< Matthew 11 >

1 When Jesus had finished directing his twelve disciples, he departed from there to teach and preach in their cities.
Bayan Yesu ya gama yi wa almajiransa gargadi, sai ya bar wannan wuri, ya tafi biranensu domin yayi koyorwa, da wa'azi.
2 Now when John heard in the prison the works of Christ, he sent two of his disciples
Da Yahaya mai baftisma ya ji daga kurkuku irin ayyukan da Yesu ke yi, sai ya aika sako ta wurin almajiransa.
3 and said to him, “Are you he who comes, or should we look for another?”
Ya ce masa. “Kai ne mai zuwa”? ko mu sa ido ga wani.
4 Jesus answered them, “Go and tell John the things which you hear and see:
Yesu ya amsa ya ce masu, “Ku je ku gaya wa Yahaya abin da ku ka gani da abin da ku ka ji.
5 the blind receive their sight, the lame walk, the lepers are cleansed, the deaf hear, the dead are raised up, and the poor have good news preached to them.
Makafi suna samun ganin gari, guragu na tafiya, ana tsarkake kutare, kurame na jin magana kuma, ana tada matattu, mabukata kuma ana ba su bishara.
6 Blessed is he who finds no occasion for stumbling in me.”
Kuma mai albarka ne wanda baya tuntube sabili da ni.
7 As these went their way, Jesus began to say to the multitudes concerning John, “What did you go out into the wilderness to see? A reed shaken by the wind?
Bayan wadannan sun tafi, sai Yesu ya fara wa jama'a jawabi game da Yahaya mai baftisma, yana cewa, “Me ake zuwa gani a jeji - ciyawa ce da iska ke busawa?
8 But what did you go out to see? A man in soft clothing? Behold, those who wear soft clothing are in kings’ houses.
Shin menene kuke zuwa gani a jeji - mutum mai sanye da tufafi masu laushi? Hakika, masu sa tufafi masu laushi suna zaune ne a fadar sarakuna.
9 But why did you go out? To see a prophet? Yes, I tell you, and much more than a prophet.
Amma me ku ke zuwa gani, annabi? Hakika ina fada maku, fiye ma da annabi.
10 For this is he, of whom it is written, ‘Behold, I send my messenger before your face, who will prepare your way before you.’
Wannan shine wanda aka rubuta game da shi, 'Duba, ina aika manzona, wanda za ya tafi gabanka domin ya shirya maka hanya inda za ka bi'.
11 Most certainly I tell you, among those who are born of women there has not arisen anyone greater than John the Baptizer; yet he who is least in the Kingdom of Heaven is greater than he.
Ina gaya maku gaskiya, cikin wadanda mata suka haifa, babu mai girma kamar Yahaya mai baftisma. Amma mafi kankanta a mulkin sama ya fi shi girma.
12 From the days of John the Baptizer until now, the Kingdom of Heaven suffers violence, and the violent take it by force.
Tun daga kwanakin Yahaya mai baftisma zuwa yanzu, mulkin sama yana shan gwagwarmaya, masu husuma kuma su kan kwace shi da karfi.
13 For all the prophets and the law prophesied until John.
Gama dukan annabawa da shari'a sun yi annabci har zuwa lokacin Yahaya.
14 If you are willing to receive it, this is Elijah, who is to come.
kuma in zaku karba, wannan shine Iliya wanda za ya zo.
15 He who has ears to hear, let him hear.
Wanda ke da kunnuwan ji, ya ji.
16 “But to what shall I compare this generation? It is like children sitting in the marketplaces, who call to their companions
Da me zan kwatanta wannan zamani? Ya na kamar yara masu wasa a kasuwa, sun zauna suna kiran juna
17 and say, ‘We played the flute for you, and you didn’t dance. We mourned for you, and you didn’t lament.’
suna cewa mun busa maku sarewa baku yi rawa ba, mun yi makoki, baku yi kuka ba.
18 For John came neither eating nor drinking, and they say, ‘He has a demon.’
Gama Yahaya ya zo, baya cin gurasa ko shan ruwan inabi, sai aka ce, “Yana da aljannu”.
19 The Son of Man came eating and drinking, and they say, ‘Behold, a gluttonous man and a drunkard, a friend of tax collectors and sinners!’ But wisdom is justified by her children.”
Dan mutum ya zo yana ci yana sha, sai aka ce, 'Duba, ga mai hadama, mashayi kuma, abokin masu karbar haraji da masu zunubi!' Amma hikima, ta wurin aikin ta ake tabbatar da ita.
20 Then he began to denounce the cities in which most of his mighty works had been done, because they didn’t repent.
Sannan Yesu ya fara tsautawa biranen nan inda ya yi yawancin ayukansa, domin ba su tuba ba.
21 “Woe to you, Chorazin! Woe to you, Bethsaida! For if the mighty works had been done in Tyre and Sidon which were done in you, they would have repented long ago in sackcloth and ashes.
“Kaiton ki Korasinu, kaiton ki Batsaida! In da an yi irin ayuka masu ban mamaki a Taya da Sidon! Yadda aka yi a cikinku, da tuni sun tuba suna sanye da tsumma da yafa toka.
22 But I tell you, it will be more tolerable for Tyre and Sidon on the day of judgment than for you.
Amma zai zama da sauki a kan Taya da Sidon a ranar shari'a fiye da ku.
23 You, Capernaum, who are exalted to heaven, you will go down to Hades. For if the mighty works had been done in Sodom which were done in you, it would have remained until today. (Hadēs g86)
Ke kafarnahum, kina tsammani za a daukaka ki har zuwa sama? A'a za a saukar da ke kasa zuwa hades. Gama in da an yi irin al'ajiban da aka yi a cikin ki a Sodom, da tana nan har yanzu. (Hadēs g86)
24 But I tell you that it will be more tolerable for the land of Sodom on the day of judgment, than for you.”
Amma ina ce maku, za a saukaka wa Sodom a ranar shari'a fiye da ku.”
25 At that time, Jesus answered, “I thank you, Father, Lord of heaven and earth, that you hid these things from the wise and understanding, and revealed them to infants.
A wannan lokaci Yesu ya ce, “Ina yabon ka, ya Uba, Ubangijin sama da kasa, domin ka boye wa masu hikima da fahimta wadannan abubuwa, ka bayyana wa marasa sani, kamar kananan yara.
26 Yes, Father, for so it was well-pleasing in your sight.
I, ya Uba gama wannan shine ya yi daidai a gare ka.
27 All things have been delivered to me by my Father. No one knows the Son, except the Father; neither does anyone know the Father, except the Son and he to whom the Son desires to reveal him.
An mallaka mani dukan abu daga wurin Ubana. Sannan babu wanda ya san Dan, sai Uban, babu kuma wanda ya san Uban, sai Dan, da duk wanda ya so ya bayyana masa.
28 “Come to me, all you who labor and are heavily burdened, and I will give you rest.
Ku zo gare ni, dukanku masu wahala da fama da nauyin kaya, ni kuma zan ba ku hutawa.
29 Take my yoke upon you and learn from me, for I am gentle and humble in heart; and you will find rest for your souls.
Ku dauki karkiya ta ku koya daga gare ni, gama ni mai tawali'u ne da saukin hali a zuciya, sannan zaku sami hutawa ga rayukanku.
30 For my yoke is easy, and my burden is light.”
Gama karkiyata mai sauki ce, kaya na kuma ba shi da nauyi.”

< Matthew 11 >