< 1 Chronicles 16 >

1 They brought in God’s ark, and set it in the middle of the tent that David had pitched for it; and they offered burnt offerings and peace offerings before God.
Suka fa kawo akwatin alkawarin Allah, suka sa a cikin tentin da Dawuda ya kafa dominsa, suka kuma miƙa hadayun ƙonawa da hadayu na salama a gaban Allah.
2 When David had finished offering the burnt offering and the peace offerings, he blessed the people in the LORD’s name.
Bayan Dawuda ya gama miƙa hadayu na ƙonawa da hadayu na salama, sai ya albarkaci mutane a cikin sunan Ubangiji.
3 He gave to everyone of Israel, both man and woman, to everyone a loaf of bread, a portion of meat, and a cake of raisins.
Sa’an nan ya ba da dunƙulen burodi da wainar dabino da kuma kauɗar zabibi ga kowane mutumin Isra’ila namiji da ta mace.
4 He appointed some of the Levites to minister before the LORD’s ark, and to commemorate, to thank, and to praise the LORD, the God of Israel:
Ya sa Lawiyawa su yi hidima a gaban akwatin alkawarin Ubangiji, su ɗaukaka, su gode, su kuma yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila.
5 Asaph the chief, and second to him Zechariah, then Jeiel, Shemiramoth, Jehiel, Mattithiah, Eliab, Benaiah, Obed-Edom, and Jeiel, with stringed instruments and with harps; and Asaph with cymbals, sounding aloud;
Asaf shi ne babba, sai Zakariya na biye, sa’an nan Ya’aziyel, Shemiramot, Yehiyel, Mattitiya, Eliyab, Benahiya, Obed-Edom da Yehiyel. Su ne za su kaɗa molaye, da garayu, Asaf kuwa zai buga ganguna,
6 with Benaiah and Jahaziel the priests with shofars continually, before the ark of the covenant of God.
Benahiya da Yahaziyel firistoci za su busa ƙahoni kullum a gaban akwatin alkawarin Allah.
7 Then on that day David first ordained giving of thanks to the LORD by the hand of Asaph and his brothers.
A wannan rana, da farko, Dawuda ya sa Asaf da’yan’uwansa su rera wannan zabura ta yabo ga Ubangiji.
8 Oh give thanks to the LORD. Call on his name. Make what he has done known among the peoples.
Ku yi godiya ga Ubangiji, ku yi shelar sunansa; ku sanar a cikin al’ummai abin da ya yi.
9 Sing to him. Sing praises to him. Tell of all his marvelous works.
Ku rera gare shi, ku rera yabo gare shi; ku faɗa dukan ayyukan banmamakinsa.
10 Glory in his holy name. Let the heart of those who seek the LORD rejoice.
Ku ɗaukaka a cikin sunansa mai tsarki bari zukatan waɗanda suke neman Ubangiji su yi farin ciki.
11 Seek the LORD and his strength. Seek his face forever more.
Ku dogara ga Ubangiji da kuma ƙarfinsa; ku nemi fuskarsa kullum.
12 Remember his marvelous works that he has done, his wonders, and the judgments of his mouth,
Ku tuna ayyukan banmamakin da ya aikata, mu’ujizansa da kuma hukuntai da ya yanke,
13 you offspring of Israel his servant, you children of Jacob, his chosen ones.
Ya ku zuriyar Isra’ila bayinsa, Ya ku’ya’yan Yaƙub maza, zaɓaɓɓunsa.
14 He is the LORD our God. His judgments are in all the earth.
Shi ne Ubangiji Allahnmu; hukuntansa suna a cikin dukan duniya.
15 Remember his covenant forever, the word which he commanded to a thousand generations,
Yakan tuna da alkawarinsa har abada, maganar da ya umarta, har tsararraki dubu,
16 the covenant which he made with Abraham, his oath to Isaac.
alkawarin da ya yi wa Ibrahim rantsuwar da ya yi ga Ishaku.
17 He confirmed it to Jacob for a statute, and to Israel for an everlasting covenant,
Ya tabbatar da shi ga Yaƙub kamar ƙa’ida, ga Isra’ila kamar madawwamin alkawari.
18 saying, “I will give you the land of Canaan, The lot of your inheritance,”
“Gare ka zan ba da ƙasar Kan’ana kamar rabon da za ka gāda.”
19 when you were but a few men in number, yes, very few, and foreigners in it.
Sa’ad da suke kima, kima sosai, da kuma baƙi a cikinta,
20 They went about from nation to nation, from one kingdom to another people.
suka yi ta yawo daga al’umma zuwa al’umma, daga wannan mulki zuwa wancan.
21 He allowed no man to do them wrong. Yes, he reproved kings for their sakes,
Bai bar wani ya zalunce su ba; saboda su ya tsawata wa sarakuna.
22 “Don’t touch my anointed ones! Do my prophets no harm!”
“Kada ku taɓa shafaffuna; kada ku yi wa annabawana lahani.”
23 Sing to the LORD, all the earth! Display his salvation from day to day.
Ku rera ga Ubangiji, ku duniya duka; ku yi shelar cetonsa kowace rana.
24 Declare his glory among the nations, and his marvelous works among all the peoples.
Ku furta ɗaukakarsa a cikin al’ummai, ayyukansa masu al’ajabai a cikin mutane.
