< 1 Chronicles 11 >

1 Then all Israel gathered themselves to David to Hebron, saying, “Behold, we are your bone and your flesh.
Dukan Isra’ila fa suka taru wurin Dawuda a Hebron suka ce, “Mu jiki da jininka ne.
2 In times past, even when Saul was king, it was you who led out and brought in Israel. The LORD your God said to you, ‘You shall be shepherd of my people Israel, and you shall be prince over my people Israel.’”
A dā, ko a lokacin da Shawulu yake sarki, ai, kai ne kake shugabantar Isra’ila a yaƙe-yaƙe. Kuma Ubangiji Allahnka ya ce maka, ‘Za ka zama makiyayin mutanena Isra’ila, za ka kuma zama mai mulkinsu.’”
3 So all the elders of Israel came to the king to Hebron; and David made a covenant with them in Hebron before the LORD. They anointed David king over Israel, according to the LORD’s word by Samuel.
Sa’ad da dukan dattawan Isra’ila suka zo wurin Sarki Dawuda a Hebron, suka yi yarjejjeniya da shi a gaban Ubangiji, suka kuwa shafe Dawuda ya zama sarki a bisa Isra’ila, yadda Ubangiji ya yi alkawari ta wurin Sama’ila.
4 David and all Israel went to Jerusalem (also called Jebus); and the Jebusites, the inhabitants of the land, were there.
Dawuda tare da dukan Isra’ilawa suka taka zuwa Urushalima (wato, Yebus). Yebusiyawan da suke zama a wurin
5 The inhabitants of Jebus said to David, “You will not come in here!” Nevertheless David took the stronghold of Zion. The same is David’s city.
suka ce wa Dawuda, “Ba za ka shiga nan ba.” Duk da haka, Dawuda ya ci kagarar Sihiyona, Birnin Dawuda.
6 David had said, “Whoever strikes the Jebusites first shall be chief and captain.” Joab the son of Zeruiah went up first, and was made chief.
Dawuda ya ce, “Duk wanda ya jagoranci yaƙi a kan Yebusiyawa zai zama babban shugaban mayaƙa.” Yowab ɗan Zeruhiya ya fara haurawa, ta haka ya zama shugaba.
7 David lived in the stronghold; therefore they called it David’s city.
Dawuda zauna a kagarar, ta haka aka kira ta Birnin Dawuda.
8 He built the city all around, from Millo even around; and Joab repaired the rest of the city.
Sai ya gina birni kewaye da shi, daga madogaran gini zuwa katangar da take kewaye, yayinda Yowab ya maido da sauran birnin.
9 David grew greater and greater, for the LORD of Hosts was with him.
Dawuda kuwa ya ƙara ƙarfi, domin Ubangiji Maɗaukaki yana tare da shi.
10 Now these are the chief of the mighty men whom David had, who showed themselves strong with him in his kingdom, together with all Israel, to make him king, according to the LORD’s word concerning Israel.
Waɗannan su ne manyan jarumawan Dawuda, su ne, tare da dukan Isra’ila, suka ba wa mulkinsa goyon baya mai ƙarfi da ya kai bisa dukan ƙasar, yadda Ubangiji ya yi alkawari.
11 This is the number of the mighty men whom David had: Jashobeam, the son of a Hachmonite, the chief of the thirty; he lifted up his spear against three hundred and killed them at one time.
Ga jerin sunayen jarumawan Dawuda. Yashobeyam wani ɗan Hakmoni, shi ne babban shugaba; ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe a ƙarawa guda kawai.
12 After him was Eleazar the son of Dodo, the Ahohite, who was one of the three mighty men.
Biye da shi, shi ne Eleyazar ɗan Dodo mutumin Aho, ɗaya daga cikin jarumawa uku.
13 He was with David at Pasdammim, and there the Philistines were gathered together to battle, where there was a plot of ground full of barley; and the people fled from before the Philistines.
Yana tare da Dawuda a Fas Dammim sa’ad da Filistiyawa suka taru can don yaƙi. A wani wuri inda akwai gona cike da sha’ir, sojoji suka gudu daga Filistiyawa.
