< 2 Peter 1 >

1 Simon Peter, a servant and emissary of Yeshua the Messiah, to those who have obtained a like precious faith with us in the righteousness of our God and Saviour, Yeshua the Messiah:
Siman Bitrus, bawa da manzon Almasihu Yesu, zuwa ga wadanda suka karbi bangaskiya mai daraja kamar yadda muka karba, bangaskiya cikin adalcin Allahnmu da Yesu Almasihu.
2 Grace to you and peace be multiplied in the knowledge of God and of Yeshua our Lord,
Bari alheri ya kasance tare da ku; bari salama ta karu ta wurin sanin Allah da na Yesu Ubangijinmu.
3 seeing that his divine power has granted to us all things that pertain to life and godliness, through the knowledge of him who called us by his own glory and virtue,
Dukkan abubuwan ikon Allah na rayuwa da Allahntaka an bamu su ta wurin sanin Allah, wanda ya kira mu ta wurin daukakarsa da nagarta.
4 by which he has granted to us his precious and exceedingly great promises; that through these you may become partakers of the divine nature, having escaped from the corruption that is in the world by lust.
Ta wurin wanan, ya bamu babban alkawari mai daraja. Yayi wanan ne saboda ku zama masu rabo cikin Allahntaka, yayin da ku ka kubuta daga lalacewa da ke cikin duniya saboda mugayen sha'awace sha, awace.
5 Yes, and for this very cause adding on your part all diligence, in your faith supply moral excellence; and in moral excellence, knowledge;
Saboda wanan dalilin kuyi iyakacin kokarinku ku kara nagarta ta wurin bangaskiyarku, kuma ta wurin adalci, sani.
6 and in knowledge, self-control; and in self-control, perseverance; and in perseverance, godliness;
Ta wurin sani ku kara da kamun kai, kuma ta wurin kamun kanku, ku kara da jimrewa, ta wurin jimrewarku, ku kara da bin Allah.
7 and in godliness, brotherly affection; and in brotherly affection, love.
Ta wurin bin Allah, ku kara da kauna irin ta 'yan'uwa, ta wurin kauna irin ta 'yan'uwa, ku kara kauna.
8 For if these things are yours and abound, they make you to not be idle or unfruitful in the knowledge of our Lord Yeshua the Messiah.
Idan wadannan abubuwan suna cikinku, kuma suka yi girma a cikinku, baza a sami bakarare ko rashin 'ya'ya cikin sanin Ubangijinmu Yesu Almasihu ba.
9 For he who lacks these things is blind, seeing only what is near, having forgotten the cleansing from his old sins.
Amma duk wanda ya rasa wadannan abubuwan yana kallon abin da ke kusa ne kawai; ya makance. Ya manta da cewa an wake shi daga tsofaffin zunubansa.
10 Therefore, brothers, be more diligent to make your calling and election sure. For if you do these things, you will never stumble.
Saboda haka, 'yan'uwa, kuyi iyakacin kokari ku tabbatar da kiranku da zabenku. Idan kun yi wadannan abubuwan, baza ku yi tuntube ba.
11 For thus you will be richly supplied with the entrance into the eternal Kingdom of our Lord and Saviour, Yeshua the Messiah. (aiōnios g166)
Ta haka zaku sami shiga cikin mulki na har'abada na Ubangijinmu da Maicetonmu Yesu Almasihu. (aiōnios g166)
12 Therefore I will not be negligent to remind you of these things, though you know them and are established in the present truth.
Saboda haka a shirye nake kulayomi in tunashe ku game da wadannan abubuwan, ko da yake kun san su, kuma kun yi karfi cikin gaskiya yanzu.
13 I think it right, as long as I am in this tent, to stir you up by reminding you,
Ina tunani daidai ne in zuga ku da tuni game da wadannan abubuwan, tun ina cikin wannan jiki.
14 knowing that the putting off of my tent comes swiftly, even as our Lord Yeshua the Messiah made clear to me.
Domin na sani jim kadan zan bar wannan jiki, kamar yadda Yesu Almasihu ya nuna mani.
15 Yes, I will make every effort that you may always be able to remember these things even after my departure.
Zan yi iyakancin kokarina kulayomi domin ku rika tunawa da abubuwan, bayan kaurata.
16 For we didn’t follow cunningly devised fables when we made known to you the power and coming of our Lord Yeshua the Messiah, but we were eyewitnesses of his majesty.
Domin bamu bi labaru da aka kago na nuna wayo cikinsu ba, da muka fada maku game da iko da bayyanuwar Ubangijinmu Yesu Almasihu, amma mu shaidu ne na ikonsa.
17 For he received from God the Father honour and glory when the voice came to him from the Majestic Glory, “This is my beloved Son, in whom I am well pleased.”
Gama ya karbi daukaka da daraja daga wurin Allah Uba lokacin da murya ta zo daga ikon mai daukaka cewa, “Wannan shine dana, kaunataccena, wanda nake jin dadinsa kwarai.”
18 We heard this voice come out of heaven when we were with him on the holy mountain.
Mun ji muryar nan da ta zo daga sama, lokacin da mu ke tare da shi a dutse mai tsarki.
19 We have the more sure word of prophecy; and you do well that you heed it as to a lamp shining in a dark place, until the day dawns and the morning star arises in your hearts,
Muna da wannan kalmar annabci wanda akwai tabbaci sosai, kun yi daidai idan kun mayar da hankali a kansu. Yana nan kamar fitillar da take walkiya a wuri mai duhu kafin asubahi ya zo, kuma tauraron asubahi ya tashi cikin zukatanku.
20 knowing this first, that no prophecy of Scripture is of private interpretation.
Ku san da wannan tun da farko, cewa babu annabci da ke bisa ga fasarar mutum.
21 For no prophecy ever came by the will of man, but holy men of God spoke, being moved by the Holy Spirit.
Domin babu annabcin da ya taba zuwa ta wurin nufin mutum. Maimakon haka, Ruhu Mai Tsarki ne ke iza su, su fadi maganar Allah.

< 2 Peter 1 >