< Job 4 >

1 Then Eliphaz the Temanite answered,
Sai Elifaz mutumin Teman ya amsa,
2 “If someone ventures to talk with you, will you be grieved? But who can withhold himself from speaking?
“In wani ya yi maka magana, za ka ji haushi? Amma wa zai iya yin shiru?
3 Behold, you have instructed many, you have strengthened the weak hands.
Ka tuna yadda ka yi wa mutane da yawa magana, yadda ka ƙarfafa hannuwa marasa ƙarfi.
4 Your words have supported him who was falling, you have made the feeble knees firm.
Maganarka ta ƙarfafa waɗanda suka yi tuntuɓe; ka ƙarfafa gwiwoyin da suka rasa ƙarfinsu.
5 But now it has come to you, and you faint. It touches you, and you are troubled.
Amma yanzu wahala ta zo maka, sai ka karaya; wahala ta sa ka rikice.
6 Isn’t your piety your confidence? Isn’t the integrity of your ways your hope?
Ashe bai kamata ka dogara ga Allahnka ba, amincinka kuma yă zama begenka?
7 “Remember, now, whoever perished, being innocent? Or where were the upright cut off?
“Ka duba ka gani yanzu. Wane marar laifi ne ya taɓa hallaka? Ko an taɓa hallaka masu adalci?
8 According to what I have seen, those who plough iniquity and sow trouble, reap the same.
Na kula cewa waɗanda suke huɗa gonar mugunta, da waɗanda suke shuka mugunta, su ne suke girbe mugunta.
9 By the breath of God they perish. By the blast of his anger are they consumed.
A sa’a ɗaya Allah yake hallaka su, cikin fushinsa yakan hallaka su.
10 The roaring of the lion, and the voice of the fierce lion, the teeth of the young lions, are broken.
Zakoki suna ruri suna gurnani; duk da haka an karya haƙoran manyan zakoki.
11 The old lion perishes for lack of prey. The cubs of the lioness are scattered abroad.
Zakoki suna mutuwa domin ba dabbar da za su kashe su ci,’ya’yan zakanya kuma sun watse.
12 “Now a thing was secretly brought to me. My ear received a whisper of it.
“Asirce aka gaya mini maganan nan, da ƙyar kunnuwana suka iya ji.
13 In thoughts from the visions of the night, when deep sleep falls on men,
Cikin mafarki da tsakar dare, lokacin kowa yana zurfin barci, na sami saƙon nan.
14 fear came on me, and trembling, which made all my bones shake.
Tsoro da fargaba suka kama ni har duk ƙasusuwan jikina suka yi ta rawa.
15 Then a spirit passed before my face. The hair of my flesh stood up.
Wani iska ya taɓa mini fuska, sai tsigar jikina ta tashi.
16 It stood still, but I couldn’t discern its appearance. A form was before my eyes. Silence, then I heard a voice, saying,
Ya tsaya cik, amma ban iya sani ko mene ne ba. Wani abu ya tsaya a gabana, na kuma ji murya.
17 ‘Shall mortal man be more just than God? Shall a man be more pure than his Maker?
‘Ko zai yiwu mutum yă fi Allah adalci, ko kuma mutum yă fi wanda ya halicce shi tsarki?
18 Behold, he puts no trust in his servants. He charges his angels with error.
In Allah bai yarda da bayinsa ba, in ya sami mala’ikunsa da laifi,
19 How much more those who dwell in houses of clay, whose foundation is in the dust, who are crushed before the moth!
to, su wane ne mutane masu zama a gidan da aka yi da laka, waɗanda da ƙura aka yi harsashensu, waɗanda za a iya murƙushe su kamar asu!
20 Between morning and evening they are destroyed. They perish forever without any regarding it.
Tsakanin safe da yamma mai yiwuwa ne ragargaza su; farat ɗaya, su mutu har abada.
21 Isn’t their tent cord plucked up within them? They die, and that without wisdom.’
Ba a tuge igiyar tentinsu, don su mutu ba tare da hikima ba?’

< Job 4 >