14 They stood in the middle of the plot, defended it, and killed the Philistines; and the LORD saved them by a great victory.
Sai shi da Dawuda suka shiga gonar sha’ir ɗin, suka tsaya ciki don su tsare ta. Suka ragargaza Filistiyawa, Ubangiji kuma ya kawo babban nasara.
15 Three of the thirty chief men went down to the rock to David, into the cave of Adullam; and the army of the Philistines were encamped in the valley of Rephaim.
Wata rana uku cikin manyan mutanen nan talatin suka gangara wurin Dawuda zuwa dutse a kogon Adullam, yayinda ƙungiyar Filistiyawa suke sansani a Kwarin Refayim.
16 David was then in the stronghold, and the garrison of the Philistines was in Bethlehem at that time.
A lokacin Dawuda yana cikin mafaka, sojojin Filistiyawa kuma suna a Betlehem.
17 David longed, and said, “Oh, that someone would give me water to drink from the well of Bethlehem, which is by the gate!”
Dawuda ya ji marmarin ruwan sha sai ya ce, “Kash, a ce wani zai sami mini ruwan sha daga rijiya kusa da ƙofar Betlehem mana!”
18 The three broke through the army of the Philistines, and drew water out of the well of Bethlehem that was by the gate, took it, and brought it to David; but David would not drink any of it, but poured it out to the LORD,
Sai Ukun suka kutsa kai cikin sansanin Filistiyawa, suka ja ruwa daga rijiyar da take kusa da ƙofar Betlehem suka ɗauko shi suka kawo wa Dawuda. Amma ya ƙi yă sha; a maimako, sai ya zubar da shi a gaban Ubangiji.
19 and said, “My God forbid me, that I should do this! Shall I drink the blood of these men who have put their lives in jeopardy?” For they risked their lives to bring it. Therefore he would not drink it. The three mighty men did these things.
Ya ce, “Allah yă sawwaƙe in yi haka, ya kamata in sha jinin waɗannan mutanen da suka yi kasai da rayukansu?” Domin sun yi kasai da rayukansu don su dawo da shi, Dawuda bai sha shi ba. Irin abubuwan da jarumawa ukun nan suka yi ke nan.
20 Abishai, the brother of Joab, was chief of the three; for he lifted up his spear against three hundred and killed them, and had a name amongst the three.
Abishai ɗan’uwan Yowab shi ma babba ne cikin Ukun nan. Ya ɗaga māshinsa a kan mutum ɗari uku, waɗanda ya kashe, ya kuma zama sananne kamar Ukun.
21 Of the three, he was more honourable than the two, and was made their captain; however he wasn’t included in the three.
Aka ninka girmama shi bisa Ukun, sai ya zama shugaba, ko da yake ba a haɗa shi a cikinsu ba.
22 Benaiah the son of Jehoiada, the son of a valiant man of Kabzeel, who had done mighty deeds, killed the two sons of Ariel of Moab. He also went down and killed a lion in the middle of a pit on a snowy day.
Benahiya ɗan Yehohiyada shi ma wani barden yaƙi ne daga Kabzeyel, wanda ya yi manyan abubuwa. Ya bugi gwanayen Mowab biyu. Ya kuma gangara zuwa cikin rami a ranar da aka yi dusar ƙanƙara ya kashe zaki.
23 He killed an Egyptian, a man of great stature, five cubits high. In the Egyptian’s hand was a spear like a weaver’s beam; and he went down to him with a staff, plucked the spear out of the Egyptian’s hand, and killed him with his own spear.
Ya kuma kashe wani mutumin Masar mai tsayi ƙafa bakwai da rabi. Ko da yake mutumin Masar yana da māshi kamar sandan masaƙa a hannunsa, Benahiya ya yaƙe shi da kulki. Ya ƙwace māshin daga hannun mutumin Masar ya kuma kashe shi da māshin nan nasa.
24 Benaiah the son of Jehoiada did these things and had a name amongst the three mighty men.
Irin abubuwan da Benahiya ɗan Yehohiyada ya yi ke nan; shi ma sananne ne kamar waɗannan jarumawa uku.
