< Ezekiel 34 >

1 The LORD’s word came to me, saying,
Maganar Ubangiji ta zo mini cewa,
2 “Son of man, prophesy against the shepherds of Israel. Prophesy, and tell them, even the shepherds, ‘The Lord GOD says: “Woe to the shepherds of Israel who feed themselves! Shouldn’t the shepherds feed the sheep?
“Ɗan mutum, ka yi annabci a kan makiyayan Isra’ila; ka yi annabci ka ce musu, ‘Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa kaiton makiyayan Isra’ila waɗanda suke kula da kansu ne kawai! Ashe, bai kamata makiyaya ne su lura da tumaki ba?
3 You eat the fat. You clothe yourself with the wool. You kill the fatlings, but you don’t feed the sheep.
Kuna cin kitsensu, kuna yi wa kanku tufafi da gashinsu, kukan yanka turkakkun, amma ba ku yi kiwon tumakin ba.
4 You haven’t strengthened the diseased. You haven’t healed that which was sick. You haven’t bound up that which was broken. You haven’t brought back that which was driven away. You haven’t sought that which was lost, but you have ruled over them with force and with rigor.
Ba ku ƙarfafa marasa ƙarfi ba, ko ku warkar da marasa lafiya ko ku ɗaura waɗanda suka ji rauni. Ba ku dawo da waɗanda suka yi makuwa ko ku nemi waɗanda suka ɓace ba. Amma sai kuka mallake su ƙarfi da yaji.
5 They were scattered, because there was no shepherd. They became food to all the animals of the field, and were scattered.
Saboda haka suka warwatse domin babu makiyayi, kuma da suka warwatsu sai suka zama abincin namun jeji.
6 My sheep wandered through all the mountains and on every high hill. Yes, my sheep were scattered on all the surface of the earth. There was no one who searched or sought.”
Tumakina suna ta yawo a kan dukan duwatsu da kuma kowane tudu. Sun watsu a dukan duniya, kuma ba wanda ya neme su.
7 “‘Therefore, you shepherds, hear the LORD’s word:
“‘Saboda haka, ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
8 “As I live,” says the Lord GOD, “surely because my sheep became a prey, and my sheep became food to all the animals of the field, because there was no shepherd, and my shepherds didn’t search for my sheep, but the shepherds fed themselves, and didn’t feed my sheep,
Muddin ina raye, in ji Ubangiji Mai Iko Duka, domin tumaki sun rasa makiyayi ta haka aka washe su suka kuma zama abincin dukan namun jeji, kuma domin makiyayana ba su nemi tumakina ba amma suka kula da kansu a maimakon tumakina,
9 therefore, you shepherds, hear the LORD’s word!”
saboda haka, ya ku makiyaya, ku ji maganar Ubangiji,
10 The Lord GOD says: “Behold, I am against the shepherds. I will require my sheep at their hand, and cause them to cease from feeding the sheep. The shepherds won’t feed themselves any more. I will deliver my sheep from their mouth, that they may not be food for them.”
Ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ina gāba da makiyaya kuma zan nemi hakkin tumakina daga gare su. Zan hana su yin kiwon tumakin don kada makiyayan su ƙara yin kiwon kansu. Zan ƙwace tumakina daga bakunansu, ba kuwa za su ƙara zama abincinsu.
11 “‘For the Lord GOD says: “Behold, I myself, even I, will search for my sheep, and will seek them out.
“‘Gama ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa ni kaina zan nemi tumakina.
12 As a shepherd seeks out his flock in the day that he is amongst his sheep that are scattered abroad, so I will seek out my sheep. I will deliver them out of all places where they have been scattered in the cloudy and dark day.
Kamar yadda makiyayi yakan lura da tumakinsa da suka watse sa’ad da yake tare da su, haka zan lura da tumakina. Zan cece su daga dukan wuraren da aka watsar da su a ranar gizagizai da baƙin duhu.
13 I will bring them out from the peoples, and gather them from the countries, and will bring them into their own land. I will feed them on the mountains of Israel, by the watercourses, and in all the inhabited places of the country.
Zan dawo da su daga al’ummai in kuma tattara su daga ƙasashe, zan kuma kawo su cikin ƙasarsu. Zan yi kiwonsu a kan duwatsun Isra’ila, a maɓulɓulai da kuma cikin wuraren zamansu a ƙasar.
14 I will feed them with good pasture, and their fold will be on the mountains of the height of Israel. There they will lie down in a good fold. They will feed on rich pasture on the mountains of Israel.
Zan kula da su a wurin kiwo mai kyau, kuma ƙwanƙolin duwatsun Isra’ila ne zai zama wurin kiwonsu. Za su kwanta a wurin kiwo mai kyau, a can kuma za su yi kiwo a wurin kiwo mai kyau a kan duwatsun Isra’ila.
