< 1 Corinthians 3 >

1 Brothers, I couldn’t speak to you as to spiritual, but as to fleshly, as to babies in Messiah.
Amma ni, yan'uwa, ba zan iya magana da ku kamar mutane masu ruhaniya ba, amma kamar mutane masu jiki, kamar jarirai cikin Almasihu.
2 I fed you with milk, not with solid food, for you weren’t yet ready. Indeed, you aren’t ready even now,
Na shayar da ku da Madara ba da nama ba, don baku isa cin nama ba, kuma ko yanzu ma baku isa ba.
3 for you are still fleshly. For insofar as there is jealousy, strife, and factions amongst you, aren’t you fleshly, and don’t you walk in the ways of men?
Gama har yanzu ku masu jiki ne. Muddin akwai kishi da jayayya a tsakaninku, ashe, ku ba masu jiki ba ne, kuma kuna tafiya bisa magwajin mutane?
4 For when one says, “I follow Paul,” and another, “I follow Apollos,” aren’t you fleshly?
Domin in wani ya ce, “Ina bayan Bulus,” wani kuma ya ce, “Ina bayan Afollos,” ashe, ba zaman mutuntaka kuke yi ba?
5 Who then is Apollos, and who is Paul, but servants through whom you believed, and each as the Lord gave to him?
To wanene Afollos? Wanene kuma Bulus? Bayi ne wadanda kuka bada gaskiya ta wurin su, kowannen su kuwa Allah ya bashi ayyuka.
6 I planted. Apollos watered. But God gave the increase.
Ni nayi shuka, Afolos yayi banruwa, amma Allah ne ya sa girma.
7 So then neither he who plants is anything, nor he who waters, but God who gives the increase.
Don haka, da mai shukar da mai banruwan, ba komi bane. Amma Allah ne mai sa girman.
8 Now he who plants and he who waters are the same, but each will receive his own reward according to his own labour.
Da mai shukar, da mai banruwan, duk daya suke, kuma kowannen su zai sami nasa lada, gwargwadon aikinsa.
9 For we are God’s fellow workers. You are God’s farming, God’s building.
Gama mu abokan aiki ne na Allah. Ku gonar Allah ne, ginin Allah kuma.
10 According to the grace of God which was given to me, as a wise master builder I laid a foundation, and another builds on it. But let each man be careful how he builds on it.
Bisa ga alherin Allah da aka bani a matsayin gwanin magini, na kafa harsashi, wani kuma yana dora gini a kai. Sai dai kowane mutum, ya lura da yadda yake dora ginin.
11 For no one can lay any other foundation than that which has been laid, which is Yeshua the Messiah.
Gama ba wanda ke iya kafa wani harsashin daban da wanda aka rigaya aka kafa, wato, Yesu Almasihu.
12 But if anyone builds on the foundation with gold, silver, costly stones, wood, hay, or straw,
Yanzu fa in wani ya dora gini a kan harashin da zinariya, ko azurfa, ko duwatsu masu daraja, ko itace, ko ciyawa, ko tattaka,
13 each man’s work will be revealed. For the Day will declare it, because it is revealed in fire; and the fire itself will test what sort of work each man’s work is.
aikinsa zai bayyanu, domin ranar nan zata tona shi. Gama za a bayyana shi cikin wuta. Wutar kuwa zata gwada ingancin aikin da kowa ya yi.
14 If any man’s work remains which he built on it, he will receive a reward.
Duk wanda aikinsa ya tsaya, zai karbi lada;
15 If any man’s work is burnt, he will suffer loss, but he himself will be saved, but as through fire.
amma duk wanda aikinsa ya kone, zai sha Asara, amma shi kansa zai tsira, sai dai kamar ta tsakiyar wuta.
16 Don’t you know that you are God’s temple and that God’s Spirit lives in you?
Ashe, baku san ku haikalin Allah ne ba, Ruhun Allah kuma yana zaune a cikin ku?
17 If anyone destroys God’s temple, God will destroy him; for God’s temple is holy, which you are.
Idan wani ya lalata haikalin Allah, Allah zai lalata shi. Gama haikalin Allah mai tsarki ne, kuma haka ku ke.
18 Let no one deceive himself. If anyone thinks that he is wise amongst you in this world, let him become a fool that he may become wise. (aiōn g165)
Kada kowa ya rudi kansa. Idan wani a cikin ku na ganin shi mai hikima ne a wannan zamani, bari ya zama” wawa” domin ya zama mai hikima. (aiōn g165)
19 For the wisdom of this world is foolishness with God. For it is written, “He has taken the wise in their craftiness.”
Gama hikimar duniyar nan wauta ce a gun Allah. Gama a rubuce yake, “Yakan kama masu hikima a cin makircin su.”
20 And again, “The Lord knows the reasoning of the wise, that it is worthless.”
Har wa yau, “Ubangiji ya san tunanin masu hikima banza ne.”
21 Therefore let no one boast in men. For all things are yours,
haka ba sauran fariya akan mutane! Domin kuwa kome naku ne,
22 whether Paul, or Apollos, or Kefa, or the world, or life, or death, or things present, or things to come. All are yours,
Ko Bulus, ko Afollos, ko kefas, ko duniya, ko rai, ko mutuwa, ko abubuwa na yanzu, ko abubuwa masu zuwa. Duka naku ne,
23 and you are Messiah’s, and Messiah is God’s.
Ku kuwa na Almasihu ne, Almasihu kuma na Allah ne.

< 1 Corinthians 3 >