< Psalms 77 >

1 For the Chief Musician. To Jeduthun. A Psalm by Asaph. My cry goes to God! Indeed, I cry to God for help, and for him to listen to me.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Don Yedutun. Na Asaf. Zabura ce. Na yi kuka ga Allah don taimako; na yi kuka ga Allah don yă ji ni.
2 In the day of my trouble I sought the Lord. My hand was stretched out in the night, and didn’t get tired. My soul refused to be comforted.
Sa’ad da nake cikin damuwa, na nemi Ubangiji; da dare na miƙa hannuwa ba gajiya raina kuma ya ƙi yă ta’azantu.
3 I remember God, and I groan. I complain, and my spirit is overwhelmed. (Selah)
Na tuna da kai, ya Allah, na kuma yi nishi; na yi nishi, ƙarfina kuwa duk ya raunana. (Sela)
4 You hold my eyelids open. I am so troubled that I can’t speak.
ka hana idanuna rufewa; na damu ƙwarai har ba na iya magana.
5 I have considered the days of old, the years of ancient times.
Na yi tunani kwanakin da suka wuce, shekarun da suka wuce da daɗewa;
6 I remember my song in the night. I consider in my own heart; my spirit diligently enquires:
na tuna da waƙoƙina da dare. Zuciyata ta yi nishi, ƙarfina kuwa ya nemi yă sani.
7 “Will the Lord reject us forever? Will he be favourable no more?
“Ubangiji zai ƙi ne har abada? Ba zai taɓa nuna alherinsa kuma ba?
8 Has his loving kindness vanished forever? Does his promise fail for generations?
Ƙaunarsa marar ƙarewa ta ɓace ke nan har abada? Alkawarinsa ya kāsa ke nan a dukan lokaci?
9 Has God forgotten to be gracious? Has he, in anger, withheld his compassion?” (Selah)
Allah ya manta yă yi jinƙai? Cikin fushinsa ya janye tausayinsa ne?” (Sela)
10 Then I thought, “I will appeal to this: the years of the right hand of the Most High.”
Sai na yi tunani, “Zan yi roƙo saboda wannan, shekarun da Mafi Ɗaukaka ya miƙa hannunsa na dama.”
11 I will remember the LORD’s deeds; for I will remember your wonders of old.
Zan tuna da ayyukan Ubangiji; I, zan tuna mu’ujizanka na tun dā.
12 I will also meditate on all your work, and consider your doings.
Zan yi tunani a kan dukan ayyukanka in lura da dukan manyan abubuwan da ka aikata.
13 Your way, God, is in the sanctuary. What god is great like God?
Hanyoyinka, ya Allah, masu tsarki ne. Wanda allah ne yake da girma kamar Allahnmu?
14 You are the God who does wonders. You have made your strength known amongst the peoples.
Kai ne Allahn da yakan aikata mu’ujizai; ka nuna ikonka a cikin mutane.
15 You have redeemed your people with your arm, the sons of Jacob and Joseph. (Selah)
Da hannunka mai ƙarfi ka fanshi mutanenka, zuriyar Yaƙub da Yusuf. (Sela)
16 The waters saw you, God. The waters saw you, and they writhed. The depths also convulsed.
Ruwaye sun gan ka, ya Allah, ruwaye sun gan ka suka firgita; zurfafan gaske sun girgiza.
17 The clouds poured out water. The skies resounded with thunder. Your arrows also flashed around.
Gizagizai sun sauko da ruwa, sararin sama suka buga tsawa; kibiyoyinka suka yi ta kai komo da walƙiya.
18 The voice of your thunder was in the whirlwind. The lightnings lit up the world. The earth trembled and shook.
Aka ji tsawanka a cikin guguwa, walƙiyarka ta haskaka duniya; duniya ta yi rawar jiki ta girgiza.
19 Your way was through the sea, your paths through the great waters. Your footsteps were not known.
Hanyarka ta bi ta cikin teku, hanyarka ta bi cikin manyan ruwaye, duk da haka ba a ga sawunka ba.
20 You led your people like a flock, by the hand of Moses and Aaron.
Ka bi da mutanenka kamar garke ta hannun Musa da Haruna.

< Psalms 77 >