< 2 Thessalonians 2 >

1 Now, brothers, concerning the coming of our Lord Yeshua the Messiah and our gathering together to him, we ask you
Game da dawowar Ubangijinmu Yesu Kiristi da game da tattara mu gare shi, muna roƙonku,’yan’uwa,
2 not to be quickly shaken in your mind or troubled, either by spirit or by word or by letter as if from us, saying that the day of Messiah has already come.
kada ku yi saurin jijjiguwa ko kuwa hankalinku yă tashi ta wurin wani annabci, rahoto ko wasiƙar da an ce daga wurinmu ne, cewa ranar Ubangiji ta riga ta zo.
3 Let no one deceive you in any way. For it will not be unless the rebellion comes first, and the man of sin is revealed, the son of destruction.
Kada ku bar wani yă ruɗe ku ko ta yaya, gama wannan rana ba za tă zo ba sai an yi tawayen nan an kuma bayyana mutumin tawayen nan, mutumin da aka ƙaddara ga hallaka.
4 He opposes and exalts himself against all that is called God or that is worshipped, so that he sits as God in the temple of God, setting himself up as God.
Zai yi gāba yă kuma ɗaukaka kansa a bisa kome da ya shafe sunan Allah, ko kuma ake yi wa sujada, domin yă kafa kansa a haikalin Allah, yana shelar kansa a kan shi Allah ne.
5 Don’t you remember that when I was still with you, I told you these things?
Ba ku tuna ba cewa sa’ad da nake tare da ku nakan gaya muku waɗannan abubuwa?
6 Now you know what is restraining him, to the end that he may be revealed in his own season.
Yanzu kuwa kun san abin da yake hana shi, wannan yana faruwa ne don a bayyana shi a daidai lokaci.
7 For the mystery of lawlessness already works. Only there is one who restrains now, until he is taken out of the way.
Gama ikon asirin tawaye ya riga ya fara aiki; sai dai wannan da yake hana shi zai ci gaba da yin haka sai an kau da shi.
8 Then the lawless one will be revealed, whom the Lord will kill with the breath of his mouth and destroy by the manifestation of his coming;
Sa’an nan za a bayyana mai tawayen, Ubangiji Yesu kuwa zai hamɓare shi da numfashin bakinsa yă kuma hallaka shi da darajar dawowarsa.
9 even he whose coming is according to the working of Satan with all power and signs and lying wonders,
Zuwan mai tawayen nan zai zama ta wurin aikin Shaiɗan da aka bayyana cikin kowane irin ayyukan banmamaki, alamu da abubuwan banmamaki na ƙarya,
10 and with all deception of wickedness for those who are being lost, because they didn’t receive the love of the truth, that they might be saved.
da kuma cikin kowace irin muguntar da take ruɗin waɗanda suke hallaka. Sun hallaka ne domin sun ƙi su ƙaunaci gaskiya don su sami ceto.
11 Because of this, God sends them a powerful delusion, that they should believe a lie,
Saboda haka Allah zai aiko musu da babban ruɗu don su gaskata ƙarya
12 that they all might be judged who didn’t believe the truth, but had pleasure in unrighteousness.
don kuma a hukunta dukan waɗanda ba su gaskata gaskiyar ba sai dai suke jin daɗin mugunta.
13 But we are bound to always give thanks to God for you, brothers loved by the Lord, because God chose you from the beginning for salvation through sanctification of the Spirit and belief in the truth,
Amma dole kullum mu gode wa Allah dominku,’yan’uwa waɗanda Ubangiji ya ƙaunace, domin daga farko Allah ya zaɓe ku don a cece ku ta wurin aikin tsarkakewar Ruhu da kuma ta wurin gaskatawa da gaskiya.
14 to which he called you through our Good News, for the obtaining of the glory of our Lord Yeshua the Messiah.
Ya kira ku ga wannan ta wurin bishararmu, don ku sami rabo a cikin ɗaukakar Ubangijinmu Yesu Kiristi.
15 So then, brothers, stand firm and hold the traditions which you were taught by us, whether by word or by letter.
Saboda haka fa,’yan’uwa, sai ku tsaya daram ku riƙe koyarwar da muka miƙa muku, ko ta wurin maganar baki ko kuma ta wurin wasiƙa.
16 Now our Lord Yeshua the Messiah himself, and God our Father, who loved us and gave us eternal comfort and good hope through grace, (aiōnios g166)
Ubangijinmu Yesu Kiristi kansa da kuma Allah Ubanmu, wanda ya ƙaunace mu kuma ta wurin alherinsa yă ba mu madawwamiyar ƙarfafawa da kyakkyawar bege, (aiōnios g166)
17 comfort your hearts and establish you in every good work and word.
yă ƙarfafa zukatanku yă kuma gina ku cikin kowane aikin nagari da kuma magana.

< 2 Thessalonians 2 >