< Ephesians 5 >

1 Be therefore imitators of God, as beloved children.
Saboda haka ku zama masu koyi da Allah, kamar kaunatattun 'ya'yansa.
2 Walk in love, even as Messiah also loved us and gave himself up for us, an offering and a sacrifice to God for a sweet-smelling fragrance.
Ku yi zama cikin kauna kamar yadda Almasihu ya kaunace mu, ya kuma mika kansa sadaka da hadaya ga Allah dominmu, hadaya mai kanshi abin karba ga Allah.
3 But sexual immorality, and all uncleanness or covetousness, let it not even be mentioned amongst you, as becomes holy ones;
Fasikanci ko kowacce irin kazamta, ko kazamar lalata kada a ambace su a tsakaninku, don haka ya dace ga masu bi.
4 nor filthiness, nor foolish talking, nor jesting, which are not appropriate, but rather giving of thanks.
Kada a ambaci batsa, maganar wauta ko alfasha wadanda ba su dace ba. Maimakon haka, mu zama masu godiya.
5 Know this for sure, that no sexually immoral person, nor unclean person, nor covetous man (who is an idolater), has any inheritance in the Kingdom of Messiah and God.
Domin wannan kun sani cewa ba fasiki, ko mara tsarki, ko mai hadama wato mai bautar gumaka zai sami gado cikin mulkin Almasihu da Allah.
6 Let no one deceive you with empty words, for because of these things the wrath of God comes on the children of disobedience.
Kada kowa ya rude ku da maganganun wofi. Saboda wadannan abubuwa ne fushin Allah ke zuwa kan kangararrun 'ya'ya.
7 Therefore don’t be partakers with them.
Kada ku yi tarayya tare da su.
8 For you were once darkness, but are now light in the Lord. Walk as children of light,
Domin da ku duhu ne, amma yanzu ku haske ne cikin Ubangiji. Sai ku yi tafiya kamar 'ya'yan haske.
9 for the fruit of the Spirit is in all goodness and righteousness and truth,
Saboda amfanin haske shine dukan alheri, adalci da gaskiya.
10 proving what is well pleasing to the Lord.
Kuna bidar abin da Ubangiji ke murna da shi.
11 Have no fellowship with the unfruitful deeds of darkness, but rather even reprove them.
Kada ku sa hannu ga ayyuka marasa amfani da ayyukan duhu amma gara a tone su.
12 For it is a shame even to speak of the things which are done by them in secret.
Don abubuwan da suke yi a boye abin kunya ne a bayyana su.
13 But all things, when they are reproved, are revealed by the light, for everything that reveals is light.
Dukan abu, idan haske ya bayyana su, za a gan su.
14 Therefore he says, “Awake, you who sleep, and arise from the dead, and Messiah will shine on you.”
Domin duk abin da aka bayyana ya zama haske. Saboda haka aka ce, “Ka farka, kai mai barci, ka tashi daga cikin matattu; Almasihu kuwa zai haskaka bisanka”.
15 Therefore watch carefully how you walk, not as unwise, but as wise,
Saboda haka, ku maida hankali yadda kuke rayuwar ku, ba kamar mutane marasa hikima ba amma kamar masu hikima.
16 redeeming the time, because the days are evil.
Ku yi lura yadda kuke amfani da lokaci don kwanakin miyagu ne.
17 Therefore, don’t be foolish, but understand what the will of the Lord is.
Kada ku zama wawaye. Maimakon haka, ku fahimci ko menene nufin Ubangiji.
18 Don’t be drunken with wine, in which is dissipation, but be filled with the Spirit,
Kuma Kada ku bugu da ruwan inabi, don yana iya lalata rayuwa. Maimakon haka, ku cika da Ruhu Mai Tsarki.
19 speaking to one another in psalms, hymns, and spiritual songs; singing and making melody in your heart to the Lord;
Kuna magana da junanku cikin zabura da wakoki da wakokin ruhaniya, kuna rairawa da yabo da zuciyarku ga Ubangiji.
20 giving thanks always concerning all things in the name of our Lord Yeshua the Messiah to God, even the Father;
Kullum kuna ba da gaskiya domin dukan abubuwa cikin sunan Ubangiji Yesu ga Allah Uba.
21 subjecting yourselves to one another in the fear of Messiah.
Kuna sarayadda kanku ga juna cikin girmama Almasihu.
22 Wives, be subject to your own husbands, as to the Lord.
Mata, ku yi biyayya ga mazan ku kamar ga Ubangiji.
23 For the husband is the head of the wife, as Messiah also is the head of the assembly, being himself the saviour of the body.
Domin miji shine shugaban matarsa kamar yadda Almasihu yake shugaban ikilisiya. Shine kuma mai ceton jiki.
24 But as the assembly is subject to Messiah, so let the wives also be to their own husbands in everything.
Amma kamar yadda ikilisiya take biyayya ga Almasihu, haka kuma dole mata suyi ga mazajen su cikin kowanne abu.
25 Husbands, love your wives, even as Messiah also loved the assembly and gave himself up for her,
Mazaje, ku kaunaci matanku kamar yadda Almasihu ya kaunaci ikilisiya har ya ba da kansa dominta,
26 that he might sanctify her, having cleansed her by the washing of water with the word,
Ya yi wannan domin ya tsarkake ta. Ya wanke mu da ruwan wanki ta wurin kalma.
27 that he might present the assembly to himself gloriously, not having spot or wrinkle or any such thing, but that she should be holy and without defect.
Ya yi wannan domin ya mika ma kansa ikilisiya mai daraja, ba tare da tabo ko cikas ko wani abu kamar wadannan, amma ta zama da tsarki da kuma mara aibi.
28 Even so husbands also ought to love their own wives as their own bodies. He who loves his own wife loves himself.
Hakannan kuma, mazaje su kaunaci matansu kamar jikunnansu. Wanda yake kaunar matarsa yana kaunar kansa.
29 For no man ever hated his own flesh, but nourishes and cherishes it, even as the Lord also does the assembly,
Ba wanda ya taba kin jikinsa. Amma, yakan ciyadda shi yana kaunarsa, kamar yadda Almasihu ya kaunaci ikilisiya.
30 because we are members of his body, of his flesh and bones.
Domin mu gabobin jikinsa ne.
31 “For this cause a man will leave his father and mother and will be joined to his wife. Then the two will become one flesh.”
“Domin wannan mutum zai rabu da ubansa da uwarsa ya manne wa matarsa, su biyu su zama nama daya”.
32 This mystery is great, but I speak concerning Messiah and the assembly.
Wannan asirin gaskiyar, da girma yake, amma ina magana ne game da Almasihu da ikilisiyarsa.
33 Nevertheless each of you must also love his own wife even as himself; and let the wife see that she respects her husband.
Duk da haka, kowannenku dole ya kaunaci matarsa kamar kansa, matar kuma dole ta girmama mijinta.

< Ephesians 5 >