< John 4 >

1 Therefore when the Lord knew that the Pharisees had heard that Jesus was making and baptizing more disciples than John
Da Yesu ya sani cewa Farisawa sun ji cewa yana samun almajirai yana kuma yi masu baftisma fiye da Yahaya
2 (although Jesus himself didn’t baptize, but his disciples),
(ko da shike ba Yesu da kansa ke yin baftismar ba, amma almajiransa ne),
3 he left Judea and departed into Galilee.
ya bar Yahudiya ya koma Galili.
4 He needed to pass through Samaria.
Amma ya zamar masa dole ya ratsa ta Samariya.
5 So he came to a city of Samaria called Sychar, near the parcel of ground that Jacob gave to his son Joseph.
Ya zo wani birnin Samariya, mai suna Sika, kusa da filin da Yakubu ya ba dansa Yusufu.
6 Jacob’s well was there. Jesus therefore, being tired from his journey, sat down by the well. It was about the sixth hour.
Rijiyar Yakubu na wurin. Da Yesu ya gaji da tafiyarsa sai ya zauna gefen rijiyar. Kusan karfe goma sha biyu na rana ne.
7 A woman of Samaria came to draw water. Jesus said to her, “Give me a drink.”
Wata mace, Ba-Samariya ta zo domin ta dibi ruwa, sai Yesu ya ce mata, “Ba ni ruwa in sha.”
8 For his disciples had gone away into the city to buy food.
Gama almajiransa sun tafi cikin gari don sayen abinci.
9 The Samaritan woman therefore said to him, “How is it that you, being a Jew, ask for a drink from me, a Samaritan woman?” (For Jews have no dealings with Samaritans.)
Sai ba-Samariyar tace masa, “Yaya kai da kake Bayahude kake tambaya ta ruwan sha, ni da nike 'yar Samariya?” Domin Yahudawa ba su harka da Samariyawa.
10 Jesus answered her, “If you knew the gift of God, and who it is who says to you, ‘Give me a drink,’ you would have asked him, and he would have given you living water.”
Sai Yesu ya amsa yace mata, “In da kin san kyautar Allah, da shi wanda yake ce da ke, 'Ba ni ruwan sha,' da kin roke shi, sai kuma ya ba ki ruwan rai.”
11 The woman said to him, “Sir, you have nothing to draw with, and the well is deep. So where do you get that living water?
Matar tace masa, “Mallam, ga shi ba ka da guga, kuma rijiyar tana da zurfi. Ina za ka samu ruwan rai?
12 Are you greater than our father Jacob, who gave us the well and drank from it himself, as did his children and his livestock?”
Ai ba ka fi Ubanmu Yakubu ba, ko ka fi shi, shi wanda ya ba mu rijiyar, shi kansa kuma ya sha daga cikin ta, haka kuma 'ya'yansa da shanunsa?”
13 Jesus answered her, “Everyone who drinks of this water will thirst again,
Yesu ya amsa yace mata, “duk wanda ya sha daga wannan ruwan zai sake jin kishi,
14 but whoever drinks of the water that I will give him will never thirst again; but the water that I will give him will become in him a well of water springing up to eternal life.” (aiōn g165, aiōnios g166)
amma duk wanda ya sha daga ruwa da zan ba shi ba zai sake jin kishi ba. Maimakon haka, ruwan da zan bashi zai zama mabulbular ruwa a cikinsa wanda ke bulbula zuwa rai madawwami.” (aiōn g165, aiōnios g166)
15 The woman said to him, “Sir, give me this water, so that I don’t get thirsty, neither come all the way here to draw.”
Matar tace masa, “Mallam, ka ba ni wannan ruwa yadda ba zan kara jin kishi ba ba kuma sai na zo nan don in dibi ruwa ba.”
16 Jesus said to her, “Go, call your husband, and come here.”
Yesu ya ce mata, “Je, ki kira maigidanki ku zo nan tare.”
17 The woman answered, “I have no husband.” Jesus said to her, “You said well, ‘I have no husband,’
Matar ta amsa tace masa, “Ba ni da miji.” Yesu yace, “Kin fadi daidai da kika ce, 'ba ni da miji,'
18 for you have had five husbands; and he whom you now have is not your husband. This you have said truly.”
domin kin auri mazaje har biyar, kuma wanda kike da shi yanzu ba mijin ki bane. Abinda kika fada gaskiya ne.”
