< Psalms 71 >

1 In you, Yahweh, I take refuge. Never let me be disappointed.
A gare ka, ya Ubangiji, na nemi mafaka; kada ka taɓa sa in sha kunya.
2 Deliver me in your righteousness, and rescue me. Turn your ear to me, and save me.
Ka kuɓutar da ni ka cece ni cikin adalcinka; ka juya kunnenka gare ni ka kuma cece ni.
3 Be to me a rock of refuge to which I may always go. Give the command to save me, for you are my rock and my fortress.
Ka zama dutsena da kagarata, inda kullum zan je. Ka ba da umarni a cece ni, gama kai ne dutsen ɓuyana da katangata.
4 Rescue me, my God, from the hand of the wicked, from the hand of the unrighteous and cruel man.
Ka cece ni, ya Allahna, daga hannun mugaye, da kuma daga ikon mugaye da masu mugunta.
5 For you are my hope, Lord Yahweh, my confidence from my youth.
Gama kai ne abin sa zuciyata, ya Ubangiji Mai Iko Duka, ƙarfin zuciyata tun ina yaro.
6 I have relied on you from the womb. You are he who took me out of my mother’s womb. I will always praise you.
Daga haihuwa na dogara gare ka; kai ka kawo ni daga cikin mahaifiyata. Kullayaumi zan yabe ka.
7 I am a marvel to many, but you are my strong refuge.
Na zama kamar abin sa zuciya ga yawanci, amma kai ne katangata mai ƙarfi.
8 My mouth shall be filled with your praise, with your honor all day long.
Bakina ya cika da yabonka, ina furta darajarka dukan yini.
9 Don’t reject me in my old age. Don’t forsake me when my strength fails.
Kada ka yar da ni sa’ad da na tsufa; kada ka yashe ni sa’ad da ƙarfina ya ƙare.
10 For my enemies talk about me. Those who watch for my soul conspire together,
Gama abokan gābana suna magana a kaina; waɗanda suke jira su kashe ni suna haɗa baki tare.
11 saying, “God has forsaken him. Pursue and take him, for no one will rescue him.”
Suna cewa, “Allah ya yashe shi; mu fafare shi mu kama shi, gama ba wanda zai kuɓutar da shi.”
12 God, don’t be far from me. My God, hurry to help me.
Kada ka yi nisa da ni, ya Allah; zo da sauri, ya Allahna, ka taimake ni.
13 Let my accusers be disappointed and consumed. Let them be covered with disgrace and scorn who want to harm me.
Bari masu zagina su hallaka da kunya; bari waɗanda suke so su cutar da ni su sha ba’a da kuma kunya.
14 But I will always hope, and will add to all of your praise.
Amma game da ni, kullayaumi zan kasance da sa zuciya; zan yabe ka sau da sau.
15 My mouth will tell about your righteousness, and of your salvation all day, though I don’t know its full measure.
Bakina zai ba da labarin adalcinka, zai yi maganar cetonka dukan yini, ko da yake ban san yawansa ba.
16 I will come with the mighty acts of the Lord Yahweh. I will make mention of your righteousness, even of yours alone.
Zan zo in furta in kuma yi shelar ayyukanka masu girma, ya Ubangiji Mai Iko Duka; zan yi shelar adalcinka, naka kaɗai.
17 God, you have taught me from my youth. Until now, I have declared your wondrous works.
Tun ina yaro, ya Allah, ka koya mini har wa yau ina furta ayyukanka masu banmamaki.
18 Yes, even when I am old and gray-haired, God, don’t forsake me, until I have declared your strength to the next generation, your might to everyone who is to come.
Ko sa’ad da na tsufa da furfura, kada ka yashe ni, ya Allah, sai na furta ikonka ga tsara mai zuwa, ƙarfinka ga dukan waɗanda suke zuwa.
19 God, your righteousness also reaches to the heavens. You have done great things. God, who is like you?
Adalcinka ya kai sararin sama, ya Allah, kai da ka yi manyan abubuwa. Wane ne kamar ka, ya Allah?
20 You, who have shown us many and bitter troubles, you will let me live. You will bring us up again from the depths of the earth.
Ko da yake ka sa na ga wahaloli, masu yawa da kuma masu ɗaci, za ka sāke mayar mini da rai; daga zurfafan duniya za ka sāke tā da ni.
21 Increase my honor and comfort me again.
Za ka ƙara girmana ka sāke ta’azantar da ni.
22 I will also praise you with the harp for your faithfulness, my God. I sing praises to you with the lyre, Holy One of Israel.
Zan yabe ka da garaya saboda amincinka, ya Allah; zan rera yabo gare ka da molo, Ya Mai Tsarki na Isra’ila.
23 My lips shall shout for joy! My soul, which you have redeemed, sings praises to you!
Leɓunana za su yi sowa don farin ciki sa’ad da na rera yabo gare ka, ni, wanda ka fansa.
24 My tongue will also talk about your righteousness all day long, for they are disappointed, and they are confounded, who want to harm me.
Harshena zai ba da labarin ayyukanka masu adalci dukan yini, gama waɗanda suka so su cutar da ni sun sha kunya suka kuma rikice.

< Psalms 71 >