya arewa da Gilgal, wadda take fuskantar hawan Adummim a kudancin kwari, ta ci gaba zuwa ruwan En Shemesh, ta ɓullo ta En Rogel.
8 The border went up by the valley of the son of Hinnom to the side of the Jebusite (also called Jerusalem) southward; and the border went up to the top of the mountain that lies before the valley of Hinnom westward, which is at the farthest part of the valley of Rephaim northward.
Sai kuma ta gangara zuwa Kwarin Ben Hinnom a gangaren kudancin birnin Yebusiyawa (wato, Urushalima). Daga can ta haura zuwa kan tudun a yammancin Kwarin Hinnom, a arewancin ƙarshen Kwarin Refayim.
9 The border extended from the top of the mountain to the spring of the waters of Nephtoah, and went out to the cities of Mount Ephron; and the border extended to Baalah (also called Kiriath Jearim);
Daga kan tudun, iyakar ta nufi maɓulɓular ruwa na Neftowa, ta ɓullo a garuruwan da suke a Dutsen Efron, ta gangara zuwa Ba’ala (wato, Kiriyat Yeyarim).
10 and the border turned about from Baalah westward to Mount Seir, and passed along to the side of Mount Jearim (also called Chesalon) on the north, and went down to Beth Shemesh, and passed along by Timnah;
Sa’an nan ta karkata yamma daga Ba’ala zuwa Dutsen Seyir, ta wuce ta gangaren Dutsen Yeyarim (wato, Kesalon), ta ci gaba zuwa Bet-Shemesh, ta bi zuwa Timna.
11 and the border went out to the side of Ekron northward; and the border extended to Shikkeron, and passed along to Mount Baalah, and went out at Jabneel; and the goings out of the border were at the sea.
Ta wuce zuwa gangaren arewancin Ekron, ta juya zuwa Shikkeron, ta wuce zuwa Dutsen Ba’ala, ta kai Yabneyel, iyakarta ta ƙare a teku.
12 The west border was to the shore of the great sea. This is the border of the children of Judah according to their families.
Bakin Bahar Rum nan ne iyakar yammanci. Wannan ita ce iyakar da ta kewaye jama’ar Yahuda bisa ga iyalansu.
13 He gave to Caleb the son of Jephunneh a portion among the children of Judah, according to the commandment of the LORD to Joshua, even Kiriath Arba, named after the father of Anak (also called Hebron).
Yoshuwa ya ba Kaleb ɗan Yefunne wuri a Yahuda, Kiriyat Arba, wato, Hebron, bisa ga umarnin Ubangiji. (Arba shi ne mahaifin Anak.)
14 Caleb drove out the three sons of Anak: Sheshai, and Ahiman, and Talmai, the children of Anak.
Daga can sai Kaleb ya kori’ya’yan Anak, maza su uku daga Hebron, wato, Sheshai, Ahiman da Talmai.
15 He went up against the inhabitants of Debir: now the name of Debir before was Kiriath Sepher.
Daga can ya nufi Debir ya yi yaƙi da mutanen da suke zama a can (Dā sunan Debir, Kiriyat Sefer ne).
16 Caleb said, “He who strikes Kiriath Sepher, and takes it, to him I will give Achsah my daughter as wife.”
Kaleb ya ce, “Zan ba da’yata Aksa aure ga wanda zai ci Kiriyat Sefer da yaƙi.”
17 Othniel the son of Kenaz, the brother of Caleb, took it: and he gave him Achsah his daughter as wife.
Otniyel ɗan Kenaz, ɗan’uwan Kaleb, ya ci Kiriyat Sefer da yaƙi; saboda haka Kaleb ya ba wa Aksa’yarsa, ya kuwa aure ta.
18 When she came, she had him ask her father for a field. She got off her donkey, and Caleb said, “What do you want?”
Wata rana da ta zo wurin Otniyel, sai ya zuga ta ta roƙi mahaifinta fili. Da ta sauka daga kan jakinta sai Kaleb ya tambaye ta ya ce, “Me kike so in yi miki?”
19 She said, “Give me a blessing. Because you have set me in the land of the South, give me also springs of water.” So he gave her the upper springs and the lower springs.
Ta amsa ta ce, “Ka yi mini alheri na musamman, tun da ka ba ni wuri a Negeb, ina roƙonka, ka ba ni maɓulɓulan ruwa.” Kaleb kuwa ya ba ta maɓulɓulan ruwa na tuddai da na kwari.
20 This is the inheritance of the tribe of the children of Judah according to their families.
Wannan shi ne gādon kabilar Yahuda bisa ga iyalansu.
21 The farthest cities of the tribe of the children of Judah toward the border of Edom in the South were Kabzeel, Eder, Jagur,
Garuruwan kabilar Yahuda da suke kudu cikin Negeb zuwa iyakar Edom su ne. Kabzeyel, Eder, Yagur,
22 Kinah, Dimonah, Adadah,
Kina, Dimona, Adada,
23 Kedesh, Hazor, Ithnan,
Kedesh, Hazor, Itnan,
24 Ziph, Telem, Bealoth,
Zif, Telem, Beyalot,
25 Hazor Hadattah, Kerioth Hezron (also called Hazor),
Hazor-Hadatta, Keriyot Hezron (wato, Hazor),
26 Amam, Shema, Moladah,
Amam, Shema, Molada,
27 Hazar Gaddah, Heshmon, Beth Pelet,
Hazar Gadda, Heshmon, Bet-Felet,
28 Hazar Shual, Beersheba, Biziothiah,
Hazar Shuwal, Beyersheba, Biziyotiya,
29 Baalah, Iim, Ezem,
Ba’ala, Iyim, Ezem,
30 Eltolad, Chesil, Hormah,
Eltolad, Kesil, Horma,
31 Ziklag, Madmannah, Sansannah,
Ziklag, Madmanna, Sansanna,
32 Lebaoth, Shilhim, Ain, and Rimmon. All the cities are twenty-nine, with their villages.
Lebayot, Shilhim, Ayin, Rimmon, jimillarsu, garuruwa da ƙauyukansu duka ashirin da tara ne.