19 The woman said to him, “Sir, I perceive that you are a prophet.
Matar tace masa, “Mallam, Na ga kai annabi ne.
20 Our fathers worshiped in this mountain, and you Jews say that in Jerusalem is the place where people ought to worship.”
Ubaninmu sun yi sujada a wannan dutse, amma kun ce Urushalima ce wurin da ya kamata mutane su yi sujada.”
21 Jesus said to her, “Woman, believe me, the hour is coming when neither in this mountain nor in Jerusalem will you worship the Father.
Yesu ya ce mata, “Mace, ki gaskata ni, cewa lokaci na zuwa wanda ba za ku yi wa Uban sujada ba ko akan wannan dutse ko a Urushalima.
22 You worship that which you don’t know. We worship that which we know; for salvation is from the Jews.
Ku kuna bauta wa abinda ba ku sani ba. Mu muna bauta wa abinda muka sani, gama ceto daga Yahudawa yake.
23 But the hour comes, and now is, when the true worshipers will worship the Father in spirit and truth, for the Father seeks such to be his worshipers.
Sai dai, sa'a tana zuwa, har ma ta yi, wadda masu sujada na gaskiya za su yi wa Uba sujada a cikin ruhu da gaskiya, domin irin wadannan ne Uban ke nema su zama masu yi masa sujada.
24 God is spirit, and those who worship him must worship in spirit and truth.”
Allah Ruhu ne, kuma mutanen da ke yi masa sujada, dole su yi sujada cikin ruhu da gaskiya.”
25 The woman said to him, “I know that Messiah is coming, he who is called Christ. When he has come, he will declare to us all things.”
Matar ta ce masa, “Na san Almasihu na zuwa (wanda ake kira Kristi). Sa'adda ya zo, zai bayyana mana kowane abu.
26 Jesus said to her, “I am he, the one who speaks to you.”
Yesu ya ce mata, “Ni ne shi, wanda ke yi maki magana.”
27 Just then, his disciples came. They marveled that he was speaking with a woman; yet no one said, “What are you looking for?” or, “Why do you speak with her?”
A daidai wannan lokaci, almajiransa suka dawo. Suna ta mamakin dalilin da yasa yake magana da mace, amma babu wanda yace, “Me kake so?” Ko kuma, “Don me ka ke magana da ita?”
28 So the woman left her water pot, went away into the city, and said to the people,
Sai matar ta bar tulunta, ta koma cikin gari, tace wa mutanen,
29 “Come, see a man who told me everything that I have done. Can this be the Christ?”
“Ku zo ku ga wani mutum wanda ya gaya mani duk wani abu da na taba yi. Wannan dai ba Almasihun bane, ko kuwa?”
30 They went out of the city, and were coming to him.
Suka bar garin suka zo wurinsa.
31 In the meanwhile, the disciples urged him, saying, “Rabbi, eat.”
A wannan lokacin, almajiransa suna rokansa, cewa, “Mallam, ka ci.”
32 But he said to them, “I have food to eat that you don’t know about.”
Amma ya ce masu, “ina da abinci da ba ku san komai akai ba.”
33 The disciples therefore said to one another, “Has anyone brought him something to eat?”
Sai almajiran suka ce da junansu, “Babu wanda ya kawo masa wani abu ya ci, ko akwai ne?”
34 Jesus said to them, “My food is to do the will of him who sent me and to accomplish his work.
Yesu ya ce masu, “Abincina shine in yi nufin wanda ya aiko ni, in kuma cika aikinsa.
35 Don’t you say, ‘There are yet four months until the harvest’? Behold, I tell you, lift up your eyes and look at the fields, that they are white for harvest already.
Ba ku kan ce, 'akwai wata hudu tukuna kafin girbi ya zo ba?' Ina gaya maku, daga idanunku ku ga gonakin, sun rigaya sun isa girbi.
36 He who reaps receives wages and gathers fruit to eternal life, that both he who sows and he who reaps may rejoice together. (aiōnios g166)
Shi wanda ke girbi yakan karbi sakamako ya kuma tattara amfanin gona zuwa rai na har abada, ta haka shi mai shuka da shi mai girbi za su yi farinciki tare. (aiōnios g166)
37 For in this the saying is true, ‘One sows, and another reaps.’
Gama cikin wannan maganar take, 'Wani na shuka, wani kuma na girbi.'
