< Yochanan 5 >

1 After these things, there was a Jewish festival, and Yeshua went up to Jerusalem.
Bayan haka akwai idi na yahudawa, kuma Yesu ya tafi Urashalima.
2 Now in Jerusalem by the sheep gate, there is a pool, which is called in Hebrew, “Bethesda”, having five porches.
To a cikin Urashilima kusa da kofar tumaki akwai tabki, wanda ake kira Baitasda da harshen Ibraniyanci, yana da shirayi biyar.
3 In these lay a great multitude of those who were sick, blind, lame, or paralysed, waiting for the moving of the water;
Taron mutane dayawa masu ciwo da, makafi da guragu da shanyayyu suna kwance a wurin [suna jira a dama ruwan].
4 for an angel went down at certain times into the pool and stirred up the water. Whoever stepped in first after the stirring of the water was healed of whatever disease he had.
Gama mala'ikan Ubangiji kan sabko a cikin tabkin ya dama ruwan, wanda ya fara taba ruwan sai ya warke komai cutar da yake da ita.
5 A certain man was there who had been sick for thirty-eight years.
Akwai wani mutum a bakin tabki yana kwance yana da rashin lafiya har shekara talatin da takwas.
6 When Yeshua saw him lying there, and knew that he had been sick for a long time, he asked him, “Do you want to be made well?”
Da Yesu ya gan shi yana kwance a wurin sai ya gane ya dade a wurin, sai ya ce masa, “Ko kana so ka warke?”
7 The sick man answered him, “Sir, I have no one to put me into the pool when the water is stirred up, but while I’m coming, another steps down before me.”
Sai mai rashin lafiyar ya amsa ya ce, “Malam, bani da kowa da zai sa ni a cikin tabkin idan ruwan ya motsa. Yayinda na ke kokari sai wani ya riga ni.”
8 Yeshua said to him, “Arise, take up your mat, and walk.”
Yesu ya ce masa,” Ka tashi ka dauki shimfidarka ka tafi.”
9 Immediately, the man was made well, and took up his mat and walked. Now that day was a Sabbath.
Nan dan nan Mutumin ya warke, ya dauki shimfidarsa ya tafi. Ranar kuwa Asabar ce.
10 So the Judeans said to him who was cured, “It is the Sabbath. It is not lawful for you to carry the mat.”
Sai Yahudawa suka ce da wanda aka warkar din, “Ai, Asabar ce, bai kuwa halatta ka dauki shimfidarka ba.”
11 He answered them, “He who made me well said to me, ‘Take up your mat and walk.’”
Sai ya amsa ya ce, “Ai wanda ya warkar da ni, shine ya ce mani 'Dauki shimfidarka, ka tafi.”
12 Then they asked him, “Who is the man who said to you, ‘Take up your mat and walk’?”
Suka tambaye shi, “wane mutum ne ya ce maka, 'Dauki shimfidar ka yi tafiya'?”
13 But he who was healed didn’t know who it was, for Yeshua had withdrawn, a crowd being in the place.
Sai dai, shi wanda aka warka din, ba san ko wanene ya warkar da shi ba, domin Yesu ya riga ya tafi aboye, saboda akwai taro a wurin.
14 Afterward Yeshua found him in the temple and said to him, “Behold, you are made well. Sin no more, so that nothing worse happens to you.”
Bayan haka, Yesu ya same shi a Haikalin, ya ce masa, “ka ga fa, ka warke. To, kada ka kara yin zunubi don kada wani abu da ya fi wannan muni ya same ka.”
15 The man went away, and told the Judeans that it was Yeshua who had made him well.
Sai mutumin ya tafi ya gaya wa Yahuduwa cewa Yesu ne ya warkar da shi.
16 For this cause the Judeans persecuted Yeshua and sought to kill him, because he did these things on the Sabbath.
To saboda haka Yahudawa suka fara tsanantawa Yesu, don ya yi wadannan abubuwa ran Asabar.
17 But Yeshua answered them, “My Father is still working, so I am working, too.”
Yesu kuwa ya amsa masu ya ce, “Ubana yana aiki har yanzu, ni ma ina aiki.”
18 For this cause therefore the Judeans sought all the more to kill him, because he not only broke the Sabbath, but also called God his own Father, making himself equal with God.
Saboda haka, Yahudawa suka kara nema su kashe shi ba don ya keta Asabar kadai ba, amma kuma domin ya ce Allah Ubansa ne, wato yana maida kansa dai-dai da Allah.
19 Yeshua therefore answered them, “Most certainly, I tell you, the Son can do nothing of himself, but what he sees the Father doing. For whatever things he does, these the Son also does likewise.
Yesu ya amsa masu ya ce, hakika hakika, ina gaya maku, Dan ba ya yin kome shi kadai, sai abin da ya ga Uba yana yi.
20 For the Father has affection for the Son, and shows him all things that he himself does. He will show him greater works than these, that you may marvel.
Domin Uban na kaunar Dan, yana kuma nuna masa dukan abinda shi da kansa yake yi, kuma zai nuna masa abubuwan da suka fi wadannan, domin ku yi mamaki.
21 For as the Father raises the dead and gives them life, even so the Son also gives life to whom he desires.
Gama kamar yadda Uba yakan tada matattu ya kuma basu rai, haka Dan ma yake bada rai ga duk wanda ya nufa.
22 For the Father judges no one, but he has given all judgement to the Son,
Gama Uban ba ya hukunta kowa, sai dai ya damka dukan hukunci ga Dan,
23 that all may honour the Son, even as they honour the Father. He who doesn’t honour the Son doesn’t honour the Father who sent him.
domin kowa ya girmama Dan, kamar yadda suke girmama Uban. Shi wanda ba ya girmama Dan, ba ya girmama Uban da ya aiko shi.
