< Mark 16 >

1 When the Sabbath was past, Miriam Magdalene, and Miriam the mother of Jacob, and Shalom bought spices, that they might come and anoint him.
Bayan ranar assabaci, Maryamu Magadaliya da Maryamu uwar Yakubu da Salomi, suka sayo man shafawa mai kamshi domin shafe jikin Yesu saboda jana'iza.
2 Very early on the first day of the week, they came to the tomb when the sun had risen.
Da safiyar ranar farko ta mako sai suka tafi kabarin a dai dai fitowar rana.
3 They were saying amongst themselves, “Who will roll away the stone from the door of the tomb for us?”
Suna magana a tsakaninsu suna cewa, wanene zai gangarar da dutsen da aka rufe bakin kabarin da shi?”
4 for it was very big. Looking up, they saw that the stone was rolled back.
Da suka daga ido, sai suka ga an riga an gangarar da dutsen, domin yana da girma.
5 Entering into the tomb, they saw a young man sitting on the right side, dressed in a white robe; and they were amazed.
Da suka shiga cikin kabarin sai ga wani saurayi saye da farar tufa, yana zaune a hannun dama, suna mamaki.
6 He said to them, “Don’t be amazed. You seek Yeshua, the Nazarene, who has been crucified. He has risen! He is not here. See the place where they laid him!
Sai ya ce masu, “Kada ku ji tsoro. Kuna neman Yesu banazare, wanda aka giciye. Ya tashi! Baya nan. Ku duba wurin da aka kwantar dashi.
7 But go, tell his disciples and Peter, ‘He goes before you into Galilee. There you will see him, as he said to you.’”
Sai ku je, ku gaya wa almajiransa da Bitrus cewa ya rigaya ya yi gabanku zuwa Galili. A can zaku ganshi, kamar yadda ya fada maku.”
8 They went out, and fled from the tomb, for trembling and astonishment had come on them. They said nothing to anyone; for they were afraid.
Suka fita daga cikin kabarin da gudu suna rawar jiki da mamaki, ba su cewa kowa komai ba domin suna jin tsoro.
9 (note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) Now when he had risen early on the first day of the week, he appeared first to Miriam Magdalene, from whom he had cast out seven demons.
(note: The most reliable and earliest manuscripts do not include Mark 16:9-20.) Da safiyar ranar farko ta mako ya fara bayyana kansa ga Maryamu Magadaliya wadda ya kori aljannu guda bakwai daga cikinta.
10 She went and told those who had been with him, as they mourned and wept.
Sai ta tafi ta shaida wadanda suke tare da shi suke makoki da kuka.
11 When they heard that he was alive and had been seen by her, they disbelieved.
Sai suka ji cewa ya tashi kuma ta ganshi, amma basu gaskata ba.
12 After these things he was revealed in another form to two of them as they walked, on their way into the country.
Bayan wadannan al'amura ya bayana kansa ta wata siffa ga mutum biyu sa'ilin da suke tafiya akan hanya.
13 They went away and told it to the rest. They didn’t believe them, either.
Sai suka tafi suka gaya wa sauran almajiransa, duk da haka basu gaskata ba.
14 Afterward he was revealed to the Eleven themselves as they sat at the table; and he rebuked them for their unbelief and hardness of heart, because they didn’t believe those who had seen him after he had risen.
Bayan wani lokaci, Yesu ya bayyana kansa ga almajiransa su goma sha daya, ya tsauta masu saboda rashin gaskatawa da taurin zuciya, bayansun ji daga wadanda suka ganshi bayan ya tashi daga matattu.
15 He said to them, “Go into all the world and proclaim the Good News to the whole creation.
Sai ya umarcesu cewa “Ku tafi cikin duniya ku yi bishara ga dukan halitta.
16 He who believes and is immersed will be saved; but he who disbelieves will be condemned.
Wanda ya ba da gaskiya aka kuma yi masa baftisma, zaya sami ceto, wanda baya bada gaskiya ba za ya hallaka.
17 These signs will accompany those who believe: in my name they will cast out demons; they will speak with new languages;
Wadannan alamu za su kasance da wadanda suka gaskata; a cikin sunana, za su fidda aljannu, za su yi magana da sabbin harsuna.
18 they will take up serpents; and if they drink any deadly thing, it will in no way hurt them; they will lay hands on the sick, and they will recover.”
Za su dauki macizai da hannayesu, idan sun sha guba ba ta cutar dasu ba, za su dibiya hannayensu ga marasa lafiya, za su sami warkaswa.”
19 So then the Lord, after he had spoken to them, was received up into heaven and sat down at the right hand of God.
Bayan Ubangiji ya gama magana da su, sai aka dauke shi zuwa sama in da zai zauna a hannun dama na Allah.
20 They went out and preached everywhere, the Lord working with them and confirming the word by the signs that followed. Amen.
Almajiransa kuma suka tafi ko'ina suna sheilar bishara. Ubangiji kuma yayi aiki tare da su, yana tabbatar da kalma ta wurin ayukan al'ajiba tare da su.

< Mark 16 >