38 I sent you to reap that for which you haven’t labored. Others have labored, and you have entered into their labor.”
Na aike ku ku yi girbin abinda ba ku yi aiki a kai ba. Wandansu sun yi aiki, ku kuma kun shiga cikin wahalarsu.
39 From that city many of the Samaritans believed in him because of the word of the woman, who testified, “He told me everything that I have done.”
Yawancin Samariyawan da ke wannan birni suka gaskata da shi sabili da labarin matar data bada shaida, “Ya gaya mani duk abinda na taba yi.”
40 So when the Samaritans came to him, they begged him to stay with them. He stayed there two days.
To sa'adda Samariyawa suka zo wurinsa, sai suka roke shi ya zauna tare da su, ya kuwa zauna wurin kwana biyu.
41 Many more believed because of his word.
Wasu da dama kuma suka gaskata domin maganarsa.
42 They said to the woman, “Now we believe, not because of your speaking; for we have heard for ourselves, and know that this is indeed the Christ, the Savior of the world.”
Suka cewa matar, “Mun bada gaskiya, ba saboda maganar ki kadai ba, amma mu kanmu munji, yanzu kuma mun sani cewa wannan lallai shine mai ceton duniya.”
43 After the two days he went out from there and went into Galilee.
Bayan wadannan kwana biyu, ya bar wurin zuwa Galili.
44 For Jesus himself testified that a prophet has no honor in his own country.
Domin Yesu da kansa yace, ba a girmama annabi a kasarsa.
45 So when he came into Galilee, the Galileans received him, having seen all the things that he did in Jerusalem at the feast, for they also went to the feast.
Da ya zo Galili, Galiliyawan suka marabce shi. Sun ga dukan abubuwan da ya yi a Urushalima wurin idin, domin su ma sun je idin.
46 Jesus came therefore again to Cana of Galilee, where he made the water into wine. There was a certain nobleman whose son was sick at Capernaum.
Kuma ya koma Kana ta Galili inda ya mayar da ruwa zuwa ruwan inabi. Akwai wani ma'aikacin fada wanda dansa na rashin lafiya a Kafarnahum.
47 When he heard that Jesus had come out of Judea into Galilee, he went to him and begged him that he would come down and heal his son, for he was at the point of death.
Da ya ji cewa Yesu ya bar Yahudiya ya koma Galili, sai ya tafi wurin Yesu ya roke shi ya sauko ya warka da dansa wanda ke bakin mutuwa.
48 Jesus therefore said to him, “Unless you see signs and wonders, you will in no way believe.”
Yesu yace masa, “Idan ba ku ga alamu da mu'ujizai ba, ba za ku gaskata ba.”
49 The nobleman said to him, “Sir, come down before my child dies.”
Ma'aikacin ya ce masa, “Mallam, ka sauko kafin da na ya mutu.”
50 Jesus said to him, “Go your way. Your son lives.” The man believed the word that Jesus spoke to him, and he went his way.
Yesu yace masa, “Je ka. Dan ka ya rayu.” Mutumin ya gaskata maganar da Yesu ya gaya masa, Sai yayi tafiyarsa.
51 As he was going down, his servants met him and reported, saying “Your child lives!”
Yayin da yake sauka kasa, bayinsa suka same shi, suna cewa, danka yana raye.
52 So he inquired of them the hour when he began to get better. They said therefore to him, “Yesterday at the seventh hour, the fever left him.”
Sai ya tambaye su sa'ar da ya fara samun sauki. Suka amsa masa, “Jiya a sa'a ta bakwai zazabin ya bar shi.”
53 So the father knew that it was at that hour in which Jesus said to him, “Your son lives.” He believed, as did his whole house.
Sai Uban ya gane cewa wannan sa'a ce Yesu ya ce masa, “Jeka, danka na raye.” Sabili da haka, shi da dukan gidansa suka bada gaskiya.
54 This is again the second sign that Jesus did, having come out of Judea into Galilee.
Wannan ce alama ta biyu da Yesu ya yi bayan da ya bar Yahudiya zuwa Galili.

< John 4 >