< Luke 4 >

1 Yeshua, full of the Holy Spirit, returned from the Jordan and was led by the Spirit into the wilderness
Sai Yesu, cike da Ruhu Mai Tsarki, ya dawo daga kogin Urdun, sai Ruhu Mai Tsarki ya bishe shi zuwa cikin jeji
2 for forty days, being tempted by the devil. He ate nothing in those days. Afterward, when they were completed, he was hungry.
kwana arba'in, shaidan kuma ya jarabce shi. A kwanakin nan, bai ci abinci ba, kuma yunwa ta kama shi bayan karshen lokacin.
3 The devil said to him, “If you are the Son of God, command this stone to become bread.”
Shaidan ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka umarci wannan dutse ya zama gurasa.”
4 Yeshua answered him, saying, “It is written, ‘Man shall not live by bread alone, but by every word of God.’”
Yesu ya amsa masa, “A rubuce yake, 'Ba da gurasa kadai Mutum zai rayu ba.'”
5 The devil, leading him up on a high mountain, showed him all the kingdoms of the world in a moment of time.
Sai shaidan ya kai shi zuwa wani tudu mai tsawo, ya kuma nuna masa dukan mulkokin duniyan nan a dan lokaci.
6 The devil said to him, “I will give you all this authority and their glory, for it has been delivered to me, and I give it to whomever I want.
Shaidan ya ce masa, “Zan ba ka iko ka yi mulkin dukan wadannan, da dukan daukakarsu. Zan yi haka domin an ba ni su duka in yi mulkinsu, kuma ina da yanci in ba dukan wanda na ga dama.
7 If you therefore will worship before me, it will all be yours.”
Saboda da haka, idan ka rusuna ka yi mani sujada, dukansu za su zama naka.”
8 Yeshua answered him, “Get behind me, Satan! For it is written, ‘You shall worship the Lord your God, and you shall serve him only.’”
Amma Yesu ya amsa ya ce masa, “A rubuce yake, 'Dole ne Ubangiji Allahnka za ka yi wa sujada, shi kadai kuma za ka bauta wa.”
9 He led him to Jerusalem and set him on the pinnacle of the temple, and said to him, “If you are the Son of God, cast yourself down from here,
Sai shaidan ya kai Yesu Urushalima, ya tsayadda shi a bisan kololuwar haikali, kuma ya ce masa, “Idan kai Dan Allah ne, ka jefas da kanka kasa daga nan.
10 for it is written, ‘He will put his angels in charge of you, to guard you;’
Domin a rubuce yake, 'Zai ba mala'ikunsa umarni su kiyaye ka, su kuma tsare ka,'
11 and, ‘On their hands they will bear you up, lest perhaps you dash your foot against a stone.’”
kuma, 'Za su daga ka sama a hannunsu, don kada ka yi tuntube a kan dutse.”
12 Yeshua answering, said to him, “It has been said, ‘You shall not tempt the Lord your God.’”
Yesu ya amsa masa cewa, “An fadi, 'Kada ka gwada Ubangiji Allahnka.'”
13 When the devil had completed every temptation, he departed from him until another time.
Da shaidan ya gama yi wa Yesu gwaji, sai ya kyale shi sai wani lokaci.
14 Yeshua returned in the power of the Spirit into Galilee, and news about him spread through all the surrounding area.
Sai Yesu ya koma Galili cike da ikon Ruhu, kuma labarinsa ya bazu cikin dukan wuraren dake wannan yankin.
15 He taught in their synagogues, being glorified by all.
Ya yi ta koyarwa a cikin majami'unsu, sai kowa na ta yabon sa.
16 He came to Nazareth, where he had been brought up. He entered, as was his custom, into the synagogue on the Sabbath day, and stood up to read.
Wata rana ya zo Nazarat, birnin da aka rene shi. Kamar yadda ya saba yi, ya shiga cikin majami'a a nan ranar Asabaci, ya kuma tashi tsaye domin ya karanta Nassi.
17 The scroll of the prophet Isaiah was handed to him. He opened the scroll, and found the place where it was written,
An mika masa littafin anabi Ishaya, ya bude littafin ya kuma ga inda an rubuta,
18 “The Spirit of the Lord is on me, because he has anointed me to proclaim good news to the poor. He has sent me to heal the broken hearted, to proclaim release to the captives, recovering of sight to the blind, to deliver those who are crushed,
“Ruhun Ubangiji yana kai na, domin ya shafe ni in yi wa'azin Bishara ga matalauta. Ya aike ni in yi shelar yanci ga daurarru, da kuma budewar idanu ga makafi, in 'yantar da wadanda su ke cikin kunci,
19 and to proclaim the acceptable year of the Lord.”
in kuma yi shelar shekarar tagomashi na Ubangiji.”
20 He closed the scroll, gave it back to the shammash, and sat down. The eyes of all in the synagogue were fastened on him.
Sai ya rufe littafin, ya mai da shi ga ma'aikacin majami'ar, sai ya zauna. Dukan wadanda suke cikin majami'ar suka zura Idanuwansu a kansa.
21 He began to tell them, “Today, this Scripture has been fulfilled in your hearing.”
Sai ya fara masu magana, “Yau wannan Nassi ya cika a kunuwanku.”
22 All testified about him and wondered at the gracious words which proceeded out of his mouth; and they said, “Isn’t this Joseph’s son?”
Dukan wadanda ke wurin sun shaida abin da ya fadi kuma dukansu sun yi ta mamakin kalmomin alheri da suke fitowa daga bakinsa. Suna cewa, “Wannan ai dan Yusufu ne kawai, ko ba haka ba?”
23 He said to them, “Doubtless you will tell me this proverb, ‘Physician, heal yourself! Whatever we have heard done at Capernaum, do also here in your hometown.’”
