< Ephesians 2 >

1 You were made alive when you were dead in transgressions and sins,
Ku kam, a dā ku matattu ne saboda laifofinku da kuma zunubanku.
2 in which you once walked according to the course of this world, according to the prince of the power of the air, the spirit who now works in the children of disobedience. (aiōn g165)
Kun yi rayuwa kamar yadda sauran mutanen duniya suke yi, cike da zunubi, kuna biyayya ga sarki masu ikon sarari sama, wato, ruhun nan da yanzu yake aiki a cikin masu ƙin biyayya ga Allah. (aiōn g165)
3 We also all once lived among them in the lusts of our flesh, doing the desires of the flesh and of the mind, and were by nature children of wrath, even as the rest.
Dukanmu a dā mun yi irin rayuwan nan a cikinsu, muna bin kwaɗayi da sha’awace-sha’awacen jikunanmu da tunaninmu. Kamar sauran mutane, mun cancanci fushin Allah.
4 But God, being rich in mercy, for his great love with which he loved us,
Amma saboda yawan ƙaunar da yake mana, Allah, wanda yake mai yawan jinƙai,
5 even when we were dead through our trespasses, made us alive together with Christ—by grace you have been saved—
ya ba mu rai sa’ad da ya tashe Kiristi daga matattu. Ta wurin alherin Allah ne aka cece ku.
6 and raised us up with him, and made us to sit with him in the heavenly places in Christ Jesus,
Allah ya tashe mu tare da Kiristi, ya kuma ba mu wurin zama tare da shi a cikin mulkin samaniya.
7 that in the ages to come he might show the exceeding riches of his grace in kindness toward us in Christ Jesus; (aiōn g165)
Allah ya yi haka domin a tsararraki masu zuwa yă nuna yalwar alherinsa da ya wuce misali, an bayyana alheransa da ya yi mana ta wurin Kiristi Yesu. (aiōn g165)
8 for by grace you have been saved through faith, and that not of yourselves; it is the gift of God,
Allah ya cece ku ta wurin alheri sa’ad da kuka ba da gaskiya. Wannan kuwa ba yinku ba ne, kyauta ce daga Allah.
9 not of works, that no one would boast.
Ba kuwa saboda aikin lada ba, don kada wani yă ɗaga kai.
10 For we are his workmanship, created in Christ Jesus for good works, which God prepared before that we would walk in them.
Ai, mu aikinsa ne, an sāke halittarmu a cikin Kiristi Yesu musamman domin mu yi kyawawan ayyuka, waɗanda Allah ya tanadar mana tun da fari, mu yi.
11 Therefore remember that once you, the Gentiles in the flesh, who are called “uncircumcision” by that which is called “circumcision” (in the flesh, made by hands),
Saboda haka, ku tuna dā ku Al’ummai ne bisa ga haihuwa, waɗanda kuma ake kira masu “kaciya” sukan kira ku “marasa kaciya” (ga shi kuwa, kaciyar nan ta jiki ce, wadda ake yi da hannu).
12 that you were at that time separate from Christ, alienated from the commonwealth of Israel, and strangers from the covenants of the promise, having no hope and without God in the world.
Ku kuma tuna a lokacin ba ku san Kiristi ba. A ware kuke daga mutanen Isra’ila, ba ku kuma da dangantaka da alkawaran da Allah ya yi da su. Kun yi zama a duniyan nan babu bege kuma babu Allah.
13 But now in Christ Jesus you who once were far off are made near in the blood of Christ.
Amma yanzu a cikin Kiristi Yesu, ku da dā kuke can da nesa an kawo ku kusa ta wurin jinin Kiristi.
14 For he is our peace, who made both one, and broke down the middle wall of separation,
Gama shi kansa shi ne salamarmu, shi ne ya kawo ƙungiyoyi biyu suka zama ɗaya, ya kuma rushe katangan nan ta ƙiyayya wadda ta raba mu.
15 having abolished in his flesh the hostility, the law of commandments contained in ordinances, that he might create in himself one new man of the two, making peace,
Kiristi ya ba da jikinsa don yă kawar da doka da dukan umarnanta da kuma ƙa’idodinta. Ya yi haka domin yă halicci sabuwar zuriya daga zuriyoyin nan biyu. Ta haka kuma ya kawo salama tsakaninsu.
16 and might reconcile them both in one body to God through the cross, having killed the hostility through it.
A kan gicciye, Kiristi ya kawar da ƙiyayyar da take tsakaninmu da juna. Ya kuma kawo sulhu tsakaninmu da Allah.
17 He came and preached peace to you who were far off and to those who were near.
Ya zo ya yi muku wa’azin salama; ku da kuke nesa da shi, ya kuma yi wa waɗanda suke kusa.
18 For through him we both have our access in one Spirit to the Father.
Gama ta wurinsa dukanmu za mu iya zuwa gun Uba ta wurin Ruhu guda.
19 So then you are no longer strangers and foreigners, but you are fellow citizens with the saints and of the household of God,
Don haka, yanzu ku ba baƙi ba ne, ku kuma ba bare ba ne. Ku’yan ƙasa ne tare da mutanen Allah, iyalin gidan Allah kuma.
20 being built on the foundation of the apostles and prophets, Christ Jesus himself being the chief cornerstone;
Ku gini ne wanda manzanni da annabawa suke tushensa, Kiristi kuma shi ne dutse mafi muhimmanci na ginin.
21 in whom the whole building, fitted together, grows into a holy temple in the Lord;
Ta wurinsa ne dukan ginin yake a haɗe, shi ne kuma yake sa ginin yă yi girma, yă zama haikali mai tsarki domin Ubangiji.
22 in whom you also are built together for a habitation of God in the Spirit.
Ku ma sashe ne na wannan ginin da Kiristi ya yi inda Allah yake zaune ta wurin Ruhunsa.

< Ephesians 2 >