< Matthew 28 >

1 Now after the Sabbath, as it began to dawn on the first day of the week, Miriam Magdalene and the other Miriam came to see the tomb.
Bayan ranar Asabbaci, da sassafe, a ranar farko ta mako, Maryamu Magdalin tare da ɗaya Maryamun, suka je don su ga kabarin.
2 Behold, there was a great earthquake, for an angel of the Lord descended from the sky and came and rolled away the stone from the door and sat on it.
Sai aka yi wata babbar girgizar ƙasa. Don wani mala’ikan Ubangiji ya sauka daga sama, ya je kabarin, ya gungurar da dutsen, ya kuma zauna a kai.
3 His appearance was like lightning, and his clothing white as snow.
Kamanninsa yana kama da walƙiya, tufafinsa kuma fari fat kamar dusan ƙanƙara.
4 For fear of him, the guards shook, and became like dead men.
Masu gadin kabarin kuma suka ji tsoro ƙwarai, suka yi rawan jiki, suka zama kamar matattu.
5 The angel answered the women, “Don’t be afraid, for I know that you seek Yeshua, who has been crucified.
Mala’ikan ya ce wa matan, “Kada ku ji tsoro, domin na san cewa kuna neman Yesu wanda aka gicciye ne.
6 He is not here, for he has risen, just like he said. Come, see the place where the Lord was lying.
Ai, ba ya nan, ya tashi kamar yadda ya faɗa. Ku zo ku ga inda ya kwanta.
7 Go quickly and tell his disciples, ‘He has risen from the dead, and behold, he goes before you into Galilee; there you will see him.’ Behold, I have told you.”
Sai ku tafi da sauri ku gaya wa almajiransa cewa, ‘Ya tashi daga matattu, ya kuma ya sha gabanku zuwa Galili. Can za ku gan shi.’ Ga shi na faɗa muku.”
8 They departed quickly from the tomb with fear and great joy, and ran to bring his disciples word.
Sai matan suka bar kabarin da hanzari, da tsoro, sai dai cike da farin ciki, suka tafi a guje don su gaya wa almajiransa.
9 As they went to tell his disciples, behold, Yeshua met them, saying, “Rejoice!” They came and took hold of his feet, and worshipped him.
Kwaram, sai ga Yesu ya gamu da su ya ce, “Gaisuwa.” Sai suka zo kusa da shi, suka rungumi ƙafafunsa, suka yi masa sujada.
10 Then Yeshua said to them, “Don’t be afraid. Go tell my brothers that they should go into Galilee, and there they will see me.”
Sai Yesu ya ce musu, “Kada ku ji tsoro, ku tafi ku gaya wa’yan’uwana, su tafi Galili. A can za su gan ni.”
11 Now while they were going, behold, some of the guards came into the city and told the chief priests all the things that had happened.
Yayinda matan nan suna cikin tafiya, sai waɗansu daga cikin masu gadin suka shiga gari, suka ba wa manyan firistoci labarin duk abin da ya faru.
12 When they were assembled with the elders and had taken counsel, they gave a large amount of silver to the soldiers,
Da manyan firistoci da dattawa suka taru, sai suka ƙulla wata dabara, suka ba wa sojojin kuɗi mai yawa.
13 saying, “Say that his disciples came by night and stole him away while we slept.
Suka ce musu, “Ku, za ku ce, ‘Almajiransa ne sun zo da dare suka sace shi, lokacin da muke barci.’
14 If this comes to the governor’s ears, we will persuade him and make you free of worry.”
In wannan labari ya kai kunnen gwamna, za mu lallashe shi, mu kuma kāre ku daga duk wata wahala.”
15 So they took the money and did as they were told. This saying was spread abroad amongst the Judeans, and continues until today.
Sai sojojin suka karɓi kuɗin, suka kuma yi kamar yadda aka umarce su. Wannan labarin kuwa shi ne ake bazawa ko’ina a cikin Yahudawa, har yă zuwa yau.
16 But the eleven disciples went into Galilee, to the mountain where Yeshua had sent them.
Sa’an nan almajiransa goma sha ɗaya, suka tafi Galili, suka je dutsen da Yesu ya gaya musu.
17 When they saw him, they bowed down to him; but some doubted.
Da suka gan shi, sai suka yi masa sujada, amma waɗansu suka yi shakka.
18 Yeshua came to them and spoke to them, saying, “All authority has been given to me in heaven and on earth.
Sai Yesu ya zo wurinsu ya ce, “An ba ni dukan iko a sama da kuma ƙasa.
19 Go and make disciples of all nations, immersing them in the name of the Father and of the Son and of the Holy Spirit,
Saboda haka ku tafi, ku mai da dukan al’umman duniya su zama almajiraina, kuna yi musu baftisma a cikinsunan Uba, da na Ɗa, da na Ruhu Mai Tsarki,
20 teaching them to observe all things that I commanded you. Behold, I am with you always, even to the end of the age.” Amen. (aiōn g165)
kuna kuma koya musu, su yi biyayya da duk abin da na umarce ku, kuma tabbatacce, ina tare da ku kullum, har ƙarshen zamani.” (aiōn g165)

< Matthew 28 >