24 “Most certainly I tell you, he who hears my word and believes him who sent me has eternal life, and doesn’t come into judgement, but has passed out of death into life. (aiōnios g166)
Hakika, hakika, duk mai jin Maganata, yana kuma gaskata wanda ya aiko ni, yana da rai madawwami ba kuma za a kashe shi ba, domin ya ratse daga mutuwa zuwa rai. (aiōnios g166)
25 Most certainly I tell you, the hour comes, and now is, when the dead will hear the Son of God’s voice; and those who hear will live.
Hakika hakika, ina gaya maku, lokaci na zuwa, har ma ya yi da matattatu za su ji muryar Dan Allah, wadanda suka ji kuwa za su rayu.
26 For as the Father has life in himself, even so he gave to the Son also to have life in himself.
Kammar yada Uba ya ke da rai a cikinsa, haka ya ba Dan don ya zama da rai cikin kansa.
27 He also gave him authority to execute judgement, because he is a son of man.
Uban ya kuma ba Dan ikon zartar da hukunci, saboda shi ne Dan Mutum.
28 Don’t marvel at this, for the hour comes in which all who are in the tombs will hear his voice
Kada ku yi mamakin wannan, domin lokaci na zuwa da duk wadanda suke kaburbura za su ji muryarsa,
29 and will come out; those who have done good, to the resurrection of life; and those who have done evil, to the resurrection of judgement.
su kuma fito: wadanda suka aikata nagarta zawa tashi na rai, wadanda suka aikata mugunta kuwa zuwa tashi na hukunci.
30 I can of myself do nothing. As I hear, I judge; and my judgement is righteous, because I don’t seek my own will, but the will of my Father who sent me.
Ba na iya yin kome ni da kai na. Yadda na ke ji, haka nake yin hukunci, Hukunci na kuwa na adalci ne, domin ba nufin kaina nake bi ba, sai dai nufin wanda ya aiko ni.
31 “If I testify about myself, my witness is not valid.
Idan zan yi shaida game da kaina, shaidata baza ta zama gaskiya ba.
32 It is another who testifies about me. I know that the testimony which he testifies about me is true.
Akwai wani wanda ya ke bada shaida game da ni, na kuwa sani shaidar da yake bayarwa game da ni gaskiya ce.
33 You have sent to Yochanan, and he has testified to the truth.
Kun aika zuwa wurin Yahaya, shi kuma ya yi shaidar gaskiya.
34 But the testimony which I receive is not from man. However, I say these things that you may be saved.
Duk da haka shaidar da na karba bata mutum bace. Na fadi wadanan abubuwa domin ku sami ceto.
35 He was the burning and shining lamp, and you were willing to rejoice for a while in his light.
Yahaya fitila ne mai ci, mai haske ne kuma, kun yarda ku yi farinciki da haskensa dan lokaci kadan.
36 But the testimony which I have is greater than that of Yochanan; for the works which the Father gave me to accomplish, the very works that I do, testify about me, that the Father has sent me.
Amma shaidar da ni ke da ita ta fi ta Yahaya karfi. Domin ayyukan da Uba ya bani ni in yi, wato ainihin ayyukan da nake yi, su ne suke shaida ta cewa, Uba ne ya aiko ni.
37 The Father himself, who sent me, has testified about me. You have neither heard his voice at any time, nor seen his form.
Uba wanda ya aiko ni, shi da kansa ya shaide ni. Ba ku taba jin muryar sa ba, ko ganin kamanninsa.
38 You don’t have his word living in you, because you don’t believe him whom he sent.
Maganarsa kuwa ba ta zaune a zuciyarku, domin baku gaskata da wanda ya aiko ni ba.
39 “You search the Scriptures, because you think that in them you have eternal life; and these are they which testify about me. (aiōnios g166)
Kuna nazarin littattafai, don a tsammaninku a cikinsu za ku sami rai Madawwami, alhali kuwa su ne suke shaidata. (aiōnios g166)
40 Yet you will not come to me, that you may have life.
kuma baku niyyar zuwa wurina domin ku sami rai.
41 I don’t receive glory from men.
Ba na karbar yabo daga wurin mutane,
42 But I know you, that you don’t have God’s love in yourselves.
amma na sani baku da kaunar Allah a zuciyarku.
43 I have come in my Father’s name, and you don’t receive me. If another comes in his own name, you will receive him.
Na zo a cikin sunan Ubana, amma ba ku karbe ni ba. Idan wani ya zo da sunan kansa, za ku karbe shi.
44 How can you believe, who receive glory from one another, and you don’t seek the glory that comes from the only God?
Ta yaya za ku ba da gaskiya, ku da kuke karban yabo daga junanku, amma ba ku neman yabon dake zuwa daga wurin Allah?
45 “Don’t think that I will accuse you to the Father. There is one who accuses you, even Moses, on whom you have set your hope.
Kada ku yi tunani zan zarge ku a wurin Uba. Mai zargin ku shine Musa, wanda kuka sa begenku a cikin sa.
46 For if you believed Moses, you would believe me; for he wrote about me.
Inda kun gaskata Musa, da kun gaskata da ni domin ya yi rubutu game da ni.
47 But if you don’t believe his writings, how will you believe my words?”
Idan kuwa ba ku gaskata abin da ya rubuta ba, ta yaya za ku gaskata maganata?”

< Yochanan 5 >