< Leviticus 24 >

1 Yahweh spoke to Moses, saying,
Ubangiji ya ce wa Musa,
2 “Command the children of Israel, that they bring to you pure olive oil beaten for the light, to cause a lamp to burn continually.
“Ka umarci Isra’ilawa su kawo tsabtataccen mai na zaitun da aka matse, don ƙuna fitilun yadda harshen wutar ba zai taɓa mutuwa ba.
3 Outside of the veil of the Testimony, in the Tent of Meeting, Aaron shall keep it in order from evening to morning before Yahweh continually. It shall be a statute forever throughout your generations.
Za a ajiye su waje da labulen Wuri Mafi Tsarki a Tentin Sujada, Haruna zai riƙa kula da fitilun a gaban Ubangiji, daga yamma zuwa safiya. Wannan za tă zama dawwammamiyar farilla wa tsararraki masu zuwa.
4 He shall keep in order the lamps on the pure gold lamp stand before Yahweh continually.
Dole a ci gaba da shirya fitilu a kan wurin ajiye fitila na zinariya, a gaban Ubangiji.
5 “You shall take fine flour, and bake twelve cakes of it: two tenths of an ephah shall be in one cake.
“Ɗauki gari mai laushi a gasa dunƙulen burodi goma sha biyu, a yi amfani da humushi biyu na garwan gari don kowace burodi.
6 You shall set them in two rows, six on a row, on the pure gold table before Yahweh.
A shirya su jeri biyu, guda shida a kowane jeri a kan teburin da aka yi da zinariya zalla, a gaban Ubangiji.
7 You shall put pure frankincense on each row, that it may be to the bread for a memorial, even an offering made by fire to Yahweh.
Za a zuba turare a kowane layin dunƙulen burodin don yă kasance abin tunawa a bisa burodin. Turaren zai ƙone a madadin burodin don yă zama kamar hadayar da aka miƙa da wuta ga Ubangiji.
8 Every Sabbath day he shall set it in order before Yahweh continually. It is an everlasting covenant on the behalf of the children of Israel.
Za a shirya wannan gurasa a gaban Ubangiji kowane Asabbaci, a madadin Isra’ilawa a matsayin madawwamin alkawari.
9 It shall be for Aaron and his sons. They shall eat it in a holy place; for it is most holy to him of the offerings of Yahweh made by fire by a perpetual statute.”
Wannan burodin zai zama na Haruna da’ya’yansa maza, waɗanda za su ci a tsattsarkan wuri, gama sashe ne mafi tsarki na rabonsu na kullum na hadayar da aka yi da wuta ga Ubangiji.”
10 The son of an Israelite woman, whose father was an Egyptian, went out among the children of Israel; and the son of the Israelite woman and a man of Israel strove together in the camp.
To, ɗan wata mutuniyar Isra’ila wanda mahaifinsa mutumin Masar ne, ya je cikin Isra’ilawa, sai faɗa ta tashi tsakaninsa da wani mutumin Isra’ila a cikin sansani.
11 The son of the Israelite woman blasphemed the Name, and cursed; and they brought him to Moses. His mother’s name was Shelomith, the daughter of Dibri, of the tribe of Dan.
Ɗan mutuniyar Isra’ila ya saɓi Sunan Ubangiji, ya kuma la’ana shi, saboda haka aka kawo shi wa Musa. (Sunan mahaifiyarsa Shelomit ne,’yar Dibri na kabilar Dan.)
12 They put him in custody until Yahweh’s will should be declared to them.
Suka sa shi a gidan tsaro sai lokacin da nufin Ubangiji ya nuna musu abin da za su yi da shi.
13 Yahweh spoke to Moses, saying,
Sai Ubangiji ya ce wa Musa,
14 “Bring him who cursed out of the camp; and let all who heard him lay their hands on his head, and let all the congregation stone him.
“Ka kai mai saɓon nan waje da sansani. Duk waɗanda suka ji maganar da mai saɓon nan ya yi su ɗibiya hannuwansu a kansa, taron jama’a kuwa gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu.
15 You shall speak to the children of Israel, saying, ‘Whoever curses his God shall bear his sin.
Faɗa wa Isra’ilawa cewa, ‘Duk wanda ya zagi Allahnsa, alhakin zai rataya a wuyansa,
16 He who blasphemes Yahweh’s name, he shall surely be put to death. All the congregation shall certainly stone him. The foreigner as well as the native-born shall be put to death when he blasphemes the Name.
duk wanda ya saɓi sunan Ubangiji, dole a kashe shi. Dole jama’a gaba ɗaya su jajjefe shi da duwatsu. Ko baƙo, ko haifaffen ɗan ƙasa, sa’ad da ya saɓi Sunan Ubangiji, dole a kashe shi.
17 “‘He who strikes any man mortally shall surely be put to death.
“‘Duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
18 He who strikes an animal mortally shall make it good, life for life.
Duk wanda ya kashe dabbar wani, dole yă biya, rai domin rai.
19 If anyone injures his neighbor, it shall be done to him as he has done:
Duk wanda ya yi wa maƙwabcinsa rauni, sai a yi masa abin da ya yi;
20 fracture for fracture, eye for eye, tooth for tooth. It shall be done to him as he has injured someone.
karaya don karaya, ido don ido, haƙori don haƙori. Kamar yadda ya yi wa wani rauni, shi ma a yi masa.
21 He who kills an animal shall make it good; and he who kills a man shall be put to death.
Duk wanda ya kashe dabba, dole yă biya, amma duk wanda ya kashe mutum, dole a kashe shi.
22 You shall have one kind of law for the foreigner as well as the native-born; for I am Yahweh your God.’”
Za ku kasance da doka iri ɗaya wa baƙo da kuma wa haifaffen ɗan ƙasa. Ni ne Ubangiji Allahnku.’”
23 Moses spoke to the children of Israel; and they brought him who had cursed out of the camp, and stoned him with stones. The children of Israel did as Yahweh commanded Moses.
Sai Musa ya yi wa Isra’ilawa magana, suka kuwa kai mai saɓon waje da sansani, suka jajjefi shi da duwatsu. Isra’ilawa suka yi yadda Ubangiji ya umarci Musa.

< Leviticus 24 >