< Psalms 48 >

1 A Song. A Psalm by the sons of Korah. Great is the LORD, and greatly to be praised, in the city of our God, in his holy mountain.
Waƙa ce. Zabura ta’ya’yan Kora maza. Ubangiji mai girma ne, kuma mafificin yabo, a birnin Allahnmu, dutsensa mai tsarki.
2 Beautiful in elevation, the joy of the whole earth, is Mount Zion, on the north sides, the city of the great King.
Kyakkyawa ce cikin tsayinta, abin farin cikin dukan duniya. Kamar ƙwanƙoli mafi tsayi na Zafon ne Dutsen Sihiyona, birnin Babban Sarki.
3 God has shown himself in her citadels as a refuge.
Allah yana cikin fadodinta; ya nuna kansa mafaka ce gare ta.
4 For, behold, the kings assembled themselves, they passed by together.
Sa’ad da sarakuna suka haɗa rundunoni, sa’ad da suka yi gaba tare,
5 They saw it, then they were amazed. They were dismayed. They hurried away.
sun gan ta suka kuwa yi mamaki; suka gudu don tsoro.
6 Trembling took hold of them there, pain, as of a woman in travail.
Rawar jiki ya kama su a can, zafi kamar na mace mai naƙuda.
7 With the east wind, you break the ships of Tarshish.
Ka hallaka su kamar jiragen ruwan Tarshish da iskar gabas ta wargaje.
8 As we have heard, so we have seen, in the city of the LORD of Hosts, in the city of our God. God will establish it forever. (Selah)
Yadda muka ji, haka muka gani a cikin birnin Ubangiji Maɗaukaki, a cikin birnin Allahnmu. Allah ya sa ta zauna lafiya har abada. (Sela)
9 We have thought about your loving kindness, God, in the middle of your temple.
Cikin haikalinka, ya Allah, mun yi tunani a kan ƙaunarka marar ƙarewa.
10 As is your name, God, so is your praise to the ends of the earth. Your right hand is full of righteousness.
Kamar sunanka, ya Allah, yabonka ya kai iyakokin duniya; hannunka na dama ya cika da adalci.
11 Let Mount Zion be glad! Let the daughters of Judah rejoice because of your judgements.
Dutsen Sihiyona ya yi farin ciki, ƙauyukan Yahuda suna murna saboda hukuntanka.
12 Walk about Zion, and go around her. Number its towers.
Yi tafiya cikin Sihiyona, ku kewaye ta, ku ƙirga hasumiyoyinta,
13 Notice her bulwarks. Consider her palaces, that you may tell it to the next generation.
ku lura da katangarta da kyau, ku dubi fadodinta, don ku faɗe su ga tsara mai zuwa.
14 For this God is our God forever and ever. He will be our guide even to death.
Gama wannan Allah shi ne Allahnmu har abada abadin; zai zama jagorarmu har zuwa ƙarshe.

< Psalms 48 >