< Psalms 139 >

1 For the Chief Musician. A Psalm by David. LORD, you have searched me, and you know me.
Don mai bi da kaɗe-kaɗe. Ta Dawuda. Zabura ce. Ya Ubangiji, ka bincike ni ka kuwa san ni.
2 You know my sitting down and my rising up. You perceive my thoughts from afar.
Ka san sa’ad da na zauna da sa’ad da na tashi; ka san tunanina daga nesa.
3 You search out my path and my lying down, and are acquainted with all my ways.
Ka san fitata da kuma kwanciyata; ka saba da dukan hanyoyina.
4 For there is not a word on my tongue, but behold, LORD, you know it altogether.
Kafin in yi magana da harshena ka santa gaba ɗaya, ya Ubangiji.
5 You hem me in behind and before. You laid your hand on me.
Ka kewaye ni, gaba da baya; ka sa hannunka a kaina.
6 This knowledge is beyond me. It’s lofty. I can’t attain it.
Irin wannan sanin game da ni ya fi ƙarfin magana, ya fi ƙarfi in gane.
7 Where could I go from your Spirit? Or where could I flee from your presence?
Ina zan tafi daga Ruhunka? Ina zan gudu in tafi daga gabanka?
8 If I ascend up into heaven, you are there. If I make my bed in Sheol, behold, you are there! (Sheol h7585)
In na haura zuwa sammai, kana a can; in na yi gado a zurfafa, kana a can. (Sheol h7585)
9 If I take the wings of the dawn, and settle in the uttermost parts of the sea,
In na tashi a fikafikan safiya, in na sauka a gefe mai nisa na teku,
10 even there your hand will lead me, and your right hand will hold me.
can ma hannunka zai bishe ni, hannunka na dama zai riƙe ni gam.
11 If I say, “Surely the darkness will overwhelm me. The light around me will be night,”
In na ce, “Tabbatacce duhu zai ɓoye ni haske kuma zai zama dare kewaye da ni,”
12 even the darkness doesn’t hide from you, but the night shines as the day. The darkness is like light to you.
duhu ma ba zai zama duhu gare ka ba; dare zai haskaka kamar rana, gama duhu ya yi kamar haske gare ka.
13 For you formed my inmost being. You knit me together in my mother’s womb.
Gama ka halicci ciki-cikina; ka gina ni gaba ɗaya a cikin mahaifar mahaifiyata.
14 I will give thanks to you, for I am fearfully and wonderfully made. Your works are wonderful. My soul knows that very well.
Ina yabonka domin yadda ka yi ni abin tsoro ne da kuma abin mamaki; ayyukanka suna da banmamaki, na san da haka sosai.
15 My frame wasn’t hidden from you, when I was made in secret, woven together in the depths of the earth.
Ƙasusuwana ba a ɓoye suke a gare ka ba sa’ad da aka yi ni asirce. Sa’ad da saƙa ni gaba ɗaya a zurfafan duniya.
16 Your eyes saw my body. In your book they were all written, the days that were ordained for me, when as yet there were none of them.
Idanunka sun ga jikina marar fasali; dukan kwanakin da aka tsara mini a rubuce suke a littafinka kafin ɗayansu yă kasance.
17 How precious to me are your thoughts, God! How vast is their sum!
Tunaninka suna da daraja gare ni, ya Allah! Yawansu ba su da iyaka!
18 If I would count them, they are more in number than the sand. When I wake up, I am still with you.
A ce zan iya ƙirgansu, za su fi yashin teku yawa. Sa’ad da na farka, ina nan tare da kai har yanzu.
19 If only you, God, would kill the wicked. Get away from me, you bloodthirsty men!
Da kawai za ka kashe mugaye, ya Allah! Ku rabu da ni, ku masu kisankai!
20 For they speak against you wickedly. Your enemies take your name in vain.
Suna magana game da kai da mugun nufi; maƙiyanka suna ɗaukan sunanka a banza.
21 LORD, don’t I hate those who hate you? Am I not grieved with those who rise up against you?
Ba ina ƙin masu ƙinka ba, ya Ubangiji, ina kuma ƙyamar waɗanda suke tayar maka ba?
22 I hate them with perfect hatred. They have become my enemies.
Ba ni da wani abu da nake musu sai kiyaye kawai; na ɗauke su abokan gābana.
23 Search me, God, and know my heart. Try me, and know my thoughts.
Ka bincike ni, ya Allah ka kuma san zuciyata; ka gwada ni ka kuma san damuwata.
24 See if there is any wicked way in me, and lead me in the everlasting way.
Duba ko akwai wani laifi a cikina, ka bishe ni a madawwamiyar hanya.

< Psalms 139 >