< 2 Thessalonians 1 >

1 Paul, Silvanus, and Timothy, to the assembly of the Thessalonians in God our Father and the Lord Yeshua the Messiah:
Bulus, da Sila, da Timoti, Zuwa ga ikkilisiya ta Tessalonikawa ta Allah Ubanmu da Ubangiji Yesu Kiristi.
2 Grace to you and peace from God our Father and the Lord Yeshua the Messiah.
Alheri da salama daga Allah Uba da kuma Ubangiji Yesu Kiristi, su kasance tare da ku.
3 We are bound to always give thanks to God for you, brothers, even as it is appropriate, because your faith grows exceedingly, and the love of each and every one of you towards one another abounds,
Dole kullum mu gode wa Allah saboda ku,’yan’uwa, haka kuwa ya dace, domin bangaskiyarku tana girma gaba-gaba, ƙaunar da kowannenku yake yi wa juna kuwa tana ƙaruwa.
4 so that we ourselves boast about you in the assemblies of God for your perseverance and faith in all your persecutions and in the afflictions which you endure.
Saboda haka, a cikin ikkilisiyoyin Allah muna taƙama game da daurewarku da kuma bangaskiyarku cikin dukan tsanani da gwaje-gwajen da kuke sha.
5 This is an obvious sign of the righteous judgement of God, to the end that you may be counted worthy of God’s Kingdom, for which you also suffer.
Dukan wannan yana tabbatar cewa hukuncin Allah daidai ne, saboda haka kuma za a lissafta ku a kan kun cancanci mulkin Allah, wanda dominsa ne kuke shan wahala.
6 For it is a righteous thing with God to repay affliction to those who afflict you,
Allah mai adalci ne, Zai sāka wa masu ba ku wahala da wahala
7 and to give relief to you who are afflicted with us when the Lord Yeshua is revealed from heaven with his mighty angels in flaming fire,
yă kuma sauƙaƙa muku ku da kuke wahala, har ma da mu. Wannan zai faru sa’ad da aka bayyana Ubangiji Yesu daga sama cikin wuta mai ci tare da mala’ikunsa masu iko.
8 punishing those who don’t know God, and to those who don’t obey the Good News of our Lord Yeshua,
Zai hukunta waɗanda ba su san Allah ba da kuma waɗanda ba su yi biyayya da bisharar Ubangijinmu Yesu ba.
9 who will pay the penalty: eternal destruction from the face of the Lord and from the glory of his might, (aiōnios g166)
Za a hukunta su da madawwamiyar hallaka a kuma kau da su daga gaban Ubangiji da kuma daga ɗaukakar ikonsa (aiōnios g166)
10 when he comes in that day to be glorified in his holy ones and to be admired amongst all those who have believed, because our testimony to you was believed.
a ranar da zai dawo don a ɗaukaka shi a cikin mutanensa masu tsarki, yă kuma zama abin banmamaki ga dukan waɗanda suka gaskata. Wannan ya haɗa har da ku, domin kun gaskata shaidar da muka yi muku.
11 To this end we also pray always for you that our God may count you worthy of your calling, and fulfil every desire of goodness and work of faith with power,
Sane da wannan, kullum muna addu’a saboda ku, don Allahnmu yă sa ku cancanci kiransa, ta wurin ikonsa kuma yă cika kowace manufarku mai kyau da kuma kowane aikin da bangaskiyarku ta iza.
12 that the name of our Lord Yeshua may be glorified in you, and you in him, according to the grace of our God and the Lord Yeshua the Messiah.
Muna wannan addu’a don sunan Ubangijinmu Yesu yă sami ɗaukaka a cikinku, ku kuma a cikinsa, bisa ga alherin Allahnmu da na Ubangiji Yesu Kiristi.

< 2 Thessalonians 1 >