Yesu ya ce masu, “Lallai za ku fada mani wannan karin magana, 'Likita, ka warkar da kanka. Duk abin da mun ji wai ka yi a Kafarnahum, ka yi shi a nan garinka ma.'”
24 He said, “Most certainly I tell you, no prophet is acceptable in his hometown.
Ya sake cewa, “Hakika na fada maku, annabi baya samun karbuwa a garinsa.
25 But truly I tell you, there were many widows in Israel in the days of Elijah, when the sky was shut up three years and six months, when a great famine came over all the land.
Amma na gaya maku gaskiya akwai gwauraye da yawa cikin Isra'ila a zamanin Iliya, lokacin da an rufe sammai shekaru uku da rabi babu ruwa, lokacin da anyi gagarumar yunwa a duk fadin kasar.
26 Elijah was sent to none of them, except to Zarephath, in the land of Sidon, to a woman who was a widow.
Amma ba a aiki Iliya zuwa wurin waninsu ba, sai wurin gwauruwa da ke a Zarifat can kusa da Sidon.
27 There were many lepers in Israel in the time of Elisha the prophet, yet not one of them was cleansed, except Naaman, the Syrian.”
Akwai kutare da yawa kuma a Isa'ila a zamanin anabi Elisha, amma babu wanda aka warkar sai dai Na'aman mutumin Suriya kadai.
28 They were all filled with wrath in the synagogue as they heard these things.
Dukan mutanen da ke cikin majami'a suka fusata kwarai sa'adda suka ji wadannan zantattuka.
29 They rose up, threw him out of the city, and led him to the brow of the hill that their city was built on, that they might throw him off the cliff.
Suka tashi suka tura shi zuwa wajen birnin, suka kai shi bakin dutsen da aka gina garinsu a kai dominsu jefar da shi kasa.
30 But he, passing through the middle of them, went his way.
Amma ya ratsa tsakaninsu ya yi gabansa.
31 He came down to Capernaum, a city of Galilee. He was teaching them on the Sabbath day,
Sannan ya gangara zuwa Kafarnahum, wani birni a Galili. Wata Asabaci yana koya wa mutane a cikin majami'a.
32 and they were astonished at his teaching, for his word was with authority.
Sun yi mamaki kwarai da koyarwan sa, domin maganarsa na da iko.
33 In the synagogue there was a man who had a spirit of an unclean demon; and he cried out with a loud voice,
A wannan lokacin akwai wani mutum a cikin majami'a mai kazamin ruhu, sai ya yi kara da babbar murya,
34 saying, “Ah! what have we to do with you, Yeshua of Nazareth? Have you come to destroy us? I know who you are: the Holy One of God!”
“Ina ruwan mu da kai, Yesu Banazarat? Ka zo domin ka hallaka mu ne? Na san ko kai wanene! Kai ne Mai Tsarki na Allah!”
35 Yeshua rebuked him, saying, “Be silent and come out of him!” When the demon had thrown him down in the middle of them, he came out of him, having done him no harm.
Yesu ya tsauta wa aljanin yana cewa, “Yi shiru ka fita daga cikinsa!” Da aljanin ya jefar da mutumin kasa a tsakiyarsu, ya fita daga cikinsa ba tare da yi masa rauni ba.
36 Amazement came on all and they spoke together, one with another, saying, “What is this word? For with authority and power he commands the unclean spirits, and they come out!”
Dukan mutanen suka yi mamaki, kuma suna ta zancen wannan abu a tsakaninsu. Sun ce, “Wanda irin maganganu kenan? Ya umarce kazaman ruhohin da karfi da iko kuma sun fita.”
37 News about him went out into every place of the surrounding region.
Saboda da haka, an fara yada labarinsa zuwa dukan kewayen yankin.
38 He rose up from the synagogue and entered into Simon’s house. Simon’s mother-in-law was afflicted with a great fever, and they begged him to help her.
Sai Yesu ya bar majami'ar ya shiga gidan Siman. A wannan lokacin, surukar Siman tana fama da zazzabi mai zafi, sai suka roke shi dominta.
39 He stood over her and rebuked the fever, and it left her. Immediately she rose up and served them.
Sai ya tsaya a kanta, ya tsautawa zazzabin, kuma ya rabu da ita. Nan take, ta tashi ta fara yi masu hidima.
40 When the sun was setting, all those who had any sick with various diseases brought them to him; and he laid his hands on every one of them, and healed them.
Da faduwar rana, mutane suka kawo wa Yesu dukan wadanda suke ciwo da cuttuttuka dabam dabam. Ya dora masu hannuwansa ya warkar da su.
41 Demons also came out of many, crying out and saying, “You are the Messiah, the Son of God!” Rebuking them, he didn’t allow them to speak, because they knew that he was the Messiah.
Aljanu kuma sun fita daga wadasunsu da dama, suna kuka cewa, “Kai ne Dan Allah!” Yesu ya tsauta wa aljannun ya kuma hana su magana, domin sun sani cewa shine Almasihu.
42 When it was day, he departed and went into an uninhabited place and the multitudes looked for him, and came to him, and held on to him, so that he wouldn’t go away from them.
Da safiya ta yi, ya kebe kansa zuwa wani wurin da babu kowa. Jama'a da dama suna neman sa suka zo inda yake. Sun yi kokari su hana shi barin su.
43 But he said to them, “I must proclaim the good news of God’s Kingdom to the other cities also. For this reason I have been sent.”
Amma ya ce masu, “Dole in yi bisharar Allah a wasu birane da dama, domin dalilin da aka aiko ni nan kenan.”
44 He was proclaiming in the synagogues of Galilee.
Sai ya ci gaba da wa'azi cikin majami'u dukan fadin Yahudiya.

< Luke 4 >