< Mark 15 >

1 Immediately in the morning the chief priests, with the elders, scribes, and the whole council, held a consultation, bound Yeshua, carried him away, and delivered him up to Pilate.
Da sassafe, sai manyan firistoci da dattawa, da malaman dokoki, da dukan Majalisa, suka yanke shawara. Suka daure Yesu, suka kai shi, suka miƙa shi ga Bilatus.
2 Pilate asked him, “Are you the King of the Jews?” He answered, “So you say.”
Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kai ne Sarkin Yahudawa?” Yesu ya amsa ya ce, “I, haka yake, kamar yadda ka faɗa.”
3 The chief priests accused him of many things.
Manyan firistoci suka zarge shi a kan abubuwa da yawa.
4 Pilate again asked him, “Have you no answer? See how many things they testify against you!”
Don haka Bilatus ya sāke tambayarsa ya ce, “Ba za ka amsa ba? Dubi abubuwa da yawa da suke zarginka da su.”
5 But Yeshua made no further answer, so that Pilate marvelled.
Amma har yanzu, Yesu bai ba da amsa ba, Bilatus ya yi mamaki.
6 Now at the feast he used to release to them one prisoner, whomever they asked of him.
Yanzu fa, al’ada ce a lokacin Bikin, a saki ɗan kurkuku guda wanda mutane suka roƙa.
7 There was one called Barabbas, bound with his fellow insurgents, men who in the insurrection had committed murder.
Wani mutumin da ake kira Barabbas, yana a kurkuku, tare da waɗansu’yan tawaye da suka yi kisankai a lokacin wani hargitsi.
8 The multitude, crying aloud, began to ask him to do as he always did for them.
Taron suka matso, suka ce roƙi Bilatus yă yi musu abin da ya saba yi.
9 Pilate answered them, saying, “Do you want me to release to you the King of the Jews?”
Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Kuna so in sakar muku Sarkin Yahudawa?”
10 For he perceived that for envy the chief priests had delivered him up.
Don ya san saboda sonkai ne manyan firistoci suka ba da Yesu a gare shi.
11 But the chief priests stirred up the multitude, that he should release Barabbas to them instead.
Amma manyan firistoci suka zuga taron su sa a saki Barabbas, a maimakon Yesu.
12 Pilate again asked them, “What then should I do to him whom you call the King of the Jews?”
Bilatus ya tambaye su ya ce, “To, me zan yi da wanda kuke ce da shi, sarkin Yahudawa?”
13 They cried out again, “Crucify him!”
Suka yi ihu, suka ce, “A gicciye shi!”
14 Pilate said to them, “Why, what evil has he done?” But they cried out exceedingly, “Crucify him!”
Bilatus ya yi tambaya ya ce, “Don me? Wane laifi ya yi?” Amma suka ƙara yin ihu suna cewa, “A gicciye shi!”
15 Pilate, wishing to please the multitude, released Barabbas to them, and handed over Yeshua, when he had flogged him, to be crucified.
Don son yă faranta wa taron rai, sai Bilatus ya sakar musu Barabbas. Ya sa aka yi wa Yesu bulala, sa’an nan ya ba da shi a gicciye.
16 The soldiers led him away within the court, which is the Praetorium; and they called together the whole cohort.
Sojojin suka tafi da Yesu cikin fadar gwamna (wato, Firetoriyum), suka kira dukan kamfanin sojoji wuri ɗaya.
17 They clothed him with purple; and weaving a crown of thorns, they put it on him.
Suka sa masa wata riga mai ruwan shunayya, suka kuma tuƙa rawanin ƙaya suka sa masa.
18 They began to salute him, “Hail, King of the Jews!”
Sai suka fara ce masa, “Ranka yă daɗe sarkin Yahudawa!”
19 They struck his head with a reed and spat on him, and bowing their knees, did homage to him.
Suka dinga bugunsa a kā da sanda, suka tattofa masa miyau. Suka durƙusa suka yi masa bangirma na ba’a.
20 When they had mocked him, they took the purple cloak off him, and put his own garments on him. They led him out to crucify him.
Bayan da suka gama yin masa ba’a, suka tuɓe rigar mai ruwan shunayyar, suka sa masa nasa tufafi. Sai suka tafi da shi don a gicciye shi.
21 They compelled one passing by, coming from the country, Simon of Cyrene, the father of Alexander and Rufus, to go with them that he might bear his cross.
Sai ga wani mutum daga Sairin da ake kira Siman, mahaifin Alekzanda da Rufus, yana wucewa kan hanyarsa daga ƙauye. Sai suka tilasta shi yă ɗauki gicciyen.
22 They brought him to the place called Golgotha, which is, being interpreted, “The place of a skull.”
Suka kawo Yesu a wurin da ake kira Golgota (wanda yake nufin Wurin Ƙoƙon Kai).
23 They offered him wine mixed with myrrh to drink, but he didn’t take it.
Sai suka miƙa masa ruwan inabi gauraye da mur, don yă rage zafi, amma bai sha ba.
24 Crucifying him, they parted his garments amongst them, casting lots on them, what each should take.
Sai suka gicciye shi. Suka rarraba tufafinsa, suka jefa ƙuri’a a kansu don su ga abin da kowa zai samu.
25 It was the third hour when they crucified him.
Sa’a ta uku na safe ce kuwa aka gicciye shi.
26 The superscription of his accusation was written over him: “THE KING OF THE JEWS.”
Akwai rubutu na zarginsa, da ya ce, Sarkin Yahudawa.