33 In the lowland, Eshtaol, Zorah, Ashnah,
Biranen da suke a filayen kwari su ne, Eshtawol, Zora; Ashna,
34 Zanoah, En Gannim, Tappuah, Enam,
Zanowa, En Gannim, Taffuwa, Enam,
35 Jarmuth, Adullam, Socoh, Azekah,
Yarmut, Adullam, Soko, Azeka,
36 Shaaraim, Adithaim and Gederah (or Gederothaim); fourteen cities with their villages.
Sha’arayim, Aditayim, Gedera (Gederotayim ke nan). Garuruwa goma sha huɗu ke nan da ƙauyukansu.
37 Zenan, Hadashah, Migdal Gad,
Zenan, Hadasha, Migdal Gad,
38 Dilean, Mizpah, Joktheel,
Dileyan, Mizfa, Yokteyel,
39 Lachish, Bozkath, Eglon,
Lakish, Bozkat, Eglon,
40 Cabbon, Lahmam, Chitlish,
Kabbon, Lahman, Kitlish,
41 Gederoth, Beth Dagon, Naamah, and Makkedah; sixteen cities with their villages.
Gederot, Bet-Dagon, Na’ama, Makkeda, garuruwa goma sha shida ke nan da ƙauyukansu.
42 Libnah, Ether, Ashan,
Libna, Eter, Ashan,
43 Iphtah, Ashnah, Nezib,
Yefta, Ashna, Nezib,
44 Keilah, Achzib, and Mareshah; nine cities with their villages.
Keyila, Akzib, Maresha, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
45 Ekron, with its towns and its villages;
Ekron da ƙauyukan da suke kewaye da ita;
46 from Ekron even to the sea, all that were by the side of Ashdod, with their villages.
yammancin Ekron da dukan garuruwa da ƙauyukan da suke kusa da Ashdod.
47 Ashdod, its towns and its villages; Gaza, its towns and its villages; to the brook of Egypt, and the great sea with its coastline.
Ashdod da garuruwa da kuma ƙauyukan da suke kewaye da ita, Gaza da garuruwanta da ƙauyukanta har zuwa Rafin Masar da kuma Bahar Rum.
48 In the hill country, Shamir, Jattir, Socoh,
Birane na cikin ƙasar tuddai kuwa, su ne, Shamir, Yattir, Soko,
49 Dannah, Kiriath Sannah (which is Debir),
Danna, Kiriyat Sanna (wato, Debir),
50 Anab, Eshtemoh, Anim,
Anab, Eshtemo, Anim,
51 Goshen, Holon, and Giloh; eleven cities with their villages.
Goshen, Holon, Gilo, garuruwa goma sha ɗaya ke nan da ƙauyukansu.
52 Arab, Dumah, Eshan,
Arab, Duma, Eshan,
53 Janim, Beth Tappuah, Aphekah,
Yanum, Bet-Taffuwa, Afeka,
54 Humtah, Kiriath Arba (also called Hebron), and Zior; nine cities with their villages.
Humta, Kiriyat Arba (wato, Hebron) da Ziyor, garuruwa tara ke nan da ƙauyukansu.
55 Maon, Carmel, Ziph, Jutah,
Mawon, Karmel, Zif, Yutta
56 Jezreel, Jokdeam, Zanoah,
Yezireyel, Yokdeyam, Zanowa,
57 Kain, Gibeah, and Timnah; ten cities with their villages.
Kayin, Gibeya, Timna, garuruwa goma ke nan da ƙauyukansu.
58 Halhul, Beth Zur, Gedor,
Halhul, Bet-Zur, Gedor,
59 Maarath, Beth Anoth, and Eltekon; six cities with their villages.
Ma’arat, Bet-Anot, Eltekon, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
60 Kiriath Baal (also called Kiriath Jearim), and Rabbah; two cities with their villages.
Kiriyat Ba’al (wato, Kiriyat Yeyarim) da Rabba, garuruwa biyu ke nan da ƙauyukansu.
61 In the wilderness, Beth Arabah, Middin, Secacah,
Biranen da suke a jeji kuwa su ne, Bet-Araba, Middin, Sekaka,
62 Nibshan, the City of Salt, and En Gedi; six cities with their villages.
Nibshan, Birnin gishiri da En Gedi, garuruwa shida ke nan da ƙauyukansu.
63 As for the Jebusites, the inhabitants of Jerusalem, the children of Judah couldn’t drive them out; but the Jebusites live with the children of Judah at Jerusalem to this day.
Kabilar Yahuda kuwa ba su iya korar Yebusiyawa waɗanda suke zama cikin Urushalima ba; har wa yau Yebusiyawa suna nan zaune tare da mutanen Yahuda.

< Joshua 15 >