< Job 42 >

1 Then Job answered Yahweh:
Sa’an nan Ayuba ya amsa wa Ubangiji,
2 “I know that you can do all things, and that no purpose of yours can be restrained.
“Na san cewa za ka iya yin dukan abubuwa; ba wanda zai iya ɓata shirinka.
3 You asked, ‘Who is this who hides counsel without knowledge?’ therefore I have uttered that which I didn’t understand, things too wonderful for me, which I didn’t know.
Ka yi tambaya, ‘Wane ne wannan da ya ƙi karɓar shawarata shi marar ilimi?’ Ba shakka na yi magana game da abubuwan da ban gane ba, abubuwan ban al’ajabi da sun fi ƙarfin ganewata.
4 You said, ‘Listen, now, and I will speak; I will question you, and you will answer me.’
“Ka ce, ‘Saurara yanzu, zan kuma yi magana zan tambaye ka, kuma za ka amsa mini.’
5 I had heard of you by the hearing of the ear, but now my eye sees you.
Kunnuwana sun ji game da kai amma yanzu na gan ka.
6 Therefore I abhor myself, and repent in dust and ashes.”
Saboda haka na rena kaina na kuma tuba cikin ƙura da toka.”
7 It was so, that after Yahweh had spoken these words to Job, Yahweh said to Eliphaz the Temanite, “My wrath is kindled against you, and against your two friends; for you have not spoken of me the thing that is right, as my servant Job has.
Bayan Ubangiji ya gaya wa Ayuba waɗannan abubuwa, ya ce wa Elifaz mutumin Teman, “Ina fushi da kai da abokanka guda biyu domin ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba, kamar yadda bawana Ayuba ya yi.
8 Now therefore, take to yourselves seven bulls and seven rams, and go to my servant Job, and offer up for yourselves a burnt offering; and my servant Job shall pray for you, for I will accept him, that I not deal with you according to your folly. For you have not spoken of me the thing that is right, as my servant Job has.”
Saboda haka yanzu sai ku ɗauki bijimai guda bakwai, da raguna bakwai, ku je wurin bawana Ayuba ku miƙa hadaya ta ƙonawa domin kanku. Bawana Ayuba zai yi muku addu’a zan kuwa karɓi addu’arsa in bi da ku nisa da wawancinku. Ba ku faɗi abin da yake daidai game da ni ba yadda bawana Ayuba ya yi ba.”
9 So Eliphaz the Temanite and Bildad the Shuhite and Zophar the Naamathite went and did what Yahweh commanded them, and Yahweh accepted Job.
Saboda haka Elifaz mutumin Teman, Bildad mutumin Shuwa da Zofar mutumin Na’ama, suka yi abin da Ubangiji ya gaya masu; Ubangiji kuma ya karɓi addu’ar Ayuba.
10 Yahweh restored Job’s prosperity when he prayed for his friends. Yahweh gave Job twice as much as he had before.
Bayan Ayuba ya yi wa abokansa addu’a, Ubangiji ya sa shi ya sāke zama mai arziki ya ninka abin da yake da shi a dā sau biyu.
11 Then all his brothers, all his sisters, and all those who had been of his acquaintance before, came to him and ate bread with him in his house. They comforted him, and consoled him concerning all the evil that Yahweh had brought on him. Everyone also gave him a piece of money, and everyone a ring of gold.
Dukan’yan’uwansa maza da mata da duk waɗanda suka san shi a dā suka zo suka ci abinci tare da shi a cikin gidansa. Suka ta’azantar da shi suka ƙarfafa shi game da duk wahalar da Ubangiji ya auka masa, kowannensu kuma ya ba shi azurfa da zobe na zinariya.
12 So Yahweh blessed the latter end of Job more than his beginning. He had fourteen thousand sheep, six thousand camels, one thousand yoke of oxen, and a thousand female donkeys.
Ubangiji ya albarkaci ƙarshen Ayuba fiye da farkonsa. Yana da tumaki guda dubu goma sha huɗu, raƙuma guda dubu shida; shanun noma guda dubu da jakuna guda dubu.
13 He had also seven sons and three daughters.
Ya kuma haifi’ya’ya maza bakwai, mata uku.
14 He called the name of the first, Jemimah; and the name of the second, Keziah; and the name of the third, Keren Happuch.
’Yar farko ya kira ta Yemima, ta biyun Keziya ta ukun Keren-Haffuk.
15 In all the land were no women found so beautiful as the daughters of Job. Their father gave them an inheritance among their brothers.
Duk a cikin ƙasar ba a samu kyawawan mata kamar’ya’yan Ayuba ba, kuma babansu ya ba su gādo tare ta’yan’uwansu maza.
16 After this Job lived one hundred forty years, and saw his sons, and his sons’ sons, to four generations.
Bayan wannan Ayuba ya rayu shekara ɗari da arba’in; ya ga’ya’yansa da’ya’yansu har tsara ta huɗu.
17 So Job died, being old and full of days.
Sa’an nan Ayuba ya rasu da kyakkyawan tsufa.

< Job 42 >