27 With him they crucified two robbers, one on his right hand, and one on his left.
Suka gicciye’yan fashi biyu tare da shi, ɗaya a damansa, ɗayan kuma a hagunsa.
28 The Scripture was fulfilled which says, “He was counted with transgressors.”
29 Those who passed by blasphemed him, wagging their heads and saying, “Ha! You who destroy the temple and build it in three days,
Masu wucewa suka zazzage shi. Suka kaɗa kai suna cewa, “To, kai da za ka rushe haikali ka kuma gina shi a kwana uku,
30 save yourself, and come down from the cross!”
sai ka sauko daga gicciyen, ka ceci kanka!”
31 Likewise, also the chief priests mocking amongst themselves with the scribes said, “He saved others. He can’t save himself.
Haka kuma, manyan firistoci da malaman dokoki suka yi masa ba’a a junansu, suna cewa, “Ya ceci waɗansu, amma ya kāsa ceton kansa!
32 Let the Messiah, the King of Israel, now come down from the cross, that we may see and believe him.” Those who were crucified with him also insulted him.
Bari wannan Kiristi, wannan Sarkin Isra’ila, yă sauko yanzu daga gicciye, don mu ga mu kuma gaskata.” Waɗanda aka gicciye tare da shi ma suka zazzage shi.
33 When the sixth hour had come, there was darkness over the whole land until the ninth hour.
Daga sa’a ta shida har zuwa sa’a ta tara na rana, duhu ya rufe dukan ƙasar.
34 At the ninth hour Yeshua cried with a loud voice, saying, “Eloi, Eloi, lama sabachthani?” which is, being interpreted, “My God, my God, why have you forsaken me?”
A daidai sa’a ta tara na rana, sai Yesu ya ɗaga murya da ƙarfi ya ce, “Eloi, Eloi, lama sabaktani?” (Wato, “Ya Allahna, ya Allahna, don me ka yashe ni?”).
35 Some of those who stood by, when they heard it, said, “Behold, he is calling Elijah.”
Da waɗansu cikin waɗanda suke tsattsaye kusa da wurin suka ji haka, suka ce, “Ku saurara, yana kiran Iliya.”
36 One ran, and filling a sponge full of vinegar, put it on a reed and gave it to him to drink, saying, “Let him be. Let’s see whether Elijah comes to take him down.”
Wani mutum ya ruga ya je ya jiƙo soso da ruwan tsami, ya soka a sanda ya miƙa wa Yesu yă sha. Ya ce, “Ku ƙyale shi. Bari mu ga ko Iliya zai zo yă saukar da shi.”
37 Yeshua cried out with a loud voice, and gave up the spirit.
Da murya mai ƙarfi, Yesu ya ja numfashinsa na ƙarshe.
38 The veil of the temple was torn in two from the top to the bottom.
Labulen haikali kuwa ya yage kashi biyu, daga sama har ƙasa.
39 When the centurion, who stood by opposite him, saw that he cried out like this and breathed his last, he said, “Truly this man was the Son of God!”
Da jarumin da yake tsaye a gaban Yesu ya ji muryarsa, ya kuma ga yadda ya mutu, sai ya ce, “Gaskiya, wannan mutum Ɗan Allah ne!”
40 There were also women watching from afar, amongst whom were both Miriam Magdalene and Miriam the mother of Jacob the less and of Yosi, and Shalom;
Waɗansu mata suna kallo daga nesa. A cikinsu kuwa akwai Maryamu Magdalin, Maryamu mahaifiyar Yaƙub ƙarami da Yusuf, da kuma Salome.
41 who, when he was in Galilee, followed him and served him; and many other women who came up with him to Jerusalem.
A Galili waɗannan mata ne suka riƙa bin sa suna yin masa hidima. Waɗansu mata da yawa da suka zo tare da shi daga Urushalima, su ma suna nan a can.
42 When evening had now come, because it was the Preparation Day, that is, the day before the Sabbath,
Ranar kuwa ita ce ranar Shirye-shirye (wato, ana kashegari Asabbaci). Saboda haka, da yamma ta yi, sai
43 Joseph of Arimathaea, a prominent council member who also himself was looking for God’s Kingdom, came. He boldly went in to Pilate, and asked for Yeshua’s body.
Yusuf daga Arimateya, wani sanannen ɗan Majalisa, wanda dā ma yake jiran zuwan mulkin Allah, ya je wajen Bilatus ba tsoro, ya roƙa a ba shi jikin Yesu.
44 Pilate was surprised to hear that he was already dead; and summoning the centurion, he asked him whether he had been dead long.
Bilatus ya yi mamaki da ya ji cewa Yesu ya riga ya mutu. Sai ya kira jarumin ya tambaye shi ko Yesu ya riga ya mutu.
45 When he found out from the centurion, he granted the body to Joseph.
Da ya ji ta bakin jarumin cewa haka ne, sai ya ba wa Yusuf jikin.
46 He bought a linen cloth, and taking him down, wound him in the linen cloth and laid him in a tomb which had been cut out of a rock. He rolled a stone against the door of the tomb.
Sai Yusuf ya kawo zanen lilin, ya saukar da jikin, ya nannaɗe shi da lilin ɗin, sa’an nan ya sa shi a kabarin da aka fafe a cikin dutse. Sai ya gungura wani dutse ya rufe bakin kabarin.
47 Miriam Magdalene and Miriam the mother of Yosi, saw where he was laid.
Maryamu Magdalin da Maryamu uwar Yusuf sun ga inda aka kwantar da shi.

< Mark 15 >