< Isaiah 61 >

1 The Lord Yahweh’s Spirit is on me, because Yahweh has anointed me to preach good news to the humble. He has sent me to bind up the broken hearted, to proclaim liberty to the captives and release to those who are bound,
Ruhun Ubangiji Mai Iko Duka yana a kaina, domin Ubangiji ya shafe ni domin in yi wa’azi labari mai daɗi ga matalauta. Ya aiko ni in warkar da waɗanda suka karai a zuci, don in yi shelar’yanci don ɗaurarru in kuma kunce’yan kurkuku daga duhu
2 to proclaim the year of Yahweh’s favor and the day of vengeance of our God, to comfort all who mourn,
don in yi shelar shekarar tagomashin Ubangiji da kuma ranar ɗaukan fansar Allahnmu, don in ta’azantar da dukan waɗanda suke makoki,
3 to provide for those who mourn in Zion, to give to them a garland for ashes, the oil of joy for mourning, the garment of praise for the spirit of heaviness, that they may be called trees of righteousness, the planting of Yahweh, that he may be glorified.
in tanada wa waɗanda suke baƙin ciki a Sihiyona, in maido musu rawani mai kyau a maimako na toka, man murna a maimako na makoki, da kuma rigar yabo a maimako na ruhun fid da zuciya. Za a ce da su itatuwan oak na adalci, shukin Ubangiji don bayyana darajarsa.
4 They will rebuild the old ruins. They will raise up the former devastated places. They will repair the ruined cities that have been devastated for many generations.
Za su sāke gina kufai na dā su raya wurare da aka lalace tun da daɗewa; za su sabunta biranen da aka rurrushe da aka lalace tun zamanai masu yawa da suka wuce.
5 Strangers will stand and feed your flocks. Foreigners will work your fields and your vineyards.
Baƙi za su yi kiwon garkunanki; baƙi za su yi miki noman gonaki da gonakin inabinki.
6 But you will be called Yahweh’s priests. Men will call you the servants of our God. You will eat the wealth of the nations. You will boast in their glory.
Za a kuma kira ku firistocin Ubangiji, za a kira ku masu hidimar Allahnmu. Za ku ci wadatar waɗansu al’ummai, kuma a cikin dukiyarsu za ku yi taƙama.
7 Instead of your shame you will have double. Instead of dishonor, they will rejoice in their portion. Therefore in their land they will possess double. Everlasting joy will be to them.
A maimakon kunyarsu mutanena za su sami rabi riɓi biyu, a maimakon wulaƙanci za su yi farin ciki cikin gādonsu; ta haka za su gāji rabo riɓi biyu a ƙasarsu, da kuma madawwamin farin ciki zai zama nasu.
8 “For I, Yahweh, love justice. I hate robbery and iniquity. I will give them their reward in truth and I will make an everlasting covenant with them.
“Gama ni, Ubangiji, ina ƙaunar adalci; na ƙi fashi da aikata laifi. Cikin adalcina zan sāka musu in kuma yi madawwamin alkawari da su.
9 Their offspring will be known among the nations, and their offspring among the peoples. All who see them will acknowledge them, that they are the offspring which Yahweh has blessed.”
Za a san da zuriyarsu a cikin al’ummai’ya’yansu kuma a cikin mutane. Dukan waɗanda suka gan su za su san cewa su mutane ne da Ubangiji ya sa wa albarka.”
10 I will greatly rejoice in Yahweh! My soul will be joyful in my God, for he has clothed me with the garments of salvation. He has covered me with the robe of righteousness, as a bridegroom decks himself with a garland and as a bride adorns herself with her jewels.
Ina jin daɗi ƙwarai a cikin Ubangiji; raina yana farin ciki a cikin Allahna. Gama ya suturce ni da rigunan ceto ya yi mini ado da rigar adalci, yadda ango yakan yi wa kansa ado kamar firist kamar kuma yadda amarya takan sha ado da duwatsunta masu daraja.
11 For as the earth produces its bud, and as the garden causes the things that are sown in it to spring up, so the Lord Yahweh will cause righteousness and praise to spring up before all the nations.
Gama kamar yadda ƙasa takan sa tsire-tsire su tohu lambu kuma ya sa iri ya yi girma, haka Ubangiji Mai Iko Duka zai sa adalci da yabo su tsiro a gaban dukan al’ummai.

< Isaiah 61 >