15 I myself will be the shepherd of my sheep, and I will cause them to lie down,” says the Lord GOD.
Ni kaina zan lura da tumakina in kuma sa su kwanta, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
16 “I will seek that which was lost, and will bring back that which was driven away, and will bind up that which was broken, and will strengthen that which was sick; but I will destroy the fat and the strong. I will feed them in justice.”’
Zan nemi ɓatattuna in kuma dawo da waɗanda suka yi makuwa. Zan ɗaura raunin waɗanda suka ji ciwo in kuma ƙarfafa marasa ƙarfi, amma zan hallaka ƙarfafa da kuma masu ƙiba. Zan yi kiwo tumaki da adalci.
17 “As for you, O my flock, the Lord GOD says: ‘Behold, I judge between sheep and sheep, the rams and the male goats.
“‘Game da ku, tumakina, ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka yana cewa zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya, da tsakanin raguna da awaki.
18 Does it seem a small thing to you to have fed on the good pasture, but you must tread down with your feet the residue of your pasture? And to have drunk of the clear waters, but must you foul the residue with your feet?
Bai isa ba a ce kun yi kiwo a wuri mai kyau? Sai kun tattake sauran wurin kiwonku da ƙafafunku tukuna? Bai isa ba a ce kun sha ruwa mai tsabta? Sai kun kuma gurɓata sauran da ƙafafunku?
19 As for my sheep, they eat that which you have trodden with your feet, and they drink that which you have fouled with your feet.’
Dole ne tumakina su ci abin da kuka tattake su kuma sha abin da kuka gurɓata da ƙafafunku?
20 “Therefore the Lord GOD says to them: ‘Behold, I, even I, will judge between the fat sheep and the lean sheep.
“‘Saboda haka ga abin da Ubangiji Mai Iko Duka ya ce musu, duba, ni kaina zan hukunta tsakanin turkakkun tumaki da ramammun tumaki.
21 Because you thrust with side and with shoulder, and push all the diseased with your horns, until you have scattered them abroad,
Domin kun tunkuɗe marasa ƙarfi da kafaɗunku, kun kuma tunkuye su da ƙahoninku sai da suka gudu,
22 therefore I will save my flock, and they will no more be a prey. I will judge between sheep and sheep.
zan cece tumakina ba za su ƙara zama ganima ba. Zan hukunta tsakanin tunkiya da tunkiya.
23 I will set up one shepherd over them, and he will feed them, even my servant David. He will feed them, and he will be their shepherd.
Zan sa musu makiyaya guda, bawana Dawuda, zai kuwa lura da su; zai kula da su ya kuma zama makiyayinsu.
24 I, the LORD, will be their God, and my servant David prince amongst them. I, the LORD, have spoken it.
Ni Ubangiji zan zama Allahnsu, bawana kuma Dawuda zai zama yerima a cikinsu. Ni Ubangiji na faɗa.
25 “‘I will make with them a covenant of peace, and will cause evil animals to cease out of the land. They will dwell securely in the wilderness and sleep in the woods.
“‘Zan yi alkawarin salama da su in kuma kawar wa ƙasar da namun jeji domin su zauna a hamada su kuma kwana a kurmi lafiya lau.
26 I will make them and the places around my hill a blessing. I will cause the shower to come down in its season. There will be showers of blessing.
Zan albarkace su in kuma sa tuduna kewaye da su. Zan zubo yayyafi a lokacinsa; za a kasance da yayyafin albarka.
27 The tree of the field will yield its fruit, and the earth will yield its increase, and they will be secure in their land. Then they will know that I am the LORD, when I have broken the bars of their yoke, and have delivered them out of the hand of those who made slaves of them.
Itatuwan gona za su ba da’ya’yansu, ƙasa kuma za tă ba da amfaninta; mutane za su zauna lafiya a ƙasarsu. Za su san cewa ni ne Ubangiji, sa’ad da na karya karkiyarsu, na cece su daga hannun waɗanda suka bautar da su.
28 They will no more be a prey to the nations, neither will the animals of the earth devour them; but they will dwell securely, and no one will make them afraid.
Ba za su ƙara zama ganimar al’ummai ba, ba kuwa namun jeji za su cinye su ba. Za su zauna lafiya, kuma babu wani da zai sa su ji tsoro.
29 I will raise up to them a plantation for renown, and they will no more be consumed with famine in the land, and not bear the shame of the nations any more.
Zan tanada musu ƙasar da aka sani don hatsinta, ba za su kuma ƙara zama abin da yunwa za tă fara musu a ƙasa ba ko su sha zargin sauran al’ummai.
30 They will know that I, the LORD, their God am with them, and that they, the house of Israel, are my people, says the Lord GOD.
Sa’an nan za su san cewa ni, Ubangiji Allahnsu, ina tare da su kuma cewa su, gidan Isra’ila, mutanena ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.
31 You my sheep, the sheep of my pasture, are men, and I am your God,’ says the Lord GOD.”
Ku tumakina, tumakin wurin kiwona, mutanena ne, ni kuwa Allahnku ne, in ji Ubangiji Mai Iko Duka.’”

< Ezekiel 34 >