< Psalms 122 >

1 A Song of Ascents. By David. I was glad when they said to me, “Let’s go to the LORD’s house!”
Waƙar haurawa. Ta Dawuda. Na yi farin ciki tare da waɗanda suka ce da ni, “Bari mu tafi gidan Ubangiji.”
2 Our feet are standing within your gates, Jerusalem!
Ƙafafunmu suna tsaye a ƙofofinki, ya Urushalima.
3 Jerusalem is built as a city that is compact together,
An gina Urushalima kamar birnin da aka yi a harhaɗe wuri guda.
4 where the tribes go up, even the LORD’s tribes, according to an ordinance for Israel, to give thanks to the LORD’s name.
A can ne kabilu suke haurawa, kabilan Ubangiji, don su yabi sunan Ubangiji bisa ga farillan da aka ba wa Isra’ila.
5 For there are set thrones for judgement, the thrones of David’s house.
A can kursiyoyin shari’a yake tsaye, kursiyoyin gidan Dawuda.
6 Pray for the peace of Jerusalem. Those who love you will prosper.
Ku yi addu’a don salamar Urushalima, “Bari waɗanda suke ƙaunarki su zauna lafiya.
7 Peace be within your walls, and prosperity within your palaces.
Bari salama ta kasance a katangarki zaman lafiya kuma a fadodinki.”
8 For my brothers’ and companions’ sakes, I will now say, “Peace be within you.”
Saboda’yan’uwana da kuma abokaina, zan ce, “Salama tă kasance tare da ke.”
9 For the sake of the house of the LORD our God, I will seek your good.
Saboda gidan Ubangiji Allahnmu, zan nemi wadatarki.

< Psalms 122 >