< John 13 >

1 Now before the feast of the Passover, Jesus, knowing that his time had come that he would depart from this world to the Father, having loved his own who were in the world, he loved them to the end.
Kamin bukin idin ketarewa, sa'adda Yesu ya san lokaci ya yi da zai tashi daga wannan duniya zuwa wurin Uba, da yake ya kaunaci nasa wadanda ke duniya- ya kaunace su har karshe.
2 During supper, the devil having already put into the heart of Judas Iscariot, Simon’s son, to betray him,
Iblis ya rigaya ya sa a zuciyar Yahuza Iskariyoti dan Saminu, ya bashe da Yesu.
3 Jesus, knowing that the Father had given all things into his hands, and that he came from God and was going to God,
Ya san cewa Uba ya bada kome a hannunsa, kuma ya zo daga wurin Allah, kuma zai koma wurin Allah.
4 arose from supper, and laid aside his outer garments. He took a towel and wrapped a towel around his waist.
Ya tashi daga cin abincin, ya tube tufafinsa, ya dauki tawul ya lullube kansa da shi.
5 Then he poured water into the basin, and began to wash the disciples’ feet and to wipe them with the towel that was wrapped around him.
Sa'an nan ya zuba ruwa a bangaji, ya fara wanke kafafun almajiran, yana shafe su da tawul din da ya lullube jikinsa da shi.
6 Then he came to Simon Peter. He said to him, “Lord, do you wash my feet?”
Ya zo wurin Bitrus Saminu, sai Bitrus ya ce masa,”Ubangiji, za ka wanke mani kafa?”
7 Jesus answered him, “You don’t know what I am doing now, but you will understand later.”
Yesu ya amsa ya ce, “Abin da nake yi ba za ka fahimce shi yanzu ba, amma daga baya za ka fahimta.”
8 Peter said to him, “You will never wash my feet!” Jesus answered him, “If I don’t wash you, you have no part with me.” (aiōn g165)
Bitrus ya ce masa, “Ba za ka taba wanke mani kafa ba.” Yesu ya amsa masa ya ce, “In ban wanke maka ba, ba ka da rabo da ni”. (aiōn g165)
9 Simon Peter said to him, “Lord, not my feet only, but also my hands and my head!”
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ba kafafuna kadai za ka wanke ba, amma da hannayena da kaina.”
10 Jesus said to him, “Someone who has bathed only needs to have his feet washed, but is completely clean. You are clean, but not all of you.”
Yesu ya ce masa, “Duk wanda ya yi wanka ba ya da bukata, sai dai a wanke kafafunsa, amma shi tsarkakakke ne baidaya; ku tsarkakakku ne, amma ba dukanku ba.”
11 For he knew him who would betray him; therefore he said, “You are not all clean.”
(Don Yesu ya san wanda zai bashe shi, shiyasa ya ce, “Ba dukanku ne ke da tsarki ba.”)
12 So when he had washed their feet, put his outer garment back on, and sat down again, he said to them, “Do you know what I have done to you?
Bayan Yesu ya wanke masu kafafu, ya dauki tufafinsa ya zauna kuma, ya ce masu, “Kun san abin da na yi muku?
13 You call me, ‘Teacher’ and ‘Lord.’ You say so correctly, for so I am.
kuna kirana, 'Malam, da Ubangiji,' kun fadi daidai, don haka Nake.
14 If I then, the Lord and the Teacher, have washed your feet, you also ought to wash one another’s feet.
Idan ni Ubangiji da kuma mallam, na wanke maku kafafu, ya kamata kuma ku wanke wa junan ku kafafu.
15 For I have given you an example, that you should also do as I have done to you.
Gama na baku misali, saboda ku yi yadda na yi maku.
16 Most certainly I tell you, a servant is not greater than his lord, neither is one who is sent greater than he who sent him.
Lalle hakika ina gaya muku, bawa ba ya fi mai gidansa girma ba; dan aike kuma ba ya fi wanda ya aiko shi girma ba.
17 If you know these things, blessed are you if you do them.
Idan kun san wadannan abubuwa, ku masu albarka ne idan kun aikata su.
18 I don’t speak concerning all of you. I know whom I have chosen; but that the Scripture may be fulfilled, ‘He who eats bread with me has lifted up his heel against me.’
Ba ina magana akan dukanku ba; Na san wadanda na zaba. Amma domin Nassi ya cika: 'Shi Wanda ya ci gurasata, ya tayar mani'.
19 From now on, I tell you before it happens, that when it happens, you may believe that I am he.
Ina fada maku wannan yanzu tun kafin haka ta faru domin sa'adda ta faru, ku gaskata Ni ne.
