< Genesis 11 >

1 The whole earth was of one language and of one speech.
To, a lokacin, yaren mutanen duniya ɗaya ne, maganarsu kuma ɗaya ce.
2 As they traveled east, they found a plain in the land of Shinar, and they lived there.
Yayinda mutane suke ta yin ƙaura zuwa gabas, sai suka sami fili a Shinar, suka zauna a can.
3 They said to one another, “Come, let’s make bricks, and burn them thoroughly.” They had brick for stone, and they used tar for mortar.
Suka ce wa juna, “Ku zo, mu yi tubula, mu gasa su sosai.” Suka yi amfani da tubula a maimakon duwatsu, kwalta kuma a maimakon laka.
4 They said, “Come, let’s build ourselves a city, and a tower whose top reaches to the sky, and let’s make a name for ourselves, lest we be scattered abroad on the surface of the whole earth.”
Sa’an nan suka ce, “Ku zo, mu gina wa kanmu birni da hasumiyar da za tă kai har sammai, domin mu yi wa kanmu suna, don kada mu warwatsu ko’ina a doron ƙasa.”
5 The LORD came down to see the city and the tower, which the children of men built.
Sai Ubangiji ya sauko don yă ga birni da kuma hasumiyar da mutanen suke gini.
6 The LORD said, “Behold, they are one people, and they all have one language, and this is what they begin to do. Now nothing will be withheld from them, which they intend to do.
Ubangiji ya ce, “Ga su, su jama’a ɗaya ce, su duka kuwa harshensu guda ne. Wannan kuwa masomi ne kawai na abin da za su iya yi, babu kuma abin da suka yi shirya yi da ba za su iya yi ba.
7 Come, let’s go down, and there confuse their language, that they may not understand one another’s speech.”
Zo, mu sauka, mu rikitar da harshensu don kada su fahimci juna.”
8 So the LORD scattered them abroad from there on the surface of all the earth. They stopped building the city.
Saboda haka Ubangiji ya watsar da su daga wurin zuwa ko’ina a doron ƙasa, suka kuwa daina gina birnin.
9 Therefore its name was called Babel, because there the LORD confused the language of all the earth. From there, the LORD scattered them abroad on the surface of all the earth.
Shi ya sa aka kira birnin Babel, domin a can ne Ubangiji ya rikitar da harshen dukan duniya. Daga can Ubangiji ya watsar da su ko’ina a doron ƙasa.
10 This is the history of the generations of Shem: Shem was one hundred years old when he became the father of Arpachshad two years after the flood.
Wannan shi ne labarin Shem. Shekara biyu bayan ambaliya, sa’ad da Shem ya yi shekara 100, sai ya haifi Arfakshad.
11 Shem lived five hundred years after he became the father of Arpachshad, and became the father of more sons and daughters.
Bayan ya haifi Arfakshad, Shem ya yi shekara 500, ya haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
12 Arpachshad lived thirty-five years and became the father of Shelah.
Sa’ad da Arfakshad ya yi shekara 35, sai ya haifi Shela.
13 Arpachshad lived four hundred three years after he became the father of Shelah, and became the father of more sons and daughters.
Bayan ya haifi Shela kuwa, Arfakshad ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
14 Shelah lived thirty years, and became the father of Eber.
Sa’ad da Shela ya yi shekaru 30, sai ya haifi Eber.
15 Shelah lived four hundred three years after he became the father of Eber, and became the father of more sons and daughters.
Bayan ya haifi Eber, Shela ya yi shekara 403, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
16 Eber lived thirty-four years, and became the father of Peleg.
Sa’ad da Eber ya yi shekaru 34, sai ya haifi Feleg.
17 Eber lived four hundred thirty years after he became the father of Peleg, and became the father of more sons and daughters.
Bayan ya haifi Feleg, Eber ya yi shekara 430, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
18 Peleg lived thirty years, and became the father of Reu.
Sa’ad da Feleg ya yi shekaru 30, sai ya haifi Reyu.
19 Peleg lived two hundred nine years after he became the father of Reu, and became the father of more sons and daughters.
Bayan ya haifi Reyu, Feleg ya yi shekara 209, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
20 Reu lived thirty-two years, and became the father of Serug.
Sa’ad da Reyu ya yi shekaru 32, sai ya haifi Serug.
21 Reu lived two hundred seven years after he became the father of Serug, and became the father of more sons and daughters.
Bayan ya haifi Serug, Reyu ya yi shekara 207, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
22 Serug lived thirty years, and became the father of Nahor.
Sa’ad da Serug ya yi shekaru 30, sai ya haifi Nahor.
23 Serug lived two hundred years after he became the father of Nahor, and became the father of more sons and daughters.
Bayan ya haifi Nahor, Serug ya yi shekara 200, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
24 Nahor lived twenty-nine years, and became the father of Terah.
Sa’ad da Nahor ya yi shekaru 29, sai ya haifi Tera.
25 Nahor lived one hundred nineteen years after he became the father of Terah, and became the father of more sons and daughters.
Bayan ya haifi Tera, Nahor ya yi shekara 119, ya kuma haifi waɗansu’ya’ya maza da mata.
26 Terah lived seventy years, and became the father of Abram, Nahor, and Haran.
Bayan Tera ya yi shekaru 70, sai ya haifi Abram, Nahor da Haran.
27 Now this is the history of the generations of Terah. Terah became the father of Abram, Nahor, and Haran. Haran became the father of Lot.
Wannan ita ce zuriyar Tera. Tera ya haifi Abram, Nahor da Haran. Haran kuma ya haifi Lot.
28 Haran died in the land of his birth, in Ur-Kasdim, while his father Terah was still alive.
Yayinda mahaifinsa Tera yana da rai, Haran ya rasu a Ur ta Kaldiyawa, a ƙasar haihuwarsa.
29 Abram and Nahor married wives. The name of Abram’s wife was Sarai, and the name of Nahor’s wife was Milcah, the daughter of Haran, who was also the father of Iscah.
Abram da Nahor suka yi aure. Sunan matar Abram, Saira ne, sunan matar Nahor kuwa Milka; ita’yar Haran ce, mahaifin Milka da Iska.
30 Sarai was barren. She had no child.
Saira kuwa bakararriya ce, ba ta da yara.
31 Terah took Abram his son, Lot the son of Haran, his son’s son, and Sarai his daughter-in-law, his son Abram’s wife. They went from Ur-Kasdim, to go into the land of Canaan. They came to Haran and lived there.
Tera ya ɗauki ɗansa Abraham, jikansa Lot ɗan Haran, da surukarsa Saira, matar Abram, tare kuwa suka bar Ur ta Kaldiyawa, don su tafi Kan’ana. Amma sa’ad da suka zo Haran sai suka zauna a can.
32 The days of Terah were two hundred five years. Terah died in Haran.
Tera yi shekaru 205, ya kuma mutu a Haran.

< Genesis 11 >