< Psalms 144 >

1 By David. Blessed be Yahweh, my rock, who trains my hands to war, and my fingers to battle—
Ta Dawuda. Yabo ya tabbata ga Ubangiji dutsena, wanda ya horar da hannuwana don yaƙi, yatsotsina don faɗa.
2 my loving kindness, my fortress, my high tower, my deliverer, my shield, and he in whom I take refuge, who subdues my people under me.
Shi ne Allah mai ƙaunata da kuma kagarata, katangata da mai cetona, garkuwata, wanda nake neman mafaka daga gare shi, wanda ya sa mutane a ƙarƙashina.
3 Yahweh, what is man, that you care for him? Or the son of man, that you think of him?
Ya Ubangiji, wane ne mutum da ka kula da shi, ɗan mutum da har za ka yi tunaninsa?
4 Man is like a breath. His days are like a shadow that passes away.
Mutum yana kama da numfashi; kwanakinsa suna wucewa kamar inuwa.
5 Part your heavens, Yahweh, and come down. Touch the mountains, and they will smoke.
Ka tsage sammanka, ya Ubangiji, ka sauko; ka taɓa duwatsu, domin su yi hayaƙi.
6 Throw out lightning, and scatter them. Send out your arrows, and rout them.
Ka aiko da walƙiya ka watsar da abokan gāba; ka karɓa kibiyoyinka ka sa su gudu.
7 Stretch out your hand from above, rescue me, and deliver me out of great waters, out of the hands of foreigners,
Ka miƙa hannunka daga bisa; ka cece ni ka kuma kuɓutar da ni daga manyan ruwaye, daga hannuwan baƙi
8 whose mouths speak deceit, whose right hand is a right hand of falsehood.
waɗanda bakunansu sun cika da ƙarya, waɗanda hannuwansu na dama masu ruɗu ne.
9 I will sing a new song to you, God. On a ten-stringed lyre, I will sing praises to you.
Zan rera sabuwar waƙa gare ka, ya Allah; a kan molo mai tsirkiya goma zan yi maka kiɗi,
10 You are he who gives salvation to kings, who rescues David, his servant, from the deadly sword.
ga Wannan wanda yake ba wa sarakuna nasara, wanda ya cece bawansa Dawuda. Daga takobin kisa.
11 Rescue me, and deliver me out of the hands of foreigners, whose mouths speak deceit, whose right hand is a right hand of falsehood.
Ka cece ni ka kuma kuɓutar da ni daga hannuwan baƙi waɗanda bakunansu sun cika da ƙarya, waɗanda hannuwansu na dama masu ruɗu ne.
12 Then our sons will be like well-nurtured plants, our daughters like pillars carved to adorn a palace.
Ta haka’ya’yanmu maza a ƙuruciyarsu za su zama kamar tsire-tsiren da aka kula da su,’ya’yanmu mata kuma za su zama kamar ginshiƙai da sassaƙa don adon fada.
13 Our barns are full, filled with all kinds of provision. Our sheep produce thousands and ten thousands in our fields.
Rumbunanmu za su cika da kowane irin tanadi. Tumakinmu za su ƙaru ninki dubu, ninki dubu goma-goma a filayenmu;
14 Our oxen will pull heavy loads. There is no breaking in, and no going away, and no outcry in our streets.
shanunmu za su ja kaya masu nauyi. Ba za a sami tashin hankali a katangarmu ba, ba zuwan zaman bauta, ba jin kukan damuwa a titunanmu.
15 Happy are the people who are in such a situation. Happy are the people whose God is Yahweh.
Masu albarka ne mutanen da wannan zai zama haka; masu albarka ne mutanen da Allah ne Ubangiji.

< Psalms 144 >