20 Most certainly I tell you, he who receives whomever I send, receives me; and he who receives me, receives him who sent me.”
Hakika, hakika, Ina gaya maku, wanda ya karbi wanda na aiko, Ni ya karba, wanda kuma ya karbe ni, ya karbi wanda ya aiko ni.
21 When Jesus had said this, he was troubled in spirit, and testified, “Most certainly I tell you that one of you will betray me.”
Bayan Yesu ya fadi haka, ya damu a ruhu, ya yi shaida ya ce, “Lalle hakika, ina gaya muku cewa daya daga cikinku zai bashe ni.”
22 The disciples looked at one another, perplexed about whom he spoke.
Almajiran suka kalli juna, suna juyayin ko akan wa yake magana.
23 One of his disciples, whom Jesus loved, was at the table, leaning against Jesus’ chest.
Daya daga cikin almajiransa, wanda Yesu yake kauna, yana a teburi, jingine a kirjin Yesu.
24 Simon Peter therefore beckoned to him, and said to him, “Tell us who it is of whom he speaks.”
Siman Bitrus ya ce wa almajirin, “ka fada mana ko akan wa ya ke magana.”
25 He, leaning back, as he was, on Jesus’ chest, asked him, “Lord, who is it?”
Sai ya sake jingina a kirjin Yesu, ya ce masa, “Ubangiji, wanene?”
26 Jesus therefore answered, “It is he to whom I will give this piece of bread when I have dipped it.” So when he had dipped the piece of bread, he gave it to Judas, the son of Simon Iscariot.
Sannan Yesu ya amsa, “Shine wanda zan tsoma gutsuren gurasa in ba shi.” Sannan bayan ya tsoma gurasar, sai ya ba Yahuza Dan Siman Iskariyoti.
27 After the piece of bread, then Satan entered into him. Then Jesus said to him, “What you do, do quickly.”
To bayan gurasar, sai shaidan ya shige shi, sai Yesu ya ce masa, “Abinda kake yi, ka yi shi da sauri.”
28 Now nobody at the table knew why he said this to him.
Babu wani a teburin da ya san dalilin dayasa ya fada masa wannan.
29 For some thought, because Judas had the money box, that Jesus said to him, “Buy what things we need for the feast,” or that he should give something to the poor.
Wadansu sun yi tsamanin cewa, tun da Yahuza ne ke rike da jakkar kudi, Yesu ya ce masa, “Ka sayi abinda muke bukata don idin”, ko kuma ya bada wani abu domin gajiyayyu.
30 Therefore having received that morsel, he went out immediately. It was night.
Bayan Yahuza ya karbi gurasar, sai ya fita nan da nan. Da daddare ne kuwa.
31 When he had gone out, Jesus said, “Now the Son of Man has been glorified, and God has been glorified in him.
Bayan Yahuza ya tafi, Yesu ya ce, “Yanzu an daukaka Dan mutum, kuma an daukaka Allah a cikinsa.
32 If God has been glorified in him, God will also glorify him in himself, and he will glorify him immediately.
Allah zai daukaka shi a cikin kansa, kuma zai daukaka shi nan da nan.
33 Little children, I will be with you a little while longer. You will seek me, and as I said to the Jews, ‘Where I am going, you can’t come,’ so now I tell you.
'Ya'ya kanana, ina tare da ku na wani gajeren lokaci. Zaku neme ni, kuma kamar yadda na fadawa Yahudawa, 'in da zan tafi ba za ku iya zuwa ba.' Yanzu kuma na fada maku wannan.
34 A new commandment I give to you, that you love one another. Just as I have loved you, you also love one another.
Ina baku sabuwar doka, ku kaunaci juna; kamar yadda na kaunace ku, haka kuma ku kaunaci juna.
35 By this everyone will know that you are my disciples, if you have love for one another.”
Ta haka kowa zai san ku almajiraina ne, idan kuna kaunar juna.”
36 Simon Peter said to him, “Lord, where are you going?” Jesus answered, “Where I am going, you can’t follow now, but you will follow afterwards.”
Siman Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, ina za ka?” Yesu ya amsa ya ce, “Inda za ni, ba zaka iya bi na ba yanzu, amma zaka bini daga baya.”
37 Peter said to him, “Lord, why can’t I follow you now? I will lay down my life for you.”
Bitrus ya ce masa, “Ubangiji, don me ba zan iya binka a yanzu ba? Zan bada raina domin ka.”
38 Jesus answered him, “Will you lay down your life for me? Most certainly I tell you, the rooster won’t crow until you have denied me three times.
Yesu ya amsa ya ce, “Za ka bada ranka domina? Lalle hakika, ina gaya maka, kafin zakara ya yi cara zaka yi musu na sau uku.”

< John 13 >