25 Behold, he was more honourable than the thirty, but he didn’t attain to the three; and David set him over his guard.
Aka ɗauka shi da bangirma fiye da Talatin nan, amma ba a haɗa shi cikin Ukun ba. Dawuda kuwa ya sa shi yă lura da masu tsaron lafiyarsa.
26 The mighty men of the armies also include Asahel the brother of Joab, Elhanan the son of Dodo of Bethlehem,
Jarumawan nan su ne, Asahel ɗan’uwan Yowab, Elhanan ɗan Dodo daga Betlehem,
27 Shammoth the Harorite, Helez the Pelonite,
Shammot mutumin Haror, Helez mutumin Felon,
28 Ira the son of Ikkesh the Tekoite, Abiezer the Anathothite,
Ira ɗan Ikkesh daga Tekowa, Abiyezer daga Anatot,
29 Sibbecai the Hushathite, Ilai the Ahohite,
Sibbekai mutumin Husha, Ilai mutumin Aho,
30 Maharai the Netophathite, Heled the son of Baanah the Netophathite,
Maharai mutumin Netofa, Heled ɗan Ba’ana mutumin Netofa,
31 Ithai the son of Ribai of Gibeah of the children of Benjamin, Benaiah the Pirathonite,
Ittai ɗan Ribai daga Gibeya a Benyamin, Benahiya mutumin Firaton,
32 Hurai of the brooks of Gaash, Abiel the Arbathite,
Hurai daga kogunan Ga’ash, Abiyel mutumin Arba,
33 Azmaveth the Baharumite, Eliahba the Shaalbonite,
Azmawet mutumin Harum, Eliyaba mutumin Sha’albo,
34 the sons of Hashem the Gizonite, Jonathan the son of Shagee the Hararite,
’ya’yan Hashem mutumin Gizon maza, Yonatan ɗan Shageye mutumin Harar,
35 Ahiam the son of Sacar the Hararite, Eliphal the son of Ur,
Ahiyam ɗan Sakar mutumin Harar, Elifal ɗan Ur,
36 Hepher the Mecherathite, Ahijah the Pelonite,
Hefer mutumin Mekerat, Ahiya mutumin Felon,
37 Hezro the Carmelite, Naarai the son of Ezbai,
Hezro mutumin Karmel, Na’arai ɗan Ezbai,
38 Joel the brother of Nathan, Mibhar the son of Hagri,
Yowel ɗan’uwan Natan, Mibhar ɗan Hagiri,
39 Zelek the Ammonite, Naharai the Berothite (the armour bearer of Joab the son of Zeruiah),
Zelek mutumin Ammon Naharai Baroti, mai ɗaukar kayan yaƙin Yowab ɗan Zeruhiya,
40 Ira the Ithrite, Gareb the Ithrite,
Ira mutumin Itra, Gareb mutumin Itra,
41 Uriah the Hittite, Zabad the son of Ahlai,
Uriya mutumin Hitti Zabad ɗan Alai,
42 Adina the son of Shiza the Reubenite (a chief of the Reubenites), and thirty with him,
Adina ɗan Shiza mutumin Ruben, wanda shi ne babba na mutanen Ruben, kuma talatin suna tare da shi,
43 Hanan the son of Maacah, Joshaphat the Mithnite,
Hanan ɗan Ma’aka, Yoshafat mutumin Mit,
44 Uzzia the Ashterathite, Shama and Jeiel the sons of Hotham the Aroerite,
Uzziya mutumin Ashtarot, Shama da Yehiyel’ya’yan Hotam mutumin Arower maza,
45 Jediael the son of Shimri, and Joha his brother, the Tizite,
Yediyayel ɗan Shimri, ɗan’uwansa Yoha mutumin Tiz,
46 Eliel the Mahavite, and Jeribai, and Joshaviah, the sons of Elnaam, and Ithmah the Moabite,
Eliyel mutumin Ma’aha, Yeribai da Yoshawiya’ya’yan Elna’am maza, Itma mutumin Mowab,
47 Eliel, Obed, and Jaasiel the Mezobaite.
Eliyel, Obed da Ya’asiyel mutumin Mezob.

< 1 Chronicles 11 >