25 For great is the LORD, and greatly to be praised. He also is to be feared above all gods.
Gama Ubangiji mai girma ne ya kuma cancanci yabo; dole a ji tsoronsa fiye da dukan alloli.
26 For all the gods of the peoples are idols, but the LORD made the heavens.
Gama dukan allolin al’ummai gumaka ne, amma Ubangiji ya yi sammai.
27 Honor and majesty are before him. Strength and gladness are in his place.
Daraja da ɗaukaka suna a gabansa; ƙarfi da farin ciki suna a wurin zamansa.
28 Ascribe to the LORD, you families of the peoples, ascribe to the LORD glory and strength!
Ku yabi Ubangiji, ku iyalan al’ummai, ku yabi ɗaukaka da ƙarfin Ubangiji,
29 Ascribe to the LORD the glory due to his name. Bring an offering, and come before him. Worship the LORD in holy array.
ku ba wa Ubangiji ɗaukakar da ta dace da sunansa. Ku kawo hadaya ku kuma zo gabansa; ku yi wa Ubangiji sujada cikin darajar tsarkinsa.
30 Tremble before him, all the earth. The world also is established that it can’t be moved.
Ku yi rawar jiki a gabansa, ya ku duniya duka! Duniya ta kahu sosai; ba za tă jijjigu ba.
31 Let the heavens be glad, and let the earth rejoice! Let them say among the nations, “The LORD reigns!”
Bari sammai su yi farin ciki, bari duniya tă yi murna; bari su ce a cikin al’ummai, “Ubangiji yana mulki!”
32 Let the sea roar, and its fullness! Let the field exult, and all that is in it!
Bari teku da kome da yake cikinsa su yi ruri; bari gonaki da kome a cikinsu su yi farin ciki!
33 Then the trees of the forest will sing for joy before the LORD, for he comes to judge the earth.
Sa’an nan itatuwan jeji za su rera, za su rera don farin ciki a gaban Ubangiji, gama ya zo don yă hukunta duniya.
34 Oh give thanks to the LORD, for he is good, for his loving kindness endures forever.
Ku yi godiya ga Ubangiji, gama shi nagari ne; ƙaunarsa madawwamiya ce.
35 Say, “Save us, God of our salvation! Gather us together and deliver us from the nations, to give thanks to your holy name, to triumph in your praise.”
Ku yi kuka, ku ce, “Cece mu, ya Allah Mai Cetonmu; tara mu ka kuma cece mu daga al’ummai, don mu yi godiya ga sunanka mai tsarki, don mu ɗaukaka a cikin yabonka.”
36 Blessed be the LORD, the God of Israel, from everlasting even to everlasting. All the people said, “Amen,” and praised the LORD.
Yabi Ubangiji, Allah na Isra’ila, daga madawwami zuwa madawwami. Sai dukan mutane suka ce, “Amin.” Suka kuma “Yabi Ubangiji.”
37 So he left Asaph and his brothers there before the ark of the LORD’s covenant, to minister before the ark continually, as every day’s work required;
Dawuda ya bar Asaf da’yan’uwansa a gaban akwatin alkawarin Ubangiji don su yi hidima a can kullum, bisa ga tsari na kowace rana.
38 and Obed-Edom with their sixty-eight relatives; Obed-Edom also the son of Jeduthun and Hosah to be doorkeepers;
Ya kuma bar Obed-Edom da’yan’uwansa sittin da takwas don su yi hidima tare. Obed-Edom ɗan Yedutun da Hosa kuma, su ne matsaran ƙofofi.
39 and Zadok the priest and his brothers the priests, before the LORD’s tabernacle in the high place that was at Gibeon,
Dawuda ya bar Zadok firist da’yan’uwansa firistoci a gaban tabanakul na Ubangiji a tudun da yake a Gibeyon
40 to offer burnt offerings to the LORD on the altar of burnt offering continually morning and evening, even according to all that is written in the LORD’s law, which he commanded to Israel;
don su miƙa hadayun ƙonawa ga Ubangiji a kan bagaden hadaya ta ƙonawa kullum, da safe da kuma yamma, bisa ga kome da yake a rubutacce a cikin Dokar Ubangiji, da ya ba wa Isra’ila.
41 and with them Heman and Jeduthun and the rest who were chosen, who were mentioned by name, to give thanks to the LORD, because his loving kindness endures forever;
Tare da su akwai Heman da Yedutun da sauran waɗannan zaɓaɓɓun da aka rubuta sunansu don yin godiya ga Ubangiji, “gama ƙaunarsa madawwamiya ce har abada.”
42 and with them Heman and Jeduthun with shofars and cymbals for those that should sound aloud, and with instruments for the songs of God, and the sons of Jeduthun to be at the gate.
Heman da Yedutun su ne da hakkin busa ƙahoni da kaɗa kuge da sauran kayan bushe-bushe da na kaɗe-kaɗe, waɗanda ake amfani da su lokacin da ake rera waƙoƙi masu tsarki.’Ya’yan Yedutun maza, su aka ba wa aikin tsaron ƙofa.
43 All the people departed, each man to his house; and David returned to bless his house.
Sa’an nan dukan mutanen suka tashi, kowa ya koma gidansa, Dawuda ya koma gida yă sa wa iyalinsa albarka.

< 1 